Gwamnatin Tarayya ta jajantawa Gwamna Bago, al’ummar Nijar bisa fashewar tankar mai

Ta’aziyya

By Collins Yakubu-Hammer

Abuja, Oktoba 23, 2025 (NAN) Gwamnatin tarayya ta jajanta wa gwamnati da al’ummar Neja bisa fashewar wata tankar man fetur a garin Essa, da ke karamar hukumar Katcha a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar ranar Alhamis a Abuja

Takardar ta bayyana matukar alhininsa bisa afkuwar lamarin da yayi sanadin salwantar rayuka da kuma jikkata wasu da dama.

“Muna tare da gwamnati da al’ummar jihar Neja wajen jimamin wannan rashi.

“Wannan lamari mai ratsa zuciya, ya sake haifar da mummunar illar hadurran tankar mai a cikin al’ummarmu.

“Gwamnatin tarayya, ta yi bakin cikin cewa, duk da cigaba da wayar da kan jama’a tare da gargadi game da illolin kwasar man fetur daga fadowar tankunan man fetur, har yanzu wasu na yin kasadar da ke barazana ga rayuwa.

“Kowane ran dan Najeriya yana da daraja, kuma irin wadannan bala’o’in za a iya kauce musu sun zama izina domin ƙarin kulawa da bin umarnin tsaro,” in ji Idris.

Ya yaba da yadda gwamnatin Neja, hukumomin tsaro da masu bada agajin gaggawa, suka gaggauta daukar matakin kashe gobarar, tare da ceto wadanda suka tsira da rayukansu, kuma suka bayar da tallafi ga iyalan wadanda abin ya shafa.

Ministan ya ce an kuma umurci Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), da ta kara kaimi akan kokarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agaji da magunguna ga wadanda abin ya shafa da iyalansu.

“Gwamnatin tarayyar ta kuma umurci hukumar wayar da kan jama’a ta kasa, da ta kara kaimi wajen wayar da kan jama’a a fadin kasar.

“A kara tsaurara matakan tsaro, musamman a yankunan karkara da masu fama hadariurra, domin hana sake afkuwar irin wannan bala’i.

“Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da wadanda abin ya shafa tare da iyalansu, da daukacin al’ummar Neja a wannan lokaci na bakin ciki.

“Allah Ya jikan wadanda suka rasu, kuma Allah Ya bawa ‘yan’uwansu ikon jure wannan rashi mai raɗaɗi,” in ji Idris. (NAN) (www.nannews.ng)

 

CMY/BEKl/BRM

==============

Edited by Abdulfatai Beki/Bashir Rabe Mani

Fassarar Aisha Ahmed

 

Wata mata ta nemi kotu ta raba aurenta saboda rashin soyayya

Soyayya

By: Mujidat Oyewole

Ilorin, Oct. 23, 2025 (NAN) Wata mata mai suna Misis Hajara Busari, ta roki wata kotu da ke garin Ilorin, da ta raba aurenta da mijinta, Mista Mumini Anafi, shekaru shida da suka gabata, saboda rashin soyayya.

Mai shigar da kara ta shaida wa kotun a ranar Alhamis cewa, ita ba ta da sha’awar auren na bisa addinin Musulunci da mijinta, kuma ta bukaci kotun da ta raba su.

Tace tana neman umarnin a raba aure, kuma a bata hakkin kula da ‘ya’yanta uku, da kuma kudi N50,000, a matsayin kudin kula da ‘ya’yanta.

A halin da ake ciki, mijin da ake kara, ya shaida wa kotun cewa har yanzu yana sha’awar zaman aure da matarsa, kuma ya bukaci kotun da kada ta yi sassauci akan abunda mai shigar da kara ya nema.

Alkalin kotun, Mista Toyin Aluko, ya bukaci maigidan da ya binciko duk wata dama da zai samu, domin samun sulhu cikin lumana kan duk wata takaddama da matarsa.

Kotun ta dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 17 ga watan Disamba, domin samun rahoton sasantawa ko kuma sauraron karar. (NAN)www.nannews.ng

 

MOB/UNS

======

 

Sandra Umeh ta gyara

Aisha Ahmed ta Fassara

Hukumar NESREA ta lalata buuhunan sassan jikin jakuna 700 da Kwastam ta mika mata

Jaki

Doris Esa

Abuja, Oktoba 16, 2025 (NAN) Hukumar Kula da Muhalli ta Kasa (NESREA) ta ce, ta lalata buhunan sassan jikin jakuna 700 da Hukumar Kwastam ta Najeriya ta mika mata a Kaduna.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Misis Nwamaka Ejiofor, mataimakiyar daraktar yada labarai ta NESREA ta fitar a Abuja.

Ta ce hakan ya yi daidai da ka’idojin muhalli da ka’idojin aminci.

Ejiofor ta ce, an lalata kasusuwan jakuna da fatun ne a ranar 3, 4 da 6ga watan Oktoba, a Kaduna.

“An yi amfani da wurare guda biyu don kona kasusuwan, yayin da aka binne fatun a wani wuri da aka kebe.

 “An gudanar da atisayen ne a gaban jami’an tsaro kuma bisa ka’idojin muhalli,” in ji shi.

Ta ce an samu nasarar gudanar da atisayen ne ta hanyar hadin gwiwar hukumar ta NESREA da hukumar Kwatam.

Ejiofor ta kara da cewa, sun tabbatar da cewa an yi aikin ne cikin aminci da kiyaye muhalli.

“Wannan ya nuna gagarumar nasara, a kokarin da ake na yaki da fataucin namun daji da kuma kare nau’o’in su da ke cikin hadari.

 “An gudanar da aikin ne a ƙarƙashin tsauraran ka’idojin hadin gwuiwa, don hana duk wani haɗarin muhalli ko lafiya.

“Ma’aikatun da ke cikin atisayen sun sanya kayan kariya na sirri, kuma an dauki matakan rage hadarin kamuwa da duk wata illar da za ta shafi rayuka,” in ji ta.

Ejiofor ta jaddada cewa hukumar NESREA a watan Yuli ta kona sama da buhu dari na al’aurar jakuna da hukumar kwastam ta Najeriya ta mika a Abuja.

Darakta Janar na Hukumar NESREA, Farfesa Innocent Barikor, ya koka da yadda jakuna ke raguwa a Najeriya, ya yi gargadin cewa sannu a hankali suna mutuwa.

Barikor ya jaddada tsayuwar daka da gwamnatin Najeriya ta ke yi na yaki da safarar jakuna ba bisa ka’ida ba.

Ya ce an dauki jakuna dabbobin gida, amma bukatarsu da masu safarar miyagun kwayoyi suke yi don yin maganin kara karfin sha’awa, ya sa gwamnatin tarayya ta ba da umarnin hana sayar da ita.

Barikor ya ce, lalata sassan jakunan da hukumar NESREA da NCS suka yi, an yi shi ne don hana fataucin jakunan ba bisa kaida ba.

Ya yi godiya ga hukumar ta Kwastam bisa gagarumin goyon baya ga yaki da fataucin miyagun kwayoyi da ke cikin hadari. (NAN) (www.nannews.ng)

 

Chidi Opara ya gyara ORD/CEO

Aisha Ahmed Ta fassara.

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da karin kasafin N75bn

 

Kasafin kudi

by Aisha Ahmed 

Dutse, Sept.18, 2025 (NAN) Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da karin kasafin kudi na Naira biliyan 75, na kasafin kudi na shekarar 2025, domin mikawa majalisar dokokin jihar gaba daya.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Mista Sagir Musa ne ya bayyana haka, a wata hira da aka yi da shi ranar Laraba a Dutse, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartarwa ta jiha. 

Ya ce rabon kasafin ya taso ne saboda karin kudaden shiga da aka samu.

“Dalilin kara kasafin kudin shine don magance bukatun kudi da suka kunno kai da kuma karfafa bangarorin da muka sa a gaba domin samun ci gaba mai dorewa a fadin jihar. 

“Alkaluman da aka amince da su sun kai biliyan ₦58 na Gwamnatin Jiha, da kuma Naira biliyan 17 na kananan hukumomi 27, wanda ya hada da na yau da kullum da kuma manyan kudade,” inji shi.

Ƙarin kasafin, in ji shi, zai haɓaka ayyuka da shirye-shirye masu gudana a sassa masu mahimmanci kamar ilimi, kiwon lafiya, kayayyakin more rayuwa, aikin gona, da sauran  ayyukan ci gaba.

Ya ce hakan zai kuma bayar da tallafin kasafin kudi don sabbin bukatu na kashe kudi da ba a zata ba, tare da daidaita kashe kudaden jama’a tare da tattalin arziki da kuma manufofin ci gaba.

Kwamishinan ya ce, za a mika kudurin karin kasafin kudin ga majalisar dokokin jihar ta Jigawa, domin tantancewa tare da amincewa da shi, kamar yadda tsarin mulki ya tanada. 

Musa ya ce, matakin ya nuna yadda gwamnati ta himmatu wajen tabbatar da gudanar da mulki cikin gaskiya, kula da harkokin kudi da kuma samar da ingantaccen hidima ga daukacin al’ummar Jigawa.

NAN ta ruwaito cewa, Gwamna Umar Namadi ya sanya hannu kan kasafin kudin jihar na shekarar 2025 na Naira biliyan 698.3 a ranar 1 ga watan Janairu, wanda ya kasance  mafi girma a tarihin jihar.

A nasa jawabin, Namadi ya bayyana kasafin a matsayin mai kawo sauyi da kuma muhimmanci ga ci gaban jihar cikin dogon lokaci.

“Kasafin kudin bana na Naira biliyan 698.3 shi ne mafi girma a tarihin jihar Jigawa, an tsara shi ne domin sake fasalin jihar zuwa mafi girma,” inji shi.

Kashi 76 cikin 100 na kasafin kudin an ware su ne ga manyan ayyuka, wanda hakan ya nuna muhimmancin gwamnatin kan samar da ababen more rayuwa da ci gaba.

Namadi ya bayyana cewa, wadannan jarin za su kafa tushen ci gaban tattalin arziki mai dorewa da kuma inganta rayuwar al’umma a fadin jihar.  (NAN) (www.nannews.ng)

 

AAA/SH

Rahoto da fassarar Aisha Ahmed

Najeriya na asarar dala biliyan 10 a duk shekara sakamakon asarar bayan girbi – Kyari  

 

Bayan girbi

Daga Aisha Ahmed 

07030065142

Kangire, (Jigawa), Satumba 16, 2025 (NAN) Ministan Noma da Samar da Abinci, Sen. Abubakar Kyari, ya ce Najeriya na asarar dala biliyan 10 a duk shekara sakamakon asarar da ake yi bayan girbi.

Kyari ya bayyana haka ne a yayin bikin kaddamar da kungiyar noma da samar da ababen more rayuwa a karkara (GRAIN) Pulse Center a kauyen Kangire, na karamar hukumar Birnin-Kudu, Jigawa.

Ya ce ana tafka asara ne sakamakon rashin wajen ajiya, rashin ababen more rayuwa, karancin kayan sarrafawa, dumamar yanayi, ambaliyar ruwa, gurbacewar kasa, da karuwar ruwan sama a fadin kasar.

A cewarsa, noma na bayar da kusan kashi 24 cikin 100 na GDPn Najeriya, inda kananan manoma ke noma kusan kashi 70 cikin 100 na abincin kasar.

“Ta hanyar karfafa wa kananan manoma da kayan aiki na zamani, fasaha, da kasuwanni, za mu iya zakulo cikakkiyar arzikin ƙasarmu da mutanenmu,” in ji Ministan.

 Kyari ya jaddada kudirin gwamnatin shugaba Bola Tinubu, na baiwa harkar noma fifiko a matsayin ginshikin kawo sauyi ga al’ummar kasar, yana mai jaddada cewa an mayar da hangen nesa zuwa aikace.

Ya bayyana yadda tsare-tsaren kamfanoni masu zaman kansu ke da muhimmancin gaske wajen karfafa tsarin abinci a Najeriya da kuma karfafa juriya kan asarar da ake yi bayan girbi.

Ministan ya ce, cibiyar pulse zata yi aiki ne a matsayin hadaddiyar cibiyar noma, samar da ababen more rayuwa, da raya karkara, ta yadda za ta hada dukkan sassan aikin gona waje guda.

Ya kara da cewa, cibiyar da aka tanadar na da kayan aiki na zamani, za ta samar da yanayi mai aminci na fitar da kayayyaki zuwa kasashen ketare, kuma za a yi irin ta a fadin kasar baki daya.

Har ila yau, Ministan Harkokin Waje, Amb. Yusuf Tuggar, ya jaddada karfin hadin gwiwar gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu, wajen ci gaba.

Ya kuma yaba da yadda aka samar da irin wadannan cibiyoyi a cikin al’ummomin noma na Jigawa.

“Wannan yunkuri zai amfanar da Najeriya saboda fa’idodi da yawa, musamman haɗa kayan aiki da fasaha na zamani,” in ji Tuggar.

Ya yabawa shugaba Tinubu da gwamnan Jigawa ta Umar Namadi, kan yadda suka ba da fifiko wajen samar da abinci a cikin manufofin ci gaban su.

Gwamna Namadi ya bayyana jin dadinsa da yadda Jigawa ta karbi bakuncin cibiyar na farko a kasar, inda ya bayyana ta a matsayin wata kyakkyawar fasaha domin dorewar rayuwar karkara.

Ya ce aikin zai zaburar da tattalin arziki, tare da nuna sauye-sauyen da al’umma za su samu ta hanyar bunkasa noma.

Namadi ya bayyana cewa, wurin ya hada da tsarin hadaka mai amfani da hasken rana, cibiyoyin sadarwa na zamani, da kuma hidimomin da suka kunshi dukkan sassan darajar aikin gona.

Ya nanata kudirin gwamnatinsa na karfafa aikin gona domin samar da ayyukan yi, fadada ababen more rayuwa, da inganta rayuwa.

Shugaban Karamar Hukumar Birnin-Kudu, Mista Muhammad Uba, ya yi alkawarin ba da goyon baya ga ajandar Shugaba Tinubu, inda ya bayyana yadda jihar Jigawa ta ba da fifiko a fannin noma da samar da abinci.

Ya kara da cewa Gwamna Namadi ya dauki muhimman matakai domin kawo sauyi da kuma daidaita harkar noma a jihar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Kyari ya kaddamar da cibiyar GRAIN Pulse Centre a Kangire, a wani bangare na shirin sabunta bege. (NAN) (www.nannews.ng)

AAA/KTO

 

======

Fassarar Aisha Ahmed

Jihar Kaduna ta fadada hanyoyin karkara domin bunkasa noma

 

Hanya

 

By Mustapha Yauri

 

Zaria (Jihar Kaduna) Satumba 8, 2025 (NAN) Gwamnatin jihar Kaduna ta fara aikin gina titunan karkara a fadin jihar domin bunkasa harkokin noma a jihar.

Yunkurin dai na nufin saukaka zirga-zirgar kayan amfanin gona, tare da inganta kasuwannin manoma da kuma karfafuwar samar da abinci a fadin jihar.

Babban sakataren ma’aikatar noma, Alhaji Umar Abba ne, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a Zariya, cewa, shirin na da nufin rage asarar da ake samu bayan girbi.

Ya ce, gwamnatin Gwamna Uba Sani, ta jajirce wajen samar da hanyoyin shiga karkara, domin karfafa ayyukan noma da bunkasa zamantakewa da tattalin arziki, tare da ci gaban al’umma baki daya.

Abba ya kara da cewa, shirin na hadin gwiwa ne tsakanin bankin duniya da gwamnatin jihar Kaduna, a karkashin shirin samar da ayyukan noma na karkara (RAAMP).

Babban sakataren ya ci gaba da cewa, a kwanakin baya ma’aikatar ta gudanar da ziyarar gani da ido, a kashi na biyu na wasu al’ummomin da suka ci gajiyar ayyukan hanyoyin.

Sakataren ya bukaci ‘yan kwangila, da su kammala ayyukan cikin gaggawa tare da kiyaye ka’idoji.

Hakazalika, Ko’odinetan ayyukan, Malam Zubairu Abubakar, ya zayyana wasu daga cikin ayyukan hanyoyin da ake gudanarwa a matakai daban-daban.

Ya ce sun hada da tituna Sama da kilomita 50 na Fala zuwa Sayasaya, Masama Gadas zuwa Anchau Road a karamar hukumar Ikara.

Sauran in ji shi, sun hada da titin Gora zuwa Kwoi, mai tsawon kilomita 3.5 a karamar hukumar Jaba, sannan titin Aduwan Gida zuwa Fadan Kaje mai nisan kilomita 5.6 a Zonkwa.

Akwai kuma na karamar hukumar Zangon Kataf da titin Illa zuwa Kofato, mai kilomita 13.4 a karamar hukumar Igabi da titin Sabon Tasha zuwa Juji zuwa Unguwar Barde da sauransu.

A cewar mai gudanar da aikin, duk ayyukan hanyoyin shiga karkara karkashin RAAMP, za a kammala sune a karshen shekarar 2025.

Don haka, ya yi kira ga mazauna yankin da masu amfani da hanyoyin, da su ci gaba da bada hadin kai ga ‘yan kwangilar, domin kammala da ayyukan cikin sauki da kuma dace. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AM/KLM

Fassarar Aisha Ahmed

 

Al’ummar Adamawa sun koka da barkewar bakuwar cuta

Daga Ibrahim Kado

Fufore (Adamawa), Satumba 5, 2025 (NAN) Mazauna garin Malabo a karamar hukumar Fufore ta jihar Adamawa, sun nuna damuwarsu kan barkewar wata bakuwar cuta da ke damun sassan jiki tare da haifar da radadi mai tsanani.

Wasu majinyata da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Malabo a ranar Juma’a, sun ce cutar kan fara ne kamar borin jiki, daga baya kuma sai ta watsu, kuma a hankali tana cin naman jiki tare da lalata kasusuwa.

Misis Phibi Sabo, ta ce ta shafe makonni tana fama da cutar.

“Abun ya fara kamar borin jiki mai zafi, daga baya ya kumbura ya fashe, sa’an nan ya fara cinye naman da ke kafada, yana lalata kasusuwa kuma ya jawo mun ciwo mai tsanani.

“Hakan ya sa ni rauni a fili, ba zan iya bayyana abin da ke faruwa da ni ba, duk da cewa na ziyarci asibiti kuma na sami magunguna,” in ji Sabo.

Ta yi kira ga gwamnati da tallafa, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin majinyata ba za su iya yin ayyukansu na yau da kullum ko kuma tallafa wa iyalansu ba.

“Don Allah, muna son taimakon gwamnati kafin al’ummarmu ta salwanta,” Sabo ya yi kuka.

Ta kuma jaddada bukatar gwamnati ta binciki musabbabin cutar, tare da samar da kayan agaji ga gidajen da lamarin ya shafa.

Wani da abin ya shafa, Malam Junaidu Adamu, shi ma ya ce ya shafe sama da watanni biyu yana fama da irin wannan ciwon, ya bayyana irin wadannan alamomin.

“Kimanin watanni biyu da suka wuce bayan na dawo daga gona, sai na ji zafi a kafata, sai ta fara kamar borin jiki, sai ta fashe ta bazu har namana ya fara rubewa.

“Ina kashe kimanin Naira 25,000 a mako-mako wajen sayen magunguna, amma idan na sha, sai ya kara tsananta yanayin.

“Yanzu matata tana gida don ta kula da ni da yaran, wanda hakan ya shafi rayuwarmu,” in ji shi.

Adamu, ya kuma roki gwamnati da ta gaggauta kawo dauki kafin cutar ta yadu zuwa ga sauran al’umma.

Da yake tabbatar da lamarin, Hakimin Malabo, Alhaji Aliyu Hammawa, ya ce akalla mutane 30 ne abin ya shafa.

Ya ce a halin yanzu mutane takwas daga ciki suna karbar magani a asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama (MAUTH) a Yola, yayin da wasu kuma ke samun kulawa a cibiyar kula da lafiyar al’umma.

Ya kuma yabawa gwamnatin jihar, bisa gaggauta daukar matakin da yi, tare da yin kira da a gaggauta gudanar da bincike don gano musabbabin cutar.

Shima da yake tabbatar da bullar cutar, Shugaban Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Adamawa, Dakta Suleiman Bashir, ya ce hukumar tare da hadin gwiwar karamar hukuma, ta dauki nauyin mutane 28 da suka kamu da cutar.

Ya tabbatar da cewa mutane takwas ne kawai suka karbi magani.

Dakta ya kara da cewa, gwamnatin jihar ta riga ta biya kudin jinyar wasu a MAUTH, yayin da aka dauki samfuri domin yin gwaji.

“Ana sa ran sakamako a cikin kwanaki 10 masu zuwa. Muna kira ga wadanda abin ya shafa, da su karbi magani maimakon dogaro da magungunan gargajiya,” in ji shi.

Bashir ya bukaci mazauna yankin, da su gaggauta kai rahoton yanayin duk wani rashin lafiya da ba a saba gani ba, zuwa ga cibiyoyin kiwon lafiya don tantancewa da kyau (NAN) IMK/TIM/YMU

Edited by Yakubu Uba

 

Fassarar Aisha Ahmed

‘Yan sanda na bincike kan harin da aka Kaiwa tawagar Malami a Kebbi

Daga Ibrahim Bello

Birnin Kebbi, Satumba 2, 2025 (NAN) Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta fara gudanar da bincike kan harin da aka kaiwa ayarin motocin tsohon ministan shari’a kuma babban lauya Abubakar Malami (SAN), a Birnin Kebbi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa an kaiwa ayarin motocin Malami hari ne a ranar Litinin, a lokacin da suke dawowa daga ziyarar jaje a babban birnin jihar.

Malami ya fice daga jam’iyyar APC ne a ranar 2 ga watan Yuli, sannan ya koma jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Bayan wani taron gaggawa da jami’an tsaro suka yi da jami’an tsaro, kwamishinan ‘yan sanda, Mista Bello Sani, ya tabbatar da cewa ba a kama kowa ba.

“Mun fara bincike kan harin, kuma ba a kama wani mutum ba tukuna, ya kara da cewa Gwamnan Kebbi, ya kira wannan taro ne domin duba abubuwan da suka shafi tsaro,” in ji Sani.

Sani ya kara da cewa, al’amarin ya faru a kewayen yankin GRA da suka shafi ‘yan jam’iyyun siyasa, wadanda ke da alaka da saba ka’idojin yakin neman zabe na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kwamishinan ya bayyana cewa, za a gayyaci shugabannin jam’iyyun siyasa tare da gargadinsu akan sabawa ya ka’idojin zabe.

Ya jaddada cewa za a dauki matakai,  da nufin hana afkuwar tashin hankali yayin da zaben da ke kara kusantowa.

Kwamishinan ya kuma bukaci shugabannin siyasa a Kebbi, da su kwantar da hankalinsu da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar. (NAN) (www.nannews.ng)

IBI/KTO

======

Fassarar Aisha Ahmed

Kungiyar IPMAN za ta dabbaka ingancin man fetur a fanfunan gidajen mai 

IPMAN

Daga Stanley Nwanosike

Enugu, 25 ga Agusta, 2025 (NAN) Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya (IPMAN), ta ce tana shirin dabbaka ingancin famfun mai a gidajen mai, ta hanyar magance magudi da kuma munanan ayyuka.

Shugaban kungiyar IPMAN reshen Jihar Enugu, Cif Chinedu Anyaso, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi a Enugu, jim kadan bayan kammala babban taron kungiyar(AGM), na shekarar 2025.

Sashen Enugu na IPMAN, ya kunshi masu sayar da man fetur masu zaman kansu a jihohin Enugu, Anambra da Ebonyi, da kuma wasu sassan jihohin Abia, Imo, Kogi da Cross River.

Anyaso, ya ce mambobin kungiyar, sun amince gaba daya a taron AGM, kan a tabbatar da ingancin famfunan mai, domin tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun ci moriyar kudadensu.

Ya jaddada cewa, IPMAN ta himmatu wajen daukaka martabarta wajen hidima da ingancin kayayyaki, inda ya kara da cewa: “IPMAN ta kuduri aniyar kafa wata rundunar da za ta tabbatar da bin dukkanin mambobinta.

“Wannan ya zama dole ne domin ingantaccen aikin samar da wutar lantarki.”

A cewarsa, za a kaddamar da kwamitin ne a watan Satumba mai zuwa, kuma za a gudanar da ayyukan ne ta hanyar kwazo a kowace jiha dake karkashin wannan runduna.

“Domin a tsaftace tsarin da kuma tabbatar da cewa an kiyaye martabar kungiyar IPMAN da gidajen man ‘ya’yanmu, mambobin kungiyar a lokacin taron kungiyar, sun amince da cewa dole ne a dakatar da magudi da kuma munanan ayyuka.

“IPMAN za ta kafa wani kwamiti na aiki na yau da kullun nan ba da jimawa ba, yayin da mambobin kungiyar baki daya suka amince da a ci tarar kudi mai yawa, tare da sanya takunkumi ga duk wani gidan mai da ya gaza mallakar kowane memba,” inji shi.

Ya kuma bayyana cewa, kungiyar ta kuduri aniyar yin tsayin daka wajen tunkarar matsalar, ta hanyar ladabtarwar cikin gida; kamar yadda kungiyar ta kawar da gurbataccen man fetur.

Shugaban kungiyar, ya bayyana cewa, kungiyar IPMAN Enugu, ta kuma yaba da irin nasarorin da gwamnoni da gwamnatocin jihohi daban-daban suke yi kan ayyukan raya kasa musamman hanyoyin mota da na tsaro a jihohin yankin.

“Mun samu kwarin guiwa da jajircewar gwamnonin, wajen ci gaba da samar da ingantaccen yanayin kasuwanci da kuma samar da titina na kayayyakin man fetur, don isa ga kowane lungu da sako na sashin,” in ji shi.

Anyaso, ya tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun amince baki daya cewa za su sake rubutawa Gwamna Chukwuma Soludo na Anambra takarda, kan batun IGR na gidajen mai a Anambra.

“Mun yaba masa kan tattaunawar da aka yi zuwa yanzu; duk da haka, muna kira ga duk masu ruwa da tsaki, da su zo kan teburin tattaunawa, don warware sabanin da ke tsakaninsu, su yi sulhu cikin lumana domin amfanar kowa da kowa,” in ji shi.

Shugaban ya ce, mambobin kungiyar sun kuma yanke shawarar sake rubutawa Gwamna Soludo takarda kan bashin sama da Naira miliyan 900 da ake bin mambobin kungiyar IPMAN da suka samar da dizal don gudanar da fitilun tituna a jihar.

“Gwamnatin Jihar Anambra ta ci basuka tun shekara daya da ta wuce, duk da wasiku da kiraye-kirayen kai-tsaye har sau uku ga Gwamna da Jami’an Jihar da abin ya shafa, har ya zuwa yanzu ba a yi komai ba.

“Muna bin hanyar diflomasiyya tunda ba ma son mu umurci mambobinmu da su shiga yajin aiki ko kuma su daina sayar da albarkatun man fetur, domin hakan zai kara sanya talakawa a wahala da kuncin rayuwa.

“Idan ‘yan kungiyar IPMAN suka tafi yajin aiki, a bayyane yake cewa litar man fetur na iya haura kusan N2,000 zuwa N3,000 a jihar, baya ga sauran illolin da wannan yunkuri zai haifar.

“Duk da haka, muna son gwamnatin jihar ta saurari kokenmu da kuma halin da ‘yan kungiyarta IPMAN ke ciki, wadanda suka samar da kayayyaki kuma a halin yanzu suna bin cibiyoyin kudi.”

Anyaso ya jaddada cewa, a cikin ‘yan watanni ‘yan kungiyar IPMAN din guda takwas a Anambra, wadanda suke bin gwamnatin jihar bashi sun mutu sakamakon damuwa da kaduwa, domin matsin lamba da hukumomin kudi ke yi, na neman a biya su lamuni mai tsanani.

“Wasu daga cikin cibiyoyin hada-hadar kudi sun karbe tashoshinsu, wasu kuma tuni aka rufe wasu da dama kuma sun kori ma’aikatansu saboda gazawar kudi,” inji shi.

Shugaban ya kara da cewa, mambobin sun kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi walwala, ingantattun hanyoyin da za a bi wajen daga man fetur da yadda za a yi shirin sayar da kayayyaki.

Kamar yadda ya fada, yace za a fito da shiri don isar da kayayyakin Dangote kai tsaye da kuma shirin samar da man fetur da iskar Gas na JEZCO don taimakawa mambobin.

A taron, an gabatar da jawabai daga hukumar harajin cikin gida ta tarayya, kan shigar da harajin lantarki, da kuma ta TradeGrid Limited kan yadda za a saukaka ayyukan sanya wutar lantarki mai amfani da hasken rana a gidajen mai, da dai sauran batutuwa. (NAN) ( www.nannews.ng )

 

KSN/KO

Fassarar Aisha Ahmed

‘Yan majalisa sun koka kan rashin tsaro a Nasarawa

Tsaro

By Awayi Kuje

Lafia, Aug. 22, 2025 (NAN) Majalisar Dokokin jihar Nasarawa, ta ja hankulan jama’a game da karuwar matsalar rashin tsaro a jihar, musamman masu garkuwa da mutane.

Dokta Danladi Jatau, kakakin majalisar ne ya bayyana hakan a bayan da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Lafia ta tsakiya, Mista Solomon Akwashiki, ya tabo batun.

Akwashiki, ya tabo batun da ya shafi bukatun jama’a a domin jaddada zaman majalisar a Lafiya.

Shugaban majalisar ya yi kira ga hukumomin tsaro a jihar, da su yi amfani da dokar yaki da garkuwa da mutane da majalisar ta kafa domin dakile satar mutane a jihar.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda ake hada baki da masu satar mutane a yi garkuwa da mutane, yana mai nuna damuwa cewa jihar na zama cibiyar garkuwa da mutane.

“Kudirinmu na haka ne, muna kira ga gwamnan jihar, da ya umarci jami’an tsaro su kara karfafa tsaro a fadin jihar.

“Na biyu, muna umurtar jami’an tsaro da su yi amfani da dokar da wannan majalisa ta kafa, wajen dakile garkuwa da mutane.

“Na uku, muna kira ga mazauna yankin da su kai rahoton duk wani motsi da ayyukan daidaikun mutane ga jami’an tsaro, don daukar mataki,” in ji kakakin.

Tun da farko, Mista Akwashiki, mamba mai wakiltar mazabar Lafia ta tsakiya, ya nuna damuwa akan cewa Lafia, babban birnin jihar Nasarawa ba shi da mafaka, sakamakon ci gaba da yin garkuwa da mutane.

“Mai girma shugaban majalisar, idan Lafia ba ta da lafiya ina kuma za a samu lafiya?

“Wadannan masu garkuwa da mutane suna ta kai hare-hare, suna barna ba tare da wata tangarda ba, dole ne mu tashi kafin lokaci ya kure,” in ji Akwashiki.

Shima da yake bayar da gudunmawarsa, Daniel Ogazi (APC-Kokona Gabas) ya tunatar da majalisar cewa majalisar dokokin jihar ta zartar da dokar yaki da garkuwa da mutane.

“Dokar da wannan majalisa ta kafa ta tanadi cewa idan aka kama mai garkuwa da mutane, a kawar da shi ko ita, wannan yana aiki, amma ba mu san abin da ya faru daga baya ba,” in ji Ogazi.

Da suke bayar da gudunmawa, shugaban masu rinjaye na majalisar, Mista Suleiman Azara, Mista Esson Mairiga (PDP-Lafia North) da kuma Mista Mohammed Omadefu (APC-Keana), sun bukaci hukumomin tsaro da su canza salon dakile satar mutane. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AKW/BEKl/COF

Fassarar Aisha Ahmed