Wani ɗan kasuwa ya bukaci kotu ta bashi hakkin kula da ɗansa mai shekara biyar
Wani ɗan kasuwa ya bukaci kotu ta bashi hakkin kula da ɗansa mai shekara biyar
Kula
Daga Christiana Nicholas
Mararaba (Jihar Nasarawa), 6 ga Agusta, 2026 (NAN) Wani ɗan kasuwa, Shafiu Daiyabu, ya nemi Kotun Ƙasa wadda ke zaune a Mararaba Gurku, Jihar Nasarawa, ta ba shi hakkin kula da ɗansa mai shekara biyar.
Daiyabu, wanda ke zaune a Mararaba Gurku, Ƙaramar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa, ya gabatar da wannan buƙata a cikin wata ƙara da ya shigar da tsohuwar matarsa, Zainab Sulaiman, wata ‘yar kasuwa daga Yan Bola, Nyanya, FCT Abuja.
Ya shaida wa kotu cewa shi da wanda ake kara sun kasance maji da mata a baya, inda suka samu ɗa, Sulaiman Shafiu, a lokacin aurensu.
Ya ƙara da cewa wanda ake kara ta tafi da ɗan a, wanda ke da shekaru biyar kacal, ba tare da amincewarsa ba.
Har ila yau, ya shaida wa kotu cewa wanda ake kara tana da “mummunar dabi’u” kuma ɗan zai lalace a hannunta.
A cewarsa, ɗan ba ya zuwa kowace makaranta a halin yanzu, inda ya nuna cewa yana son sanya ɗansa a makarantar boko da ta Islamiyya.
Saboda haka, ya roƙi kotu ta ba shi kulawar ɗan.
Alkali Mohammed Shomo sai ya daga shari’ar har zuwa 17 ga Satumba don cigaba da sauraron ta.(NAN)(www.nannews.ng)
CN/HA
=======
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta gyara

