Daraktocin DSS na Arewa maso Yamma sun yi gangamin yaki da ta’addanci da ‘yan fashi

Daga Abbas Bamalli

Katsina, Agusta 14, 2026 (NAN) Daraktocin Hukumar Tsaro ta farin kaya ta kasa (DSS) na Arewa maso Yamma, sun yi kira da a kara karfafa musayar bayanai da hadin gwiwa a fannin aiki domin dakile ta’addanci, fashi da makami da sauran barazanar tsaro a yankin.

An yi kiran ne a taron Daraktocin Tsaro na Jihohin Arewa maso Yamma, wanda Ma’aikatar Tsaro ta kasa (DSS) ta shirya a Katsina, mai taken: “Ku Haɗa Kai Don Yaƙi da Ta’addanci.”

Daraktan Tsaro na Jihar Katsina, Alhaji Alhassan Iliyasu, ya ce taron ya ba wa hukumomin leƙen asiri damar yin bitar ƙalubalen tsaro da ke tasowa da kuma haɓaka dabarun da suka dace don shawo kansu.

Iliyasu, ya ce taron zai bai wa mahalarta damar kwatanta abubuwan da suka faru, gano gibin aiki da kuma ƙarfafa matakan magance ayyukan fashi da makami da sauran laifuka masu alaƙa a faɗin Arewa maso Yamma.

Ya ce tattaunawar za ta ƙare da wani jawabi, wanda zai zama taswirar da za a iya aiwatarwa ga hukumomin tsaro a yankin.

A cewarsa, yaƙi da ta’addanci yana buƙatar dukkan masu ruwa da tsaki, ciki har da hukumomin tsaro, al’ummomi, ƙungiyoyin ‘yan banga da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya yaba da hadin gwiwar da ake da shi tsakanin hukumomin tsaro a Katsina, yana mai cewa hadin gwiwar ya taimaka sosai wajen inganta yanayin tsaro a jihar.

“Haɗin Kai kan Yaƙi da Ta’addanci ya shafi kowa da kowa, ba kawai hukumomin tsaro ba, har ma da dukkan al’umma,” in ji shi.

Hukumar ta ce martanin tsaro da Katsina ta mayar kan al’umma, gami da shigar da rundunar tsaro ta Community Watch Corps da ƙungiyoyin ‘yan banga, ya ƙarfafa matakan da ake ɗauka a gaba wajen yaƙi da barazanar tsaro.

Ya yi kira ga mazauna yankin da su tabbatar da cewa sun sauke nauyin da ke kansu na jama’a, ta hanyar bayar da rahoton abubuwan da ake zargi da kuma ayyukan da ake yi ga hukumomin tsaro.

Da yake jawabi, Kwamandan runduna ta 17 Brigade, Brig.-Gen. Ishaya Ibrahim, ya bayyana jigon taron a matsayin wanda ya dace, yana mai cewa hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro muhimmin abu ne wajen tunkarar barazanar da ke tasowa da kuma rashin iyaka.

Ibrahim ya ce duk da cewa karfin soji, dabarun aiki da ayyukan yankuna suna da mahimmanci, bayanan sirri da za a iya samarwa, sun kasance masu mahimmanci don tabbatar da daidaito da inganci a ayyukan yaki da ta’addanci.

Ya yaba wa DSS saboda basira, sa ido, kimanta barazana da kuma hanyoyin sadarwa ga al’umma, wanda, a cewarsa, ya samar da bayanan da ake buƙata don ingantaccen martanin soja.

Kwamandan ya ce, ‘yan ta’adda da ‘yan fashi, sun yi amfani da gibin da ke akwai a fannin bayanai, hadin kai da kuma amana.

Ya yi kira ga hukumomin tsaro, da su rufe irin wadannan gibin ta hanyar musayar bayanai, a ainihin lokaci da kuma tsara ayyukan hadin gwiwa.

Daga nan ne ya kara da cewa yana da kyau a karfafa ka’idojin sadarwa, horaswa tare da goyon bayan juna tsakanin hukumomin tsaro.

A cewarsa, hukumomin tsaro dole ne su sami kwarin gwiwar al’ummomi, domin za a cimma nasara ta ƙarshe a kan ta’addanci ta hanyar haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da jama’a.

A jawabinsa, Gwamna Dikko Radda na Jihar Katsina, ya yaba wa Hukumar Tsaro ta DSS kan kiran taron, sannan ya bayyana jigon a matsayin wanda ya dace da kalubalen tsaro da Arewa maso Yamma ke fuskanta.

Radda, wanda Mataimakin Gwamna Faruk Lawal-Jobe ya wakilta, ya ce kalubalen tsaro da yankin ke fuskanta suna da alaƙa sosai, don haka yana buƙatar dabarun gama gari da haɗin gwiwa mai ɗorewa tsakanin hukumomin tsaro.

Ya ce Katsina ta sami ci gaba mai yawa a fannin tsaro ta hanyar haɗa hanyoyin da dama.

A cewarsa, gwamnatin jihar ta tallafawa hukumomin tsaro yayin da take aiwatar da matakan da suka dace don magance yanayin zamantakewa da tattalin arziki na al’ummomin da ‘yan fashi suka shafa.

Ya ce gwamnati ta samar da ayyukan kiwon lafiya kyauta ga wadanda hare-haren ‘yan fashi suka shafa, tare da ƙarfafa tallafin noma ta hanyar amfani da injina, ayyukan faɗaɗawa, ingantattun iri da kuma rarraba taki. (NAN) (www.nannews.ng)

AABS/AAA 

Fassara da gyarawa Aisha Ahmed

 

Gwamnonin Jihohin Najeriya sun jaddada kudirinsu ga cigaban yara kanana

Daga Emmanuel Oloniruha

Abuja, Agusta 14, 2026 (NAN) Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta sake jaddada alƙawarin da dukkan gwamnonin jihohi 36 suka ɗauka na sanya tallafawa cigaban yara kanana (ECD), a matsayin muhimmin abu a cikin ajandar cigaban ɗan adam ta Najeriya.

An sake jaddada wannan alƙawarin ne tare da haɗin gwiwar Bankin Duniya, cigaban dan adam (HCD) da ma’aikatar kasafin Kuɗi da tsarin Tattalin Arziki.

Daraktan yada labarai da sadarwa na NGF, Yunusa Abdullahi, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, cewa babban darakta na Sakatariyar NGF, Dr Abdulateef Shittu, ya yi alƙawarin a wani taron ba da shawara kan harkokin kuɗi na yankin Arewa maso Yamma kan ECD.

Shittu, wanda Abdullahi ya wakilta a taron bitar, ya bayyana jarin da aka zuba a farkon shekarun, a matsayin jarin da aka zuba na dogon lokaci a fannin lafiya, ilimi, tsarin aiki da kuma makomar tattalin arziki a Najeriya.

“Lokacin da yaro ke ciki har zuwa shekaru biyar na farko na rayuwa, yana wakiltar wani muhimmin kafar ci gabansa.”

“A cikin waɗannan shekarun ne aka kafa harsashin lafiya, ilmantarwa, cigaban fahimta da kuma samar da aiki a nan gaba,” in ji shi.

Daraktan ya bayyana cewa, dole ne Najeriya ta dauki ECD a matsayin muhimmin ci gaba da tattalin arziki, maimakon a matsayin wani shiri da ya takaita ga wani fanni guda.

“Saboda haka, saka hannun jari a ci gaban yara tun suna ƙanana, ba wai kawai jari ne ga yara ba, har ma da saka hannun jari a al’ummar Najeriya da kuma ci gaban tattalin arziki na dogon lokaci,” in ji Shittu.

Ya jaddada cewa, za a tantance ingancin manufofin ECD na ƙasa, ta hanyar fassara su zuwa shirye-shirye na zahiri a matakin ƙasa da ƙasa.

“Duk da cewa manufofi da tsare-tsare na ƙasa suna ba da muhimmin alkibla, tasirinsu a ƙarshe zai dogara ne akan yadda aka mayar da su aiki yadda ya kamata, a matakan jiha da ƙananan hukumomi.

“Wannan ya sanya mu, masu ruwa da tsaki a harkokin gwamnati, a tsakiyar ajandar ECD ta Najeriya,” in ji shi.

Bugu da kari, Shittu ya lura cewa sarkakiyar ECD tana buƙatar tsarin haɗin gwiwa da daban-daban da zai shafi dukkan fannoni masu dacewa, domin babu wata ma’aikata guda ɗaya da za ta iya samar da nau’ikan ayyukan da yaro ke buƙata don bunƙasa.

“Dole ne dukkan sassan su yi aiki tare don cimma sakamako iri ɗaya ga yara,” in ji shi.

Shittu ya ƙara yin gargaɗi game da ɗaukar tsarin da muhimmanci, a matsayin wani abu da zai kawo cigaba, yana mai jaddada muhimmancin aiwatarwa, kuɗaɗen da za a kashe, daidaitawa da kuma ɗaukar alhakin da ya dace.

“Tsammaninmu shi ne cewa, wannan tsari ya wuce tsarin tsara shirye-shirye.”

Ya ƙara da cewa, “Shirye-shiryen da aka tsara a nan, ya kamata su samar da hanya bayyananna don aiwatarwa, daidaitawa, kuɗi da kuma riƙon amana, kuma mafi mahimmanci, ya kamata a haɗa su cikin tsare-tsaren jiha da kasafin kuɗi da ake da su a yanzu.”

Hakazalika, ya yi alƙawarin cewa Sakatariyar NGF, za ta ci gaba da amfani da hadin gwuiwa da ilmantarwa tsakanin takwarorinta, don tallafawa jihohi wajen ƙarfafa tsarin ECD ɗinsu.

A karshe Daraktan, ya yi kira ga mahalarta taron da su yi amfani da wannan damar wajen samar da tsare-tsare masu inganci wadanda za su iya samar da ingantattun sakamako ga kananan yara. (NAN)(www.nannees.ng)

 

OBE/AAA/FOF

Fassarar Aisha Ahmed

Zanga zanga ta barke bisa karin farashin man fetur a Kenya

Zanga zanga

Nairobi, 19 ga Mayu, 2026 (Reuters/NAN) Zanga zanga ta barke a wasu garuruwa na Kenya ranar Litinin, saboda karin farashin man fetur, ciki har da yajin aikin sufuri na jama’a, wanda ya tilastawa matafiya tafiya da lafa zuwa wurin aiki.

Kungiyar Sufuri ta kasar, ta ce a ranar Lahadi ya kamata motocin da ke da alaƙa da ƙungiyoyin membobinta su daina aiki daga tsakar dare, don nuna rashin amincewa da hauhawar farashi, inda ‘yan sanda suka yi alƙawarin magance duk wani cikas.

Hukumar Kula da Makamashi da Man Fetur ta Kenya, ta kara farashin mai da kashi 23.5 cikin 100, bayan ta kara farashinsa da kashi 24.2 cikin 100 a watan Afrilu, yayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke kara matsin lamba kan samar da mai da iskar gas a duniya.

A safiyar Litinin, an toshe hanyoyin shiga babban birnin Nairobi ta hanyar masu sufuri da kuma gungun masu zanga-zanga da suka watse.

‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa a wasu yankuna, yayin da wasu masu zanga-zanga suka kunna tayoyi don hana shiga manyan hanyoyi, lamarin da ya kara ta’azzara cunkoso da kuma barin mutane da yawa da ke tafiya a kasa.

A Mombasa, babban birnin tashar jiragen ruwa na Kenya, yajin aikin ya haifar da fargabar jinkirin da ake samu wajen samar da kayayyaki.

Ministan Kudi na kasar, John Mbadi ya shaida wa tashar talabijin ta Citizen cewa, ma’aikatun kudi da makamashi suna fatan ganawa da masu kula da sufuri na jama’a a ranar Litinin don tattauna mafita, yana mai lura da cewa an riga an tallafa wa farashin da ake da shi a yanzu.

“Kenya tana shigo da kusan dukkan kayayyakin mai daga Gabas ta Tsakiya ta hanyar yarjejeniyar gwamnati da gwamnati da masu samar da mai na yankin Gulf.

“Karin farashin mai ya ƙara yawan kuɗin sufuri da kuma ƙara farashin kayan masarufi, wanda hakan ya ƙara matsin lamba ga iyalai da ke fama da tsadar rayuwa,” Ministan yace.

Ma’aikacin hulda da jama’a, Gabriel Odhiambo, mai shekaru 24, ya ce farashin sufurinsa ya ninka sau biyu kuma farashin abinci shi ma ya tashi.

Ya ce yanzu haka, farashin tumatir guda hudu suna kan farashin shilling 60 (cent 50 na Amurka), ƙarin ya ninka sau uku.

Kenya ta ƙara farashin famfon mai na super petrol a Nairobi zuwa 214.25 na Kenya ​shillings ($1.66) a kowace lita daga 206.97, dizal zuwa 242.92 ​shillings daga 196.63 na zagayowar 15 ga Mayu zuwa 14 ga Yuni, yayin da kananzir bai canza ba a shilling 152.78. (Reuters/NAN) ( www.nannews.ng )

 

HLM/CEO/AAA

Edited by Hadiza Mohammed/Chidi Opara

 

Fassarar Aisha Ahmed 

Tinubu ya gabatar da da shawara akan kasuwanci a Najeriya ga Afrika

 

Kasuwanci

Daga Muhydeen Jimoh

Abuja, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Shugaba Bola Tinubu ya ci gaba da jajircewa wajen cigaban Najeriya ta hanyar gyare-gyare da kuma sanya kasar a matsayin babbar hanyar zuba jari a nahiyar Afirka da duniya baki daya.

 

Mista Sunday Dare, mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa ga shugaban kasa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa kafin halartar Tinubu a taron shugabannin Afirka na 2026 da za a yi a Kigali, Rwanda.

 

Sanarwar, mai taken “A Rwanda, Tinubu Ya Bayyana Kasuwancin Najeriya Ga Sauran kasashen Afirka,” ta bayyana Kigali a matsayin matattara ɗaya daga cikin manyan masu zuba jari da gwamnatin ta yi tun lokacin da ta hau mulki.

 

A cewar Dare, sakon Tinubu ga masu zuba jari abu ne mai sauƙi: Najeriya ta kasance ɗaya daga cikin wuraren zuba jari mafi riba a duniya, inda kasuwanci masu inganci za su iya samar da riba mai ban mamaki fiye da tsammanin kasuwa na yau da kullun.

 

Ya ce yayin da yawancin ayyukan tsarin saka hannun jari na duniya ke dawowa tsakanin kashi 20 zuwa 25 cikin 100, Najeriya ta ci gaba da wuce irin wannan hasashen saboda yawan jama’arta, karuwar buƙatu, da kuma saurin bunkasa yanayin gyara.

 

Dare ya ambaci kamfanin sadarwa na MTN Nigeria a matsayin misali, inda ya lura cewa ci gaban kasuwar kamfanin, faɗaɗa masu biyan kuɗi, da kuma ribar da kamfanin ya samu ya wuce tsammanin farko bayan ya shiga kasuwar Najeriya a shekarar 2001.

 

Ya ce MTN Nigeria yanzu tana samar da tiriliyan na nairori kowace shekara, kuma har yanzu tana ɗaya daga cikin kamfanoni mafi daraja da aka jera a kasuwar musayar kuɗi ta Najeriya, wanda ke nuna babbar damar da ƙasar ke da ita ta kasuwanci da kasuwar masu saye.

 

Mataimakin shugaban ya kuma yi nuni da kamfanin MultiChoice, masu tallata DStv, yana mai cewa ayyukan kamfanin a Najeriya sun rikide zuwa daya daga cikin manyan cibiyoyin kasuwanci saboda fadada birane, karuwar amfani da kayayyaki, da kuma yawan jama’a.

 

Dare ya yarda cewa ƙalubalen Najeriya na nan a bayyane kuma wani lokacin ana ƙara gishiri, amma ya dage cewa a ƙarƙashinsu akwai ɗaya daga cikin kasuwannin masu saye mafi zurfi a duniya kuma ɗaya daga cikin al’ummomin da suka fi kasuwanci a Afirka.

 

Ya ce Najeriya tana da damarmakin fadada ababen more rayuwa, bunkasa yanayin fasahar zamani, wadataccen albarkatun ma’adinai, da kuma makamashin da ba a iya misaltawa ba wanda zai iya haifar da ci gaban masana’antu da tattalin arziki mai dorewa a fadin nahiyar Afirka.

 

A cewarsa, taron shugabannin Afirka ya fi wakiltar fiye da taro, yana mai bayyana shi a matsayin kasuwa don jarin saka hannun jari, haɗin gwiwa, alkiblar manufofi, da tattaunawa mai mahimmanci waɗanda ke tsara makomar tattalin arzikin Afirka da gasa.

 

Ya ce sama da manyan jami’ai 2,000, masu zuba jari, masu kudi, masu tsara manufofi, manajojin dukiya mai cikakken iko, da masu yanke shawara daga ƙasashen duniya za su halarci taron Kigali don tattauna damarmakin ci gaban Afirka a nan gaba da dabarun sauye-sauyen tattalin arziki.

 

Dare ya ce Najeriya na da niyyar tabbatar da cewa tattalin arzikinta ya ci gaba da kasancewa babban jigon tattaunawar ta hanyar gabatar da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi a matsayin wani ɓangare na dabarun dawo da sahihancin tattalin arziki da kuma jawo hankalin masu zuba jari masu ɗorewa.

 

Ya lissafa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, wadanda suka hada da cire tallafin mai, ‘yantar da darajar musayar kudi, sabunta haraji, rangwamen kayayyakin more rayuwa, sake fasalin bangaren wutar lantarki, kasuwancin iskar gas, da kuma shirye-shiryen fadada tattalin arzikin dijital.

 

A cewarsa, gwamnatin ta fahimci cewa gyare-gyare kadai ba su isa ba sai dai idan an sanar da masu zuba jari yadda ya kamata waɗanda ke buƙatar kwarin gwiwa, bayyana manufofi, hasashen abubuwa, ƙudurin shugabanci, da kuma alkiblar tattalin arziki mai dorewa na dogon lokaci.

 

Dare ya lura cewa duk da rikice-rikicen wucin gadi da ke tattare da gyare-gyare, masu zuba jari na duniya sun fahimci cewa lokutan sauyin tsari galibi suna haifar da wasu daga cikin manyan damarmaki na dogon lokaci na saka hannun jari ga tattalin arziki masu tasowa.

 

Ya ce yawan matasan Najeriya, wurin da ake da shi na dabaru, fadada birane, albarkatun kasa, da damammaki a karkashin Yankin Ciniki Mai ‘Yanci na Nahiyar Afirka sun sanya kasar a matsayin kasa mai karfin gasa a fannin masana’antu da kasuwanci.

 

Mataimakin shugaban ya bayyana Kigali a matsayin wani wuri da ba wai kawai wani wuri na diflomasiyya ba, yana mai cewa wannan wuri ne da za a fara amfani da shi wajen samar da dabarun zuba jari na nahiyar Afirka a Najeriya, kuma wani dandamali ne da Tinubu zai gabatar da shawarar tattalin arzikin Najeriya da kansa.

 

Ya tuna da ayyukan Tinubu a baya a Equatorial Guinea da Tanzania, inda Shugaban ya ci gaba da haɗin gwiwar makamashi, kuɗaɗen samar da ababen more rayuwa, da kuma tattaunawar ci gaban yanki a matsayin wani ɓangare na diflomasiyyar tattalin arzikin nahiyar.

 

Dare ya ce sakon Najeriya a Kigali zai ci gaba da kasancewa a bayyane: gyare-gyare na ci gaba, damammaki suna fadada, ana iya sarrafa hadurra, kuma kasar ta kasance wuri mafi jan hankali a Afirka don zuba jari, kasuwanci, masana’antu, da kuma samun riba mai yawa.

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron shugabannin kamfanoni na Afirka na 2026 zai gudana a Kigali, Rwanda daga ranar 14 ga Mayu zuwa 15 ga Mayu, inda zai tattaro manyan shugabannin kasuwanci sama da 2,000, masu zuba jari da shugabannin gwamnati. (NAN)

 

MUYI/AAA/

 

Fassarar Aisha Ahmed

 

 

 

Sent from my Galaxy

 

Kotu ta yiwa tsohon Ministan Wuta na Najariya daurin shekaru 75

Daga Taiye Agbaje da Chinyere Onuorah

Abuja, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Mista Saleh Mamman, hukuncin daurin shekaru 75 a gidan yari, bayan ya aikata laifukan halatta kudaden haram na Naira biliyan 33.8.

Alkali James Omotosho, wanda ya yanke wa Mamman hukunci a dukkan tuhume-tuhume 12 da hukumar EFCC ta shigar a kansa, ya ba da umarnin cewa hukuncin zai gudana ne a jere ba a lokaci guda ba.

Mai Shari’a Omotosho ya ce, rashin halartar tsohon ministan kotun a yau da kuma ranar da aka dage zaman kotun na karshe, wani yunkuri ne na dakatar da shari’a.

Alkalin, wanda ya amince da lauyan EFCC, Rotimi Oyedepo, SAN, cewa duk da cewa wanda ake tuhuma bai kasance a kotu ba, tanadin Dokar Shari’a ta Shari’a ta Gudanar da Laifuka (ACJA), 2015, ya ba kotun ikon ci gaba da yanke hukunci.

Alkalin ya yanke hukuncin cewa Mamman ba zai iya da’awar cewa ya fuskanci rashin adalci ba.

Saboda haka ya yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin daurin shekaru bakwai a kan laifuka na farko, biyu, uku, shida, bakwai, takwas, tara, goma, 11 da 12 ba tare da zaɓin tara ba.

Alkali Omotosho ya kuma yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru uku a kurkuku a kan tuhuma ta 4 tare da zaɓin tarar Naira miliyan 10 da kuma ɗaurin shekaru biyu a kan tuhuma ta 5 ba tare da zaɓin tarar ba.

Alkalin, wanda ya ba da umarnin a yi hukuncin a jere, ya ce wannan zai fara ne daga ranar da aka kama shi.

Saboda haka, ya umarci dukkan hukumomin tsaro a ciki da wajen ƙasar, ciki har da INTERPOL, da su kama Mammn duk inda aka gan shi, sannan a miƙa shi ga Hukumar Gidajen gyaran hali ta Najeriya don zaman gidan yari.

Dangane da buƙatar lauya mai gabatar da ƙara, wanda lauyan tsohon ministan, Mohammed Ahmed, bai ƙalubalanta ba, Alkali Omotosho ya kuma ba da umarnin a kwace kadarorin Mamman guda biyu da ke yankunan da aka zaɓa a Abuja da kuma kuɗaɗen da hukumomin yaƙi da cin hanci suka kwato a wasu kuɗaɗe daban-daban.

Alkalin ya kuma bayar da umarnin cewa wanda ake tuhuma, ya mayar wa da wanda ake tuhuma da laifin bambancin adadin da ke tsakanin kudaden da kadarorin da aka kwato daga Mamman da kuma Naira biliyan 22 da masu gabatar da kara suka iya tantancewa a lokacin shari’ar, daga cikin Naira biliyan 33.8 da ake zargin an sace daga ayyukan Zungeru da Mambilla Hydro Electric Power.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Alkali Omotosho ya yanke wa Mamman hukunci a ranar 7 ga Mayu bayan ya yi batan dabo kan zargin halatta kudaden haram.

Duk da cewa Mamman bai halarci kotu ba a bayyane, Alkali Omotosho, a hukuncin, ya yanke hukuncin cewa EFCC ta sami damar tabbatar da tuhume-tuhume 12 da aka yi wa wanda ake tuhuma ba tare da wata shakka ba.(NAN)(www.nannews.ng)

TOA/SCO/SH

 

 

Fassarar Aisha Ahmed

 

Satar mutane: Yan sanda sun ceto Likita daga harin gungun mutane bisa zargin sata  

 

Ceto

Daga Suleiman Shehu

Ibadan, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Rundunar ‘yan sanda a jihar Oyo ta ceto wani likitan Najeriya da ke zaune a Amurka, Dakta Afolabi, daga zargi da aka yi masa kan zargin sace wasu mata.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar Oyo, DSP Ayanlade Olayinka, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin da karfe 2:30 na rana a kan titin Ologuneru da ke Ibadan.

A cikin wata sanarwa da aka bai wa manema labarai a Ibadan, Olayinka ya ce taron jama’ar na shirin cinnawa likitan wuta lokacin da tawagar ‘yan sanda ta isa wajen.

Ya ce mutanen sun kona motar likitan kirar Lexus RX 330 SUV.

A cewar Olayinka, wanda abin ya shafa a halin yanzu yana samun kulawar likita a Hukumar Kula da Lafiya ta ‘Yan Sanda, kuma yana samun kulawar gaggawa bayan an yi masa magani.

Olayinka ya ce ‘yan matan biyu, Deborah, mai shekaru 15 da Rebecca, mai shekaru 12, wadanda ake zargin likitan ya sace, an same su ne a cikin motarsa, a halin yanzu kuma suna hannun ‘yan sanda.

Olayinka ya ce, binciken farko ya nuna cewa Afolabi, likita ne da ke aiki a Amurka, ba mai satar mutane ba ne kamar yadda aka zarge shi a cikin rahotannin da ke yawo a shafukan sada zumunta da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce ƙarin binciken ya nuna cewa an kwace ‘yan matan biyu da aka samu a cikin motar Afolabi, bisa doka daga hannun wata Misis Idowu Abimbola a yankin Eleyele da ke Ibadan.

Olayinka ya bayyana cewa za a kai ‘yan matan ne ga mahaifiyar Afolabi, domin taimakawa wajen ayyukan gida.

“A yayin gudanar da bincike, an gayyaci Mrs. Idowu Abimbola zuwa ofishin ‘yan sanda inda ta tabbatar da shirin, yayin da ‘yan matan biyu suka tabbatar da labarin kuma suka yi mu’amala da matar cikin kwanciyar hankali, ta haka ne aka kawar da zargin sace ta.

“Bincike ya nuna cewa rashin fahimtar da ta haifar da kararrawar satar mutane ta karya ta fara ne lokacin da Dr Afolabi ya yi yunkurin shiga ta ƙofar Polytechnic Ibadan, kuma wani mai gadi ya tsayar da shi don duba abin hawa.”

“Bayan sun sauke gilashin taga na motar, an yi zargin an ga ‘yan matan biyu a tsirara, lamarin da ya jawo shakku nan take tsakanin masu kallo da jami’an tsaro.”

“An tattara bayanai cewa rashin iyawar wanda abin ya shafa, wajen bayar da amsoshi masu gamsarwa ga tambayoyin da aka yi masa a wurin, tare da shawarar da ya yanke na kauce wa wurin binciken ababen hawa, ya kara tsananta zargi.”

“Lamarin ya ƙara ta’azzara ne sakamakon rashin iya magana da harshen yankin da kuma bayyana ra’ayoyinsu yadda ya kamata da Turanci, wanda hakan ya ƙara rura wutar ƙaryar satar mutane,” in ji shi.

Kakakin ‘yan sandan ya ce wannan lamari ya haifar da zanga-zanga, inda daga bisani likitocin suka kama matasan da suka fusata suka kuma yi masa mummunan rauni kafin ‘yan sanda su isa wurin.

Olayinka ya ce an samu bayanai daga shaidun gani da ido, ciki har da wani direban Okada da ake zargin an harba a lokacin rudanin da ya biyo baya.

Ya ce ana ci gaba da kokarin gano tare da kama duk mutanen da ke da hannu a cikin rikicin da kuma lalata kadarori.

Olayinka ya ce Kwamishinan ‘Yan Sanda a Jihar Oyo, Mista Abimbola Olugbenga, ya yi Allah wadai da yaɗa labaran ƙarya da ba a tabbatar da su ba waɗanda ke iya haifar da tashin hankali da kuma lalata ribar tsaro da aka samu a jihar. (NAN)(www.nannews.ng)

 

SYS/AOS/AAA/

 

============

Bayo Sekoni ne ya gyara

Fassarar Aisha Ahmed

 

Mutane 25 sun mutu, 14 sun bace a hatsarin jirgin ruwa a Yobe

Hadari

Nabilu Balarabe

Damaturu, Janairu 5, 2026 (NAN) Akalla mutane 25 ne suka mutu yayin da wasu 14 suka bace bayan kifewar wani kwale-kwale a bakin kogin Yobe a garin Garbi, karamar hukumar guru ta jihar.

Dakta Mohammad Goje, Sakataren zartarwa na hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Yobe (YOSEMA), ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Damaturu.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:48 na yamma a ranar 3 ga Janairu, bayan da wadanda abin ya shafa, wadanda galibi manoma ne da ‘yan kasuwa, suka shiga jirgin ruwa a garin Adiyani da ke makwabtaka da Jigawa.

Goje ya ce, “An ruwaito cewa wadanda abin ya shafa, suna dawowa ne daga garin Adiyani, inda suke aikin kamun kifi, noma, da sauran harkokin kasuwanci na gida, lokacin da kwale-kwalen ya kife a tsakiyar tafiya.”

Sakataren zartarwar ya kara da cewa an ceto fasinjoji 13 daga bala’in, kuma suna karɓar magani a asibiti.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike da ceto, inda hukumomin tsaro, masu ba da agajin gaggawa, da kuma masu aikin sa kai na al’umma ke aiki don gano fasinjojin da suka ɓace da kuma gano gawarwakinsu.”

“Tun daga lokacin aka tura tawagar bincike da ceto ta SEMA, daga Bade da Nguru, don tallafawa tawagar da ke ƙasa,” in ji shi.

Goje ya ce, Gwamna Mai Mala Buni ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, sannan ya umurci YOSEMA da ta samar da tallafin lafiya da kayan aiki ga wadanda aka ceto.

Sakataren zartarwar ya tabbatar cewa, gwamnan ya jaddada cewa dole ne a hanzarta ayyukan tura mutane domin ceto rayuka ba tare da ɓata lokaci ba.(NAN)(www.nannews.ng)

NB/YMU

An gyara ta Yakubu Uba

Fassarar Aisha Ahmed

 

Sojojin Guinea-Bissau sun ayyana Janar a matsayin Shugaban sabon mulkin soja a kasar

Gabaɗaya

Dakar, 28 ga Nuwamba, 2025 (dpa/NAN) A ranar Alhamis ne sojojin kasar Guinea-Bissau da ke gabar tekun yammacin Afirka, suka sanar da nada sabon shugaba.

Gidan yada labarai na gwamnati TGB, ya ruwaito cewa Janar Horta Inta-A, zai yi aiki a matsayin shugaban rikon kwarya na tsawon shekara guda.

Ya zuwa yanzu dai, ba a fayyace komai game da daidaiton madafun iko a kasar da kuma yanayin da ake zargin juyin mulkin, kwanaki kadan bayan zaben shugaban kasar zai haifar ba.

Shaidun gani da ido sun shaidawa dpa cewa, titunan babban birnin kasar, Bissau, ba kowa, yayin da aka jibge sojoji a muhimman wurare a fadin birnin.

Kwana daya da ta gabata, wasu gungun jami’ai sun ce sun karbi mulki a kasar mai dauke da mutane kusan miliyan 2.2.

Sun ce sojoji sun bankado wani shiri na magudin zabe da kuma tada zaune tsaye a kasar, wanda ya hada da ‘yan siyasa da masu safarar miyagun kwayoyi.

Guinea-Bissau dai muhimmiyar cibiyar safarar hodar Iblis ce tsakanin Latin Amurka da Turai.

Rahotanni sun ce, shugaba Umaro Sissoco Embaló da aka hambare a yanzu, ya shaidawa kafar yada labaran Faransa cewa sojoji sun tsare shi. Sai dai ya ce ba a yi masa lahani ba.

An kuma ce sojoji sun tsare abokin hamayyar Embaló, Fernando Dias.

Duka Embaló da Dias, sun bayyana kansu a matsayin wadanda suka yi nasara bayan zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar Lahadi. Har yanzu ba a buga sakamakon zaben ba.

Kasar Guinea-Bissau dai ta fuskanci juyin mulki da yunkurin juyin mulki da dama tun bayan samun ‘yancin kai daga kasar Portugal a shekarar 1974.

Sojoji sun shafe shekaru da dama suna shiga siyasa sosai.

Tsohon Janar Embaló yana kan karagar mulki tun shekarar 2020, kuma ya rusa majalisar a karshen shekarar 2023.

A baya dai ya sha yin magana game da yunkurin juyin mulkin da aka yi masa, na baya bayan nan a watan Oktoba.

 

HS

===

Halima Sheji ta gyara

AAA/

Aisha Ahmed ta fassara

 

NELFUND za ta fadada lamuni zuwa ga dalibai masu horon sana’o’i

 

Lamuni

By Funmilayo Adeyemi

Abuja, Nuwamba 18, 2025 (NAN) Asusun bada lamunu na ilimin Najeriya (NELFUND), ya sanar da shirin tsawaita shirin ba da lamuni na dalibai don shirye shiryen koyon sana’o’i.

Manajan Darakta na NELFUND, Akintunde Sawyerr ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a Abuja.

Sawyerr ya ce tsarin fadadawar ya yi dai-dai da shirin gwamnatin tarayya na bunkasa ilimi da fasaha.

Ya kara da cewa matakin ya nuna yadda shugaban kasa Bola Tinubu, ya kuduri aniyar samar da ci gaban jarin masu sana’o’i fiye da ilimin jami’a na gargajiya.

“Babu wata al’umma da masana suka gina su kadai.

“Yana da matukar muhimmanci a sami mutanen da za su iya amfani da hannayensu, a kara masu kuzari, ƙarfafa su, da basira don aiwatar da dabaru masu wayo da ke fitowa daga waɗanda ke fitowa daga cibiyoyin ilimi,” in ji shi.

Sawyerr ya bayyana cewa, yayin da NELFUND ta fi mayar da hankali kan bayar da tallafin kudi ga dalibai a manyan makarantu tun lokacin da aka kaddamar da shi, aka fara shirye-shiryen fadada shi ga masu sana’a da fasaha a fadin kasar.

A cewarsa, mataki na gaba na ci gaban Najeriya yana bukatar daidaito tsakanin kwarewar ilimi da fasaha.

“A NELFUND, muna da hurumin yin sana’o’i.

“Ba mu fara ba tukuna, amma na san cewa gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ta tabbatar da cewa an samu cikakken bayani kan batun.

” Ma’aikatar ci gaban matasa tana yin sana’o’i, ma’aikatar Ilimi ta shiga sana’o’i da kuma ma’aikatar tattalin arziki ta dijital ta shiga cikin dabarun IT.

“Don haka, fasaha wani abu ne da aka sa ma’aikatun gwamnati da yawa da aikatawa.

“Kuma ina ganin a fili yake cewa injiniyan da zai iya yin gini, ya fi injiniyan da zai iya zane kawai.

“Matakin da muke a kasar nan a yanzu, shine abin da zan kira, tsarawa, ginawa, da sarrafa matakin,” in ji shi.

(NAN)( www.nannews.ng )

FAK/ROT

=======

Rotimi Ijikanmi ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara shi.

Nnamdi Kanu ya kori kungiyar lauyoyi masu kare shi, ya kalubalanci hurumin kotu

 

By Taiye Agbaje

Abuja, Oktoba 23, 2025 (NAN) Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), a ranar Alhamis, ya bayyana korar tawagar lauyoyinsa, karkashin jagorancin Cif Kanu Again, SAN, a babbar kotun tarayya dake Abuja.

Kanu, ya shaida wa mai shari’a James Omotosho, a zaman da aka ci gaba da zaman, cewa a shirye yake ya kare kansa.

Biyo bayan matakin da shugaban kungiyar ta IPOB ya dauka, dukkan manyan masu fafutuka a cikin kungiyar da suka hada da Cif Agabi, tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), sun janye daga ci gaba da fitowarsu a shari’ar.

Dangane da wannan al’amari, Kanu, wanda a yake gabatar da jawabi a gaban kotun, ya kalubalanci hurumin kotun da ta gurfanar da shi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa Kanu ya sanya hannu a kan korafinsa kuma ya shigar da shi a ranar 21 ga watan Oktoba.

Ya kuma sanya tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami da sauran su, a matsayin shaidu a ci gaba da shari’ar da ake yi na zargin ta’addanci, kuma ya jera manyan mutane da dama a matsayin shaidu.

Daga cikin wadanda Kanu ya lissafa a matsayin “shaidu masu karfi” akwai Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike; tsohon ministan tsaro, Janar Theophilus Danjuma mai ritaya da kuma tsohon babban hafsan sojin kasa, Janar Tukur Buratai mai ritaya.

Sauran sun hada da, Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas, Gwamna Hope Uzodinma na Imo, ministan ayyuka, Dave Umahi, tsohon Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu, da tsohon Darakta-Janar, Hukumar Leken Asiri ta (NIA), Ahmed Abubakar.

Sauran sun hada da tsohon shugaban hukumar tsaro ta farin kaya, Yusuf Bichi, da kuma shaidu da dama da bai bayyana sunayensu ba.

Kanu, a cikin karar, ya yi alkawarin gabatar da bayanan rantsuwar dukkan shaidun, na son rai ga wannan kotu mai girma, kuma za su sanar da masu gabatar da kara a lokacin da ya  dace.

Hakazalika, NAN ta ruwaito cewa shugaban na IPOB ya yi ganawar sirri da tawagar lauyoyin sa a babbar kotun kasa a Abuja ranar Laraba.

Kanu wanda jami’an hukumar tsaro na farin kaya (DSS) suka gabatar da shi a kotu, ya gana da ‘yan kungiyar llauyoyin nasa a kotun mai shari’a James Omotosho, kamar yadda aka umarta a baya.(NAN)(www.nannews.ng)

TOA/SH

Fassarar Aisha Ahmed 

=====