UNFPA ta bayar da tallafin kayan kula da mata masu yoyon fitsari ta Sokoto
UNFPA ta bayar da tallafin kayan kula da mata masu yoyon fitsari ta Sokoto
Gudunmawa
Daga Habibu Harisu
Sokoto, 4 ga Agusta, 2026 (NAN) Hukumar kula da yawan Jama’a ta Majalisar Dinkin Duniya (UNFPA) ta bayar da kayan aikin likita don tallafawa kula da marasa lafiya masu fama da ciwon yoyon fitsari (VVF) a Asibitin Mata da Yara na Maryam Abacha, Sokoto.
Kamfanin Dillancin Labarai ta Najeriya (NAN) ya tuwaito cewa an mika kayan aikin ne ta hannun Shugaban Tawagar Jihar UNFPA, Dakta Rabi’atu Sageer, ga Kwamishinan Lafiya na Jihar, Dakta Faruk Abubakar-Wurno, a wani bikin da aka gudanar ranar Talata a Sokoto.
Yayin da ya karɓi kayan aikin, Abubakar-Wurno ya bayyana wannan taimako a matsayin wani muhimmin mataki a kokarin jihar na karfafa ayyukan kula da lafiya na iyaye mata da na haihuwa.
Ta hanyar Wakilin Daraktan Ayyukan Jinya, Abubakar Shehu, Kwamishinan ya ce gudummawar zata kara karfin asibitin wajen bayar da ingantaccen aikin lafiya da kuma kulawa ga mata masu fama da yoyon fitsari wanda a ka fi samu daga haihuwa.
Wannan kayan aiki zai karfafa kiwon lafiya na mata da na haihuwa kuma zai tabbatar cewa mata da suka kamu da yoyon fitsari da mata masu haihuwa suna samun kulawa mai inganci, da daraja,” in ji shi.
Kwamishinan ya nuna godiya ga UNFPA saboda ci gaba da haɗin gwiwarsu da gwamnatinsa wajen inganta isar da kiwon lafiya, sannan ya yi kira ga shugabannin asibitin da su tabbatar da amfani da kayan aikin yadda ya kamata da kuma kula da shi.
“Ina matukar godiya da UNFPA saboda haɗin gwiwa da tallafin da bai misaltawa wajen inganta kiwon lafiya a Jihar Sokoto. Ina kira ga shugabancin asibitin da su yi amfani da wannan kayan aikin yadda ya dace kuma su tabbatar da kula da shi domin amfanin al’ummarmu,” in ji shi.
A jawabin ta, Shugabar Ƙungiyar UNFPA ta Jihar, Sageer, ta ce babban burin ƙungiyar shine kawar da yoyon fitsari a Jihar Sokoto da ƙasa baki ɗaya ta hanyar rigakafi, yayin da ake tabbatar da ingantaccen magani ga waɗanda suka rigaya da samun matsala.
“Babban burinmu a UNFPA ba wai ci gaba da samar da kayan aikin tiyata ba ne.
“Babban burinmu shine mu samu babu ciwon fistula na haihuwa a Jihar Sokoto,” in ji ta.
Sageer ta bayyana ciwon yoyon fitsari a matsayin wata matsala mai muni amma mai iya kaucewa wadda ke nuna rashin daidaito na zamantakewa da ke shafar mata da ‘yan mata.
“Ciwon yoyon fitsari na da muni, amma kuma ana iya kauce masa. Yana tunatar da rashin daidaito da ke cikin al’umma.
“Yana nuna rashin karfin ikon kai, karancin ilimi da raguwa wajen samun kudi ga mata da yawa,” in ji ta.
Sageer ta jaddada cewa UNFPA na kallon ciwon yoyon fitsari ba kawai a matsayin ƙalubale na lafiya ba amma har ma da batun zamantakewa da ci gaba.
“Haka nan yana da nasaba da mata da aka bari a baya, kuma ba za mu iya cimma manufofin ci gaba mai dorewa ba idan muka bari wani a baya,” ta kara da cewa.
Sageer ta lura cewa UNFPA ta tallafawa Cibiyar VVF a asibitin a tsawon shekaru ta hanyar kudade daga abokan hadin gwiwa na ci gaba, ciki har da Tarayyar Turai ta hanyar Ayyukan Lafiya da Gwamnatin Canada, da wasu.
Ta bukaci asibitin da ya tabbatar da kulawa da kayan aikin.
Haka kuma a lokacin da yake magana, Sakataran Dindindin na Ma’aikatar Kasafin Kudi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki ta Jihar Sokoto, Alhaji Buhari Umar,
ya tabbatar da kudurin gwamnatin jihar na yin aiki tare da abokan ci gaba don inganta bayar da kiwon lafiya.
Umar ya ce shugabancin Gwamna Ahmed Aliyu ya mayar da hankali ne wajen gina haɗin kai da daidaita shirin ci gaba da abubuwan da suka fi muhimmanci ga jihar bisa tsarin manufofi guda tara.
“Manufar wannan shugabanci ita ce tabbatar da an kafa haɗin kai da daidaituwa.”
“Muna godiya ga UNFPA saboda daidaita ayyukansa da bukatun jihar Sokoto, kuma muna sa ran ingantaccen haɗin gwiwa tare da sauran abokan ci gaba,” in ji shi.
Sakataran dindindin, wanda ya ce ya burge shi matuƙa ganin ci gaban da asibitin ya samu a lokacin ziyararsa ta baya-bayan nan, ya ƙalubalanci shugabannin su maida sabbin kayan aiki zuwa sakamako mai kyau ga kiwon lafiya.
“Farashin yin kyakkyawan aiki shine yin mai kyau. Abu ɗaya ne yin biki; wani abu ne daban samun sakamako.
Umar ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da goyon bayan shirye-shiryen da ke inganta ayyukan kiwon lafiya da
kawo sakamako mai kyau ga jama’ar Jihar Sokoto. (NAN)(www.nannews.ng)
HMH/AOS
=========
Bayo Sekoni ne ya gyara

