Zanga zanga ta barke bisa karin farashin man fetur a Kenya

Zanga zanga

Nairobi, 19 ga Mayu, 2026 (Reuters/NAN) Zanga zanga ta barke a wasu garuruwa na Kenya ranar Litinin, saboda karin farashin man fetur, ciki har da yajin aikin sufuri na jama’a, wanda ya tilastawa matafiya tafiya da lafa zuwa wurin aiki.

Kungiyar Sufuri ta kasar, ta ce a ranar Lahadi ya kamata motocin da ke da alaƙa da ƙungiyoyin membobinta su daina aiki daga tsakar dare, don nuna rashin amincewa da hauhawar farashi, inda ‘yan sanda suka yi alƙawarin magance duk wani cikas.

Hukumar Kula da Makamashi da Man Fetur ta Kenya, ta kara farashin mai da kashi 23.5 cikin 100, bayan ta kara farashinsa da kashi 24.2 cikin 100 a watan Afrilu, yayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke kara matsin lamba kan samar da mai da iskar gas a duniya.

A safiyar Litinin, an toshe hanyoyin shiga babban birnin Nairobi ta hanyar masu sufuri da kuma gungun masu zanga-zanga da suka watse.

‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa a wasu yankuna, yayin da wasu masu zanga-zanga suka kunna tayoyi don hana shiga manyan hanyoyi, lamarin da ya kara ta’azzara cunkoso da kuma barin mutane da yawa da ke tafiya a kasa.

A Mombasa, babban birnin tashar jiragen ruwa na Kenya, yajin aikin ya haifar da fargabar jinkirin da ake samu wajen samar da kayayyaki.

Ministan Kudi na kasar, John Mbadi ya shaida wa tashar talabijin ta Citizen cewa, ma’aikatun kudi da makamashi suna fatan ganawa da masu kula da sufuri na jama’a a ranar Litinin don tattauna mafita, yana mai lura da cewa an riga an tallafa wa farashin da ake da shi a yanzu.

“Kenya tana shigo da kusan dukkan kayayyakin mai daga Gabas ta Tsakiya ta hanyar yarjejeniyar gwamnati da gwamnati da masu samar da mai na yankin Gulf.

“Karin farashin mai ya ƙara yawan kuɗin sufuri da kuma ƙara farashin kayan masarufi, wanda hakan ya ƙara matsin lamba ga iyalai da ke fama da tsadar rayuwa,” Ministan yace.

Ma’aikacin hulda da jama’a, Gabriel Odhiambo, mai shekaru 24, ya ce farashin sufurinsa ya ninka sau biyu kuma farashin abinci shi ma ya tashi.

Ya ce yanzu haka, farashin tumatir guda hudu suna kan farashin shilling 60 (cent 50 na Amurka), ƙarin ya ninka sau uku.

Kenya ta ƙara farashin famfon mai na super petrol a Nairobi zuwa 214.25 na Kenya ​shillings ($1.66) a kowace lita daga 206.97, dizal zuwa 242.92 ​shillings daga 196.63 na zagayowar 15 ga Mayu zuwa 14 ga Yuni, yayin da kananzir bai canza ba a shilling 152.78. (Reuters/NAN) ( www.nannews.ng )

 

HLM/CEO/AAA

Edited by Hadiza Mohammed/Chidi Opara

 

Fassarar Aisha Ahmed 

Tinubu ya gabatar da da shawara akan kasuwanci a Najeriya ga Afrika

 

Kasuwanci

Daga Muhydeen Jimoh

Abuja, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Shugaba Bola Tinubu ya ci gaba da jajircewa wajen cigaban Najeriya ta hanyar gyare-gyare da kuma sanya kasar a matsayin babbar hanyar zuba jari a nahiyar Afirka da duniya baki daya.

 

Mista Sunday Dare, mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa ga shugaban kasa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa kafin halartar Tinubu a taron shugabannin Afirka na 2026 da za a yi a Kigali, Rwanda.

 

Sanarwar, mai taken “A Rwanda, Tinubu Ya Bayyana Kasuwancin Najeriya Ga Sauran kasashen Afirka,” ta bayyana Kigali a matsayin matattara ɗaya daga cikin manyan masu zuba jari da gwamnatin ta yi tun lokacin da ta hau mulki.

 

A cewar Dare, sakon Tinubu ga masu zuba jari abu ne mai sauƙi: Najeriya ta kasance ɗaya daga cikin wuraren zuba jari mafi riba a duniya, inda kasuwanci masu inganci za su iya samar da riba mai ban mamaki fiye da tsammanin kasuwa na yau da kullun.

 

Ya ce yayin da yawancin ayyukan tsarin saka hannun jari na duniya ke dawowa tsakanin kashi 20 zuwa 25 cikin 100, Najeriya ta ci gaba da wuce irin wannan hasashen saboda yawan jama’arta, karuwar buƙatu, da kuma saurin bunkasa yanayin gyara.

 

Dare ya ambaci kamfanin sadarwa na MTN Nigeria a matsayin misali, inda ya lura cewa ci gaban kasuwar kamfanin, faɗaɗa masu biyan kuɗi, da kuma ribar da kamfanin ya samu ya wuce tsammanin farko bayan ya shiga kasuwar Najeriya a shekarar 2001.

 

Ya ce MTN Nigeria yanzu tana samar da tiriliyan na nairori kowace shekara, kuma har yanzu tana ɗaya daga cikin kamfanoni mafi daraja da aka jera a kasuwar musayar kuɗi ta Najeriya, wanda ke nuna babbar damar da ƙasar ke da ita ta kasuwanci da kasuwar masu saye.

 

Mataimakin shugaban ya kuma yi nuni da kamfanin MultiChoice, masu tallata DStv, yana mai cewa ayyukan kamfanin a Najeriya sun rikide zuwa daya daga cikin manyan cibiyoyin kasuwanci saboda fadada birane, karuwar amfani da kayayyaki, da kuma yawan jama’a.

 

Dare ya yarda cewa ƙalubalen Najeriya na nan a bayyane kuma wani lokacin ana ƙara gishiri, amma ya dage cewa a ƙarƙashinsu akwai ɗaya daga cikin kasuwannin masu saye mafi zurfi a duniya kuma ɗaya daga cikin al’ummomin da suka fi kasuwanci a Afirka.

 

Ya ce Najeriya tana da damarmakin fadada ababen more rayuwa, bunkasa yanayin fasahar zamani, wadataccen albarkatun ma’adinai, da kuma makamashin da ba a iya misaltawa ba wanda zai iya haifar da ci gaban masana’antu da tattalin arziki mai dorewa a fadin nahiyar Afirka.

 

A cewarsa, taron shugabannin Afirka ya fi wakiltar fiye da taro, yana mai bayyana shi a matsayin kasuwa don jarin saka hannun jari, haɗin gwiwa, alkiblar manufofi, da tattaunawa mai mahimmanci waɗanda ke tsara makomar tattalin arzikin Afirka da gasa.

 

Ya ce sama da manyan jami’ai 2,000, masu zuba jari, masu kudi, masu tsara manufofi, manajojin dukiya mai cikakken iko, da masu yanke shawara daga ƙasashen duniya za su halarci taron Kigali don tattauna damarmakin ci gaban Afirka a nan gaba da dabarun sauye-sauyen tattalin arziki.

 

Dare ya ce Najeriya na da niyyar tabbatar da cewa tattalin arzikinta ya ci gaba da kasancewa babban jigon tattaunawar ta hanyar gabatar da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi a matsayin wani ɓangare na dabarun dawo da sahihancin tattalin arziki da kuma jawo hankalin masu zuba jari masu ɗorewa.

 

Ya lissafa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, wadanda suka hada da cire tallafin mai, ‘yantar da darajar musayar kudi, sabunta haraji, rangwamen kayayyakin more rayuwa, sake fasalin bangaren wutar lantarki, kasuwancin iskar gas, da kuma shirye-shiryen fadada tattalin arzikin dijital.

 

A cewarsa, gwamnatin ta fahimci cewa gyare-gyare kadai ba su isa ba sai dai idan an sanar da masu zuba jari yadda ya kamata waɗanda ke buƙatar kwarin gwiwa, bayyana manufofi, hasashen abubuwa, ƙudurin shugabanci, da kuma alkiblar tattalin arziki mai dorewa na dogon lokaci.

 

Dare ya lura cewa duk da rikice-rikicen wucin gadi da ke tattare da gyare-gyare, masu zuba jari na duniya sun fahimci cewa lokutan sauyin tsari galibi suna haifar da wasu daga cikin manyan damarmaki na dogon lokaci na saka hannun jari ga tattalin arziki masu tasowa.

 

Ya ce yawan matasan Najeriya, wurin da ake da shi na dabaru, fadada birane, albarkatun kasa, da damammaki a karkashin Yankin Ciniki Mai ‘Yanci na Nahiyar Afirka sun sanya kasar a matsayin kasa mai karfin gasa a fannin masana’antu da kasuwanci.

 

Mataimakin shugaban ya bayyana Kigali a matsayin wani wuri da ba wai kawai wani wuri na diflomasiyya ba, yana mai cewa wannan wuri ne da za a fara amfani da shi wajen samar da dabarun zuba jari na nahiyar Afirka a Najeriya, kuma wani dandamali ne da Tinubu zai gabatar da shawarar tattalin arzikin Najeriya da kansa.

 

Ya tuna da ayyukan Tinubu a baya a Equatorial Guinea da Tanzania, inda Shugaban ya ci gaba da haɗin gwiwar makamashi, kuɗaɗen samar da ababen more rayuwa, da kuma tattaunawar ci gaban yanki a matsayin wani ɓangare na diflomasiyyar tattalin arzikin nahiyar.

 

Dare ya ce sakon Najeriya a Kigali zai ci gaba da kasancewa a bayyane: gyare-gyare na ci gaba, damammaki suna fadada, ana iya sarrafa hadurra, kuma kasar ta kasance wuri mafi jan hankali a Afirka don zuba jari, kasuwanci, masana’antu, da kuma samun riba mai yawa.

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron shugabannin kamfanoni na Afirka na 2026 zai gudana a Kigali, Rwanda daga ranar 14 ga Mayu zuwa 15 ga Mayu, inda zai tattaro manyan shugabannin kasuwanci sama da 2,000, masu zuba jari da shugabannin gwamnati. (NAN)

 

MUYI/AAA/

 

Fassarar Aisha Ahmed

 

 

 

Sent from my Galaxy

 

Kotu ta yiwa tsohon Ministan Wuta na Najariya daurin shekaru 75

Daga Taiye Agbaje da Chinyere Onuorah

Abuja, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Mista Saleh Mamman, hukuncin daurin shekaru 75 a gidan yari, bayan ya aikata laifukan halatta kudaden haram na Naira biliyan 33.8.

Alkali James Omotosho, wanda ya yanke wa Mamman hukunci a dukkan tuhume-tuhume 12 da hukumar EFCC ta shigar a kansa, ya ba da umarnin cewa hukuncin zai gudana ne a jere ba a lokaci guda ba.

Mai Shari’a Omotosho ya ce, rashin halartar tsohon ministan kotun a yau da kuma ranar da aka dage zaman kotun na karshe, wani yunkuri ne na dakatar da shari’a.

Alkalin, wanda ya amince da lauyan EFCC, Rotimi Oyedepo, SAN, cewa duk da cewa wanda ake tuhuma bai kasance a kotu ba, tanadin Dokar Shari’a ta Shari’a ta Gudanar da Laifuka (ACJA), 2015, ya ba kotun ikon ci gaba da yanke hukunci.

Alkalin ya yanke hukuncin cewa Mamman ba zai iya da’awar cewa ya fuskanci rashin adalci ba.

Saboda haka ya yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin daurin shekaru bakwai a kan laifuka na farko, biyu, uku, shida, bakwai, takwas, tara, goma, 11 da 12 ba tare da zaɓin tara ba.

Alkali Omotosho ya kuma yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru uku a kurkuku a kan tuhuma ta 4 tare da zaɓin tarar Naira miliyan 10 da kuma ɗaurin shekaru biyu a kan tuhuma ta 5 ba tare da zaɓin tarar ba.

Alkalin, wanda ya ba da umarnin a yi hukuncin a jere, ya ce wannan zai fara ne daga ranar da aka kama shi.

Saboda haka, ya umarci dukkan hukumomin tsaro a ciki da wajen ƙasar, ciki har da INTERPOL, da su kama Mammn duk inda aka gan shi, sannan a miƙa shi ga Hukumar Gidajen gyaran hali ta Najeriya don zaman gidan yari.

Dangane da buƙatar lauya mai gabatar da ƙara, wanda lauyan tsohon ministan, Mohammed Ahmed, bai ƙalubalanta ba, Alkali Omotosho ya kuma ba da umarnin a kwace kadarorin Mamman guda biyu da ke yankunan da aka zaɓa a Abuja da kuma kuɗaɗen da hukumomin yaƙi da cin hanci suka kwato a wasu kuɗaɗe daban-daban.

Alkalin ya kuma bayar da umarnin cewa wanda ake tuhuma, ya mayar wa da wanda ake tuhuma da laifin bambancin adadin da ke tsakanin kudaden da kadarorin da aka kwato daga Mamman da kuma Naira biliyan 22 da masu gabatar da kara suka iya tantancewa a lokacin shari’ar, daga cikin Naira biliyan 33.8 da ake zargin an sace daga ayyukan Zungeru da Mambilla Hydro Electric Power.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Alkali Omotosho ya yanke wa Mamman hukunci a ranar 7 ga Mayu bayan ya yi batan dabo kan zargin halatta kudaden haram.

Duk da cewa Mamman bai halarci kotu ba a bayyane, Alkali Omotosho, a hukuncin, ya yanke hukuncin cewa EFCC ta sami damar tabbatar da tuhume-tuhume 12 da aka yi wa wanda ake tuhuma ba tare da wata shakka ba.(NAN)(www.nannews.ng)

TOA/SCO/SH

 

 

Fassarar Aisha Ahmed

 

Satar mutane: Yan sanda sun ceto Likita daga harin gungun mutane bisa zargin sata  

 

Ceto

Daga Suleiman Shehu

Ibadan, 15 ga Mayu, 2026 (NAN) Rundunar ‘yan sanda a jihar Oyo ta ceto wani likitan Najeriya da ke zaune a Amurka, Dakta Afolabi, daga zargi da aka yi masa kan zargin sace wasu mata.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar Oyo, DSP Ayanlade Olayinka, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Litinin da karfe 2:30 na rana a kan titin Ologuneru da ke Ibadan.

A cikin wata sanarwa da aka bai wa manema labarai a Ibadan, Olayinka ya ce taron jama’ar na shirin cinnawa likitan wuta lokacin da tawagar ‘yan sanda ta isa wajen.

Ya ce mutanen sun kona motar likitan kirar Lexus RX 330 SUV.

A cewar Olayinka, wanda abin ya shafa a halin yanzu yana samun kulawar likita a Hukumar Kula da Lafiya ta ‘Yan Sanda, kuma yana samun kulawar gaggawa bayan an yi masa magani.

Olayinka ya ce ‘yan matan biyu, Deborah, mai shekaru 15 da Rebecca, mai shekaru 12, wadanda ake zargin likitan ya sace, an same su ne a cikin motarsa, a halin yanzu kuma suna hannun ‘yan sanda.

Olayinka ya ce, binciken farko ya nuna cewa Afolabi, likita ne da ke aiki a Amurka, ba mai satar mutane ba ne kamar yadda aka zarge shi a cikin rahotannin da ke yawo a shafukan sada zumunta da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce ƙarin binciken ya nuna cewa an kwace ‘yan matan biyu da aka samu a cikin motar Afolabi, bisa doka daga hannun wata Misis Idowu Abimbola a yankin Eleyele da ke Ibadan.

Olayinka ya bayyana cewa za a kai ‘yan matan ne ga mahaifiyar Afolabi, domin taimakawa wajen ayyukan gida.

“A yayin gudanar da bincike, an gayyaci Mrs. Idowu Abimbola zuwa ofishin ‘yan sanda inda ta tabbatar da shirin, yayin da ‘yan matan biyu suka tabbatar da labarin kuma suka yi mu’amala da matar cikin kwanciyar hankali, ta haka ne aka kawar da zargin sace ta.

“Bincike ya nuna cewa rashin fahimtar da ta haifar da kararrawar satar mutane ta karya ta fara ne lokacin da Dr Afolabi ya yi yunkurin shiga ta ƙofar Polytechnic Ibadan, kuma wani mai gadi ya tsayar da shi don duba abin hawa.”

“Bayan sun sauke gilashin taga na motar, an yi zargin an ga ‘yan matan biyu a tsirara, lamarin da ya jawo shakku nan take tsakanin masu kallo da jami’an tsaro.”

“An tattara bayanai cewa rashin iyawar wanda abin ya shafa, wajen bayar da amsoshi masu gamsarwa ga tambayoyin da aka yi masa a wurin, tare da shawarar da ya yanke na kauce wa wurin binciken ababen hawa, ya kara tsananta zargi.”

“Lamarin ya ƙara ta’azzara ne sakamakon rashin iya magana da harshen yankin da kuma bayyana ra’ayoyinsu yadda ya kamata da Turanci, wanda hakan ya ƙara rura wutar ƙaryar satar mutane,” in ji shi.

Kakakin ‘yan sandan ya ce wannan lamari ya haifar da zanga-zanga, inda daga bisani likitocin suka kama matasan da suka fusata suka kuma yi masa mummunan rauni kafin ‘yan sanda su isa wurin.

Olayinka ya ce an samu bayanai daga shaidun gani da ido, ciki har da wani direban Okada da ake zargin an harba a lokacin rudanin da ya biyo baya.

Ya ce ana ci gaba da kokarin gano tare da kama duk mutanen da ke da hannu a cikin rikicin da kuma lalata kadarori.

Olayinka ya ce Kwamishinan ‘Yan Sanda a Jihar Oyo, Mista Abimbola Olugbenga, ya yi Allah wadai da yaɗa labaran ƙarya da ba a tabbatar da su ba waɗanda ke iya haifar da tashin hankali da kuma lalata ribar tsaro da aka samu a jihar. (NAN)(www.nannews.ng)

 

SYS/AOS/AAA/

 

============

Bayo Sekoni ne ya gyara

Fassarar Aisha Ahmed

 

Mutane 25 sun mutu, 14 sun bace a hatsarin jirgin ruwa a Yobe

Hadari

Nabilu Balarabe

Damaturu, Janairu 5, 2026 (NAN) Akalla mutane 25 ne suka mutu yayin da wasu 14 suka bace bayan kifewar wani kwale-kwale a bakin kogin Yobe a garin Garbi, karamar hukumar guru ta jihar.

Dakta Mohammad Goje, Sakataren zartarwa na hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Yobe (YOSEMA), ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Damaturu.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:48 na yamma a ranar 3 ga Janairu, bayan da wadanda abin ya shafa, wadanda galibi manoma ne da ‘yan kasuwa, suka shiga jirgin ruwa a garin Adiyani da ke makwabtaka da Jigawa.

Goje ya ce, “An ruwaito cewa wadanda abin ya shafa, suna dawowa ne daga garin Adiyani, inda suke aikin kamun kifi, noma, da sauran harkokin kasuwanci na gida, lokacin da kwale-kwalen ya kife a tsakiyar tafiya.”

Sakataren zartarwar ya kara da cewa an ceto fasinjoji 13 daga bala’in, kuma suna karɓar magani a asibiti.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike da ceto, inda hukumomin tsaro, masu ba da agajin gaggawa, da kuma masu aikin sa kai na al’umma ke aiki don gano fasinjojin da suka ɓace da kuma gano gawarwakinsu.”

“Tun daga lokacin aka tura tawagar bincike da ceto ta SEMA, daga Bade da Nguru, don tallafawa tawagar da ke ƙasa,” in ji shi.

Goje ya ce, Gwamna Mai Mala Buni ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, sannan ya umurci YOSEMA da ta samar da tallafin lafiya da kayan aiki ga wadanda aka ceto.

Sakataren zartarwar ya tabbatar cewa, gwamnan ya jaddada cewa dole ne a hanzarta ayyukan tura mutane domin ceto rayuka ba tare da ɓata lokaci ba.(NAN)(www.nannews.ng)

NB/YMU

An gyara ta Yakubu Uba

Fassarar Aisha Ahmed

 

Sojojin Guinea-Bissau sun ayyana Janar a matsayin Shugaban sabon mulkin soja a kasar

Gabaɗaya

Dakar, 28 ga Nuwamba, 2025 (dpa/NAN) A ranar Alhamis ne sojojin kasar Guinea-Bissau da ke gabar tekun yammacin Afirka, suka sanar da nada sabon shugaba.

Gidan yada labarai na gwamnati TGB, ya ruwaito cewa Janar Horta Inta-A, zai yi aiki a matsayin shugaban rikon kwarya na tsawon shekara guda.

Ya zuwa yanzu dai, ba a fayyace komai game da daidaiton madafun iko a kasar da kuma yanayin da ake zargin juyin mulkin, kwanaki kadan bayan zaben shugaban kasar zai haifar ba.

Shaidun gani da ido sun shaidawa dpa cewa, titunan babban birnin kasar, Bissau, ba kowa, yayin da aka jibge sojoji a muhimman wurare a fadin birnin.

Kwana daya da ta gabata, wasu gungun jami’ai sun ce sun karbi mulki a kasar mai dauke da mutane kusan miliyan 2.2.

Sun ce sojoji sun bankado wani shiri na magudin zabe da kuma tada zaune tsaye a kasar, wanda ya hada da ‘yan siyasa da masu safarar miyagun kwayoyi.

Guinea-Bissau dai muhimmiyar cibiyar safarar hodar Iblis ce tsakanin Latin Amurka da Turai.

Rahotanni sun ce, shugaba Umaro Sissoco Embaló da aka hambare a yanzu, ya shaidawa kafar yada labaran Faransa cewa sojoji sun tsare shi. Sai dai ya ce ba a yi masa lahani ba.

An kuma ce sojoji sun tsare abokin hamayyar Embaló, Fernando Dias.

Duka Embaló da Dias, sun bayyana kansu a matsayin wadanda suka yi nasara bayan zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar Lahadi. Har yanzu ba a buga sakamakon zaben ba.

Kasar Guinea-Bissau dai ta fuskanci juyin mulki da yunkurin juyin mulki da dama tun bayan samun ‘yancin kai daga kasar Portugal a shekarar 1974.

Sojoji sun shafe shekaru da dama suna shiga siyasa sosai.

Tsohon Janar Embaló yana kan karagar mulki tun shekarar 2020, kuma ya rusa majalisar a karshen shekarar 2023.

A baya dai ya sha yin magana game da yunkurin juyin mulkin da aka yi masa, na baya bayan nan a watan Oktoba.

 

HS

===

Halima Sheji ta gyara

AAA/

Aisha Ahmed ta fassara

 

NELFUND za ta fadada lamuni zuwa ga dalibai masu horon sana’o’i

 

Lamuni

By Funmilayo Adeyemi

Abuja, Nuwamba 18, 2025 (NAN) Asusun bada lamunu na ilimin Najeriya (NELFUND), ya sanar da shirin tsawaita shirin ba da lamuni na dalibai don shirye shiryen koyon sana’o’i.

Manajan Darakta na NELFUND, Akintunde Sawyerr ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a Abuja.

Sawyerr ya ce tsarin fadadawar ya yi dai-dai da shirin gwamnatin tarayya na bunkasa ilimi da fasaha.

Ya kara da cewa matakin ya nuna yadda shugaban kasa Bola Tinubu, ya kuduri aniyar samar da ci gaban jarin masu sana’o’i fiye da ilimin jami’a na gargajiya.

“Babu wata al’umma da masana suka gina su kadai.

“Yana da matukar muhimmanci a sami mutanen da za su iya amfani da hannayensu, a kara masu kuzari, ƙarfafa su, da basira don aiwatar da dabaru masu wayo da ke fitowa daga waɗanda ke fitowa daga cibiyoyin ilimi,” in ji shi.

Sawyerr ya bayyana cewa, yayin da NELFUND ta fi mayar da hankali kan bayar da tallafin kudi ga dalibai a manyan makarantu tun lokacin da aka kaddamar da shi, aka fara shirye-shiryen fadada shi ga masu sana’a da fasaha a fadin kasar.

A cewarsa, mataki na gaba na ci gaban Najeriya yana bukatar daidaito tsakanin kwarewar ilimi da fasaha.

“A NELFUND, muna da hurumin yin sana’o’i.

“Ba mu fara ba tukuna, amma na san cewa gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ta tabbatar da cewa an samu cikakken bayani kan batun.

” Ma’aikatar ci gaban matasa tana yin sana’o’i, ma’aikatar Ilimi ta shiga sana’o’i da kuma ma’aikatar tattalin arziki ta dijital ta shiga cikin dabarun IT.

“Don haka, fasaha wani abu ne da aka sa ma’aikatun gwamnati da yawa da aikatawa.

“Kuma ina ganin a fili yake cewa injiniyan da zai iya yin gini, ya fi injiniyan da zai iya zane kawai.

“Matakin da muke a kasar nan a yanzu, shine abin da zan kira, tsarawa, ginawa, da sarrafa matakin,” in ji shi.

(NAN)( www.nannews.ng )

FAK/ROT

=======

Rotimi Ijikanmi ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara shi.

Nnamdi Kanu ya kori kungiyar lauyoyi masu kare shi, ya kalubalanci hurumin kotu

 

By Taiye Agbaje

Abuja, Oktoba 23, 2025 (NAN) Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), a ranar Alhamis, ya bayyana korar tawagar lauyoyinsa, karkashin jagorancin Cif Kanu Again, SAN, a babbar kotun tarayya dake Abuja.

Kanu, ya shaida wa mai shari’a James Omotosho, a zaman da aka ci gaba da zaman, cewa a shirye yake ya kare kansa.

Biyo bayan matakin da shugaban kungiyar ta IPOB ya dauka, dukkan manyan masu fafutuka a cikin kungiyar da suka hada da Cif Agabi, tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), sun janye daga ci gaba da fitowarsu a shari’ar.

Dangane da wannan al’amari, Kanu, wanda a yake gabatar da jawabi a gaban kotun, ya kalubalanci hurumin kotun da ta gurfanar da shi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa Kanu ya sanya hannu a kan korafinsa kuma ya shigar da shi a ranar 21 ga watan Oktoba.

Ya kuma sanya tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami da sauran su, a matsayin shaidu a ci gaba da shari’ar da ake yi na zargin ta’addanci, kuma ya jera manyan mutane da dama a matsayin shaidu.

Daga cikin wadanda Kanu ya lissafa a matsayin “shaidu masu karfi” akwai Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike; tsohon ministan tsaro, Janar Theophilus Danjuma mai ritaya da kuma tsohon babban hafsan sojin kasa, Janar Tukur Buratai mai ritaya.

Sauran sun hada da, Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas, Gwamna Hope Uzodinma na Imo, ministan ayyuka, Dave Umahi, tsohon Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu, da tsohon Darakta-Janar, Hukumar Leken Asiri ta (NIA), Ahmed Abubakar.

Sauran sun hada da tsohon shugaban hukumar tsaro ta farin kaya, Yusuf Bichi, da kuma shaidu da dama da bai bayyana sunayensu ba.

Kanu, a cikin karar, ya yi alkawarin gabatar da bayanan rantsuwar dukkan shaidun, na son rai ga wannan kotu mai girma, kuma za su sanar da masu gabatar da kara a lokacin da ya  dace.

Hakazalika, NAN ta ruwaito cewa shugaban na IPOB ya yi ganawar sirri da tawagar lauyoyin sa a babbar kotun kasa a Abuja ranar Laraba.

Kanu wanda jami’an hukumar tsaro na farin kaya (DSS) suka gabatar da shi a kotu, ya gana da ‘yan kungiyar llauyoyin nasa a kotun mai shari’a James Omotosho, kamar yadda aka umarta a baya.(NAN)(www.nannews.ng)

TOA/SH

Fassarar Aisha Ahmed 

=====

 

Shugabar wata karamar hukuma a Legas ta haramta cinikin gefen hanya

Gefen hanya

Daga Idris Olukoya

Epe (Lagos), Oktoba 23, 2025 (NAN) Shugabar karamar hukumar Epe ta jihar Legas, Ms. Surah Animashahun, ta yi gargadi da a daina yin ciniki a gefen titi a yankin, saboda hadurran da ke tattare hakan da kuma cunkoson ababen hawa.

Animashahun, ta shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Alhamis cewa, matakin ya zama dole domin inganta zirga-zirgar ababen hawa, da inganta lafiyar jama’a, da kuma maido da tsari a wuraren da jama’a ke cunkoso.

Ta ce, an kai samame ne a kan muhimman wurare kamar; Kasuwar Aiyetoro, Tsohon Garage Ijebu-Ode, Ita-Opo, Kasuwar Inuwa da sauran wuraren da aka gano a cikin al’umma.

“Yan kasuwa a wadannan yankuna sun samu koma bayan tsarin hanya da kuma hanyoyin tafiya, domin hakan  na haifar da hadari mai tsanani.

“Daga yanzu, majalisar ba za ta amince da yin cinikin gefen hanya ba, saboda hadurra da cunkoson ababen hawa,” in ji ta.

Shugaban ya ce jami’an kungiyar yaki da rashin da’a ta Kick Against Indiscipline (KAI), za su zagaya domin gudanar da ayyukan dakile cin hanci da rashawa da ake yi a kan tituna a fadin al’umma.

Animashahun, ta kuma bayyana cewa, an samu hadurra da dama a kan titin Aiyetoro, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi sakamakon tukin ganganci.

“Ba za mu iya ci gaba da jure asarar rayuka da dukiyoyi ba sakamakon rashin da’a daga mutanenmu, saboda hanyoyin mota ne, ba na kasuwanci ba,” in ji ta.

Ta bayyana cewa, karamar hukumar ta samar da wurin da ya dace a bayan kasuwar Aiyetoro domin ‘yan kasuwa su gudanar da harkokinsu lafiya ba tare da hana zirga-zirga ba.

“Mun yi isassun shirye-shirye domin ‘yan kasuwarmu su yi cinikinsu a bayan kasuwa, inda masu ababen hawa ba sa wucewa, a hukumance an kebe wurin domin yin ciniki,” inji ta.

Shugaban karamar hukumar, ta bada tabbacin cewa ana ci gaba da kokarin sake gina kasuwar Aiyetoro, wadda ta ruguje a zamanin gwamnatin tsohon gwamna Akinwunmi Ambode.

Ta kara da cewa, nan ba da dadewa ba, za a sake gina kasuwar a karkashin jagorancin Gwamna Babajide Sanwo-Olu, inda ta cigaba da cewa, tattaunawa da tsare-tsare sun yi nisa.

NAN ta ruwaito cewa, ‘yan kasuwa a wuraren da abin ya shafa kamar, Aiyetoro, Ita-Opo, Shade, Popo Oba, da Papa, an umurce su da su koma kasuwannin da gwamnati ta amince da su.

Karamar hukumar ta kara yi gargadin cewa, duk dan kasuwan da ya karya dokar zai fuskanci takunkumi a atisayen aiwatar dokar a gaba.

Animashahun ta cigaba da cewa ba wai an yi wannan shiri ne don farautar kowa ba, sai don tabbatar da tsari, da’a da kuma tsaron mazauna yankin.

Ta yi kira ga shugabannin kasuwar, da shugabannin al’umma da su wayar da kan ‘ya’yansu akan muhimmancin bin doka da oda, inda ta jaddada cewa gyare-gyaren harkokin gudanar da birane za su ci gaba da samun fifiko a karkashin gwamnatinta. (NAN)(www.nannews.ng).

 

SIO/KOLE/CHOM

========

 

Remi Koleoso/Chioma Ugboma ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara

Wata gidauniya ta zaburar da sarakuna domin yaki da cin zarafin mata a Bauchi

Daga Amina Ahmed

Ningi (Bauchi srate), Oktoba 23, 2025 (NAN) Wata kungiya mai zaman kanta, Ikra Foundation for Women and Youth Development (IKFWYD), ta fara wani shiri na shekaru biyu, don zaburar da maza wajen magance cin zarafi.(GBV).

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa ana aiwatar da shirin ne a kananan hukumomin Bauchi, Ningi, da Toro.

Jami’in sa ido da tantancewa na gidauniyar, Isma’il Umar ne ya bayyana hakan a wani taron bayar da shawarwari da aka gudanar da hakiman kananan hukumomi a garin Ningi.

Ya ce rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa na yin tasiri mai kyau wajen canza halayya tare da hana wuce gona da iri ba.

“An tsara shirin ne domin jawo hankalin maza, kan batutuwan da suka shafi kare hakkin mata da ‘ya’ya mata baki daya.

“Ba za a iya samun jin daɗin iyali da haɗin kai ba, ba tare da sa hannun maza ba,” in ji shi.

Umar ya lura cewa, kalubale kamar rashin fahimtar juna ta jinsi, rashin fahimtar juna a cikin gida, rashin fahimtar juna a tsakanin ma’aurata, da karancin sanin nauyin da ya rataya a wuyansu na haifar da rashin zaman lafiya a iyali.

“In aka mayar da hankali ga maza a matsayin abokan haɗin gwiwa don inganta zaman lafiya da walwala, wannan shirin yana da nufin ƙarfafa tasirin su a cikin iyalai da al’ummomi,” in ji shi.

Umar ya kara da cewa, shirin zai samar da hadin kai tsakanin maza da mata, wajen wanzar da zaman lafiya a gidajen aure.

Shi ma da yake jawabi, Mista Bamidele Jacobs, Daraktan Shari’a na Lauyoyin Alert, ya ce Lauyoyin ALert da Iqra Foundation, za su aiwatar da shirin na tsawon shekaru biyu.

A cewarsa, maza na da matukar muhimmanci wajen dakile barazanar GBV, ya kara da cewa za a zabi zakarun maza don gudanar da shirin.

A nasu jawabai mabambanta, sarakunan gargajiya sun bayyana goyon bayansu da jajircewarsu ga shirin.

Hakimin Ningi, Alhaji Yusuf Danyaya, ya yi alkawarin zaburar da maza domin gudanar da wannan shiri, inda ya ce “gidan da babu tashin hankali yana haifar da zaman lafiya a cikin al’umma.”

Hakazalika, Hakimin Miri da ke cikin birnin Bauchi, Alhaji Hussaini Uthman, ya ce manufar shirin ta yi daidai da irin rawar da shugabannin al’umma ke takawa wajen samar da sulhu a tsakanin ma’aurata.

A nasa bangaren, Hakimin Toro, Alhaji Umar Adamu, ya ce, yin jawabi akan GBV, wani nauyi ne da ya rataya a wuyansu domin tabbatar da cewa al’umma sun kasance cikin aminci da lumana. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AE/BEKl/KLM

iEdited by Abdulfatai Beki/Muhammad Lawal

Fassarar Aisha Ahmed