Gidauniyar Sultan Foundation ta bayar da tallafin magungunan da kudinsu ya kai N1.7bn ga Sokoto, Kebbi



Najeriya za ta iya cin gajiyar dala Amruka biliyan 100 a kasuwannin magani a duniya – cewar Masaniya
Magani
Daga Alaba Olusola Oke
Ondo (Jihar Ondo), 30 ga Agusta, 2024 (NAN) Wata Ma’aikaciyar harhada magunguna, Misis Zainab Shariff, ta ce Najeriya za ta iya cin gajiyar dalar Amruka biliyan 100 a kasuwannin magani ta duniya.
Ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar maganin gargajiya na Afirka, wanda Cibiyar Nazarin Magungunan Gargajiya da Bincike ta Jami’ar Kimiyyar Lafiya (UNIMED) Ondo ta shirya a ranar Alhamis.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron mai suna “Hadawa da Inganta Magungunan Gargajiya na asali don Saukake Kiwon Lafiyar ” wanda a ka shirya a garin Ondo.
Shariff, wadda wata kwararriyar mai fafutuka ce na inganta Magungunan Gargajiya da na Asali (TCAM) Najeriya ce ta bayyana haka.
Masaniyar ta ce yin amfani da kasuwannin duniya don samar da irin magungunan zai samar da kusan dala tiriliyan biyar nan da shekarar 2050 a duniya.
A cikin makalarta ta mai taken “Haɓaka da Ci gaban Tsirrai na Magani don Samar da Kiwon Lafiya a Duniya” ta jaddada buƙatar ƙara darajar magungunan da ake da su a ƙasar nan don fitar da su zuwa kasashen waje.
Gaskiyar halin da ake ciki yanzu, a cewarta, ba a nuna kasar Najeriya wajen fitar da tsire-tsire masu magani zuwa kasashen waje ba, duk da dimbin albarkatun da take da su.
Sai dai ta kara da cewa har yanzu akwai fata ga kasar idan har al’ummar kasar za su iya tantance filayen noman tsire-tsire na magani don kara darajarsu.
Masaniyar harhada magungunan ta ce kasar za ta iya samar da magungunan ganye da ire-iren su da za su shiga jerin amicewar hukumar ta NAFDAC zuwa kantuna daban-daban don tallafawa ci gaba da bincike.
Ta ba da shawarar cewa ya kamata kasar ta fadada hadin gwiwarta da masu ruwa da tsaki tare da aiwatar da shirye-shiryen digiri a fannin likitancin tsire-tsire.
A nasa jawabin, mataimakin shugaban Jami’ar UNIMED ta Ondo, Farfesa Adesegun Fatusi, ya ce tuni cibiyar ta dauki nauyin gudanar da karatun digiri na uku a fannin likitancin tsire-tsire.
Ya ce “a wani bangare na habakar huldar, cibiyar ta bayyana fa’idar magungunan ganye da tsire-tsire, ta kuma kafa Sashen fannin Magungunan da za su fara digiri na farko a shirin a watan Oktoba 2024.”
A nasa bangaren, Dokta Oghale Ovuakporie-Uvo, Darektan riko na cibiyar kula da magungunan tsire-tsire da ganye tare da gano magunguna, ya nanata kudurin cibiyar na gano magungunan ganye da tsire tsire domin saukaka harkokin kiwon lafiya a duniya.
Ovuakporie-Uvo ya ce fahimtar shirin shine tushe da kuma amfani da hankali na magungunan gargajiya na asali, musamman al’adun gargajiya da na lafiya dangane da amfani da tsire-tsire da ganye wanda ke da mahimmanci samar da cikakkiyar lafiya a yanayin mutanen Afirka. (NAN) (www.nannews.ng)
OKEO/HA
=======
Hadiza Mohammed-Aliyu ta gyara
Ziyara
Daga Salif Atojoko
Abuja, Agusta 29, 2024 (NAN) Shugaban Kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa Beijing, Kasar Sin, a ranar Alhamis don ziyarar aikin gwamnati da ta shafi Kasa da Kasa.
Jami’in yada labarai na fadar Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale, ya bayyana cewa Tinubu zai yi aiki na ɗan lokaci a Kasar Gamayyar Larabawa (United Arab Emirates) .
Ya kara da cewa “a kasar Sin, Shugaban kasar zai gana da Shugaba Xi Jinping na Kasar Sin kuma ya yi ganawa da shugabannin kasuwancin kasar Sin a kan batun taron hadin kai tsakanin Kasar Sin da yankin Afirka.
“A cikin tawagar akwai jami’an gwamnatin tarayya tare da wasu muhimman mutane da su ka marawa Shugaba Tinubu baya a tafiyar.” (NAN)(www.nannews.ng)
SA/BRM
=======
Bashir Rabe Mani ne ya buga
Sojoji
Sumaila Ogbaje
Abuja, Aug. 29, 2024 (NAN) Babbar rundunar tsaron aikin sojoji ta kasa ta ce sojoji sun yi nasarar kawar da ‘yan ta’adda 1,166, tare da cafke mutane 1,096 da ake zargi da aikata laifukfuka a cikin kwanaki 29 a fadin kasar nan.
Shugaban yada labarai na hukumar, Manjo Janar. Edward Buba, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar a ranar Alhamis a Abuja.
Buba ya ce sojojin sun kuma ceto mutane 721 da aka yi garkuwa da su.
Ya ce sojojin sun kuma kwato makamai 391, alburusai 15,234 da suka hada da bindigogi kirar AK47 guda 208, bindigogi kirar gida guda 54, bindigogin toka guda 53, bindigogi masu feshi 36, da kuma alburusai 10,452 ma tsawon mita 7.62 na musamman a cikin watan.
Sauran makaman a cewarsa, sun kunshi harsashi 1,991 na NATO masu tsawon mita 7.62, harsashi 293, makamai iri-iri 42 da harsasai iri daban daban su ka Kai guda 2,498.
Ya ce an kashe wasu shugabannin ‘yan ta’adda da kwamandoji a lokutan artabun sakamakon farmakin da sojoji suka kai musu a cikin watan.
A cewarsa, wadanda a ka kashe a Arewa maso gabas sun hada da: Munir Arika, Sani Dilla ( da a ka fi sani da Dan Hausawan Jibilarram), Amir Modu, Dan Fulani Fari Fari, Bakoura Araina Chikin, Dungusu, Abu Darda da Abu Rijab.
“Wadanda ke yankin Arewa maso Yamma sun hada da; Kachalla Dan Ali Garin Fadama, Kachalla Dan Mani Na Inna, Kachalla Basiru Zakariyya, Sani Baka Tsine, Inusa Zangon Kuzi, Ibrahim, Tukur da Kamilu Buzaru, da sauransu.
“Ayyukan da ake ci gaba da gudanarwa a duk fadin kasar sun yi matukar rage karfin kungiyoyin ta’addanci tare da hana ‘yan ta’adda damar kai gaggarumin farmaki.
“Halin da a ka fuskanta galibi a kwanakin nan shi ne fadace-fadace da kai hare-hare kan wurare masu sauki.
“Muna sane da cewa muna tunkarar abokan gaba masu wayo, marasa tausayi da muguwar dabi’a wadanda dole ne a dakatar da su daga ayyukansu na ta’addanci.
“Saboda haka, sojoji a shirye suke su yi aiki da daukar matakin da ya dace da za a yi don wargaza wadannan kungiyoyin ta’addanci.
“Dabarun sojoji shi ne su lalata karfin wadannan kungiyoyin ta’addanci da samar da yanayin da ba za su iya aiwatar da ayyukan ta’addanci ko cutar da mutanen kasa ba.
“Saboda haka, sojoji sun ba da fifiko wajen kai hari ga shugabannin ‘yan ta’adda, kwamandoji, sojojin kafa da kuma abokan aikinsu,” in ji shi.
A yankin Arewa maso gabas, Buba ya ce dakarun Operation Hadin Kai, sun kashe ‘yan ta’adda 292, sun kama mutane 254 da ake zargi da kuma ceto mutane 213 da aka yi garkuwa da su a cikin watan.
Ya kara da cewa wani adadin mayakan na Boko Haram/ISWAP 2,742 da iyalansu, sun mika wuya ga sojoji tare da kwato manyan makamai da alburusai.
A yankin Arewa ta tsakiya, Buba ya ce dakarun Operation Safe Haven sun kashe ‘yan ta’adda 50, sun kama 290 tare da kubutar da masu garkuwa da mutane 121 tare da kwato tarin makamai.
A karkashin Operation Whirl Stroke, ya ce sojojin sun kashe ‘yan ta’adda 37, sun kama mutane 94 da a ke zargi, tare da kubutar da mutane 68 da a ka yi garkuwa da su.
A yankin Arewa maso Yamma, kakakin rundunar tsaron ya ce dakarun Operation Hadarin Daji sun kashe ‘yan ta’adda 153, sun kama mutane 97 da a ke zargi da kuma kubutar da masu garkuwa da mutane 186 tare da kwato tarin makamai.
A karkashin Operation Whirl Punch, ya ce sojojin sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda 63, sun kuma kama mutane 291 da a ke zargi da kuma kubutar da masu garkuwa da mutane 62, tare da kwato tarin makamai da alburusai.
A yankin Kudu-maso-Kudu, Buba ya ce dakarun Operation Delta Safe, sun kara yawan danyen man da kasa ke hakowa a kullum zuwa sama da ganga miliyan daya da rabi a kowace rana a cikin watan Agusta.
Ya ce sojojin sun kama mutane 71 da ke satar danyen mai tare da kama lita 5,047,150 na danyen mai, lita 1,152,500 na nau’in man naurori, lita 320 na nau’in man manyan injuna da kuma lita 28,500 na man kananun abubuwan sufuri.
“Bugu da kari, sojojin sun kwato alburusai iri-iri 194 tare da lalata kwale-kwalen katako 125 da kuma wuraren tace haramtattun wurare 458.
“Duk da haka, sojoji suna yin kira da a kara nuna gaskiya da ba su ingantattun shawarwari na gwarin guiwa daga masu ruwa da tsaki a fannin tsaro da kuma hadin kai daga al’ummomin yankin.
“Sojoji kuma suna sa ido kan yadda ake hukunta masu laifin satar danyen mai,” in ji shi.
A yankin Kudu maso Gabas, Buba ya ce dakarun Operation UDO KA sun kai farmaki kan kungiyar ta’addanci ta IPOB/ESN tare da kashe ‘yan ta’adda 34, sun kama mutane 82 da a ke zargi da kuma kubutar da masu garkuwa da mutane 26. (NAN) ( www.nannews.ng )
OYS/SH
======
edita Sadiya Hamza
Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 8 a Kaduna
‘Yan fashi
Daga Mohammed Tijjani
Kaduna, Agusta 29, 2024(NAN) Gwamnatin jihar Kaduna (KDSG), ta ce dakarunta sun kashe ‘yan bindiga takwas a karamar hukumar Birnin Gwari (LGA), ta jihar.
Kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Kaduna.
Aruwan ya ce bisa ga bayanan da rundunar ta bayar, sojojin sun fara sintiri a yankin Kampanin Doka inda suka tuntubi wasu ‘yan bindiga da suka isa wurin.
Ya ce ba tare da bata lokaci ba sojojin sun yi artabu tare da kashe bakwai daga cikin ‘yan fashin.
“Akan tsaro da bincike a yankin, sojojin sun kwato, bindigogi kirar AK-47 guda uku, mujallu takwas, hudu babu kowa, hudu dauke da jumullar harsashi 120 na alburusai 7.62mm da kuma mai daukar mujallu.” Inji shi.
Aruwan ya ce sauran kayayyakin da aka kwato sun hada da babura shida, wayoyin hannu guda uku, gidan rediyon Baofeng guda biyu da kuma tufafin farar hula guda biyu.
A cewarsa yayin kammala aikin sintiri, an ci gaba da tuntubar juna da ‘yan bindiga a kusa da babban yankin Gayam.
” Sojojin sun kashe daya yayin da ake zargin wasu sun tsere da raunukan harbin bindiga. ” in ji shi.
Aruwan ya ce Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya godewa jami’an tsaro da suka amsa.
A cewarsa, gwamnan ya kuma yabawa sojojin, a karkashin jagorancin babban kwamandan rundunar soji ta 1 Division Nigerian Army/Commander Operation Whirl Punch (OPWP), Maj-Gen. Mayirenso Saraso, saboda jajircewarsu da kuma gagarumin ci gaba.
“An yi kira ga jama’a da su kai rahoton mutanen da ake zargin suna neman maganin raunukan harbin bindiga zuwa dakin aikin tsaro ta layukan waya 09034000060 da 08170189999.
“Za a ci gaba da yakin sintiri a yankin gaba daya da sauran wuraren da ake sha’awar,” inji Aruwan.(NAN)(www.nannews.ng)
TJ/CHOM/BHB
=========
Chioma Ugboma/Buhari Bolaji ne suka gyara shi
Cunkoso: Masu ruwa da tsaki sun bukaci alkalai su yi la’akari da zabin hukunci
Cunkoso
Daga Habibu Harisu
Sokoto, Agusta 29, 2024 (NAN) Kungiyar masu ruwa da tsaki kan gyara harkokin shari’a a jihar Sokoto sun bukaci alkalai da su yi la’akari da wasu zabuka na hukunta wadanda aka yankewa hukunci ba dauri ba a kowane lokaci.
Kiran na daga cikin kudurorin da Mr Rabi’u Gandi, wakilin kungiyoyin farar hula ya karanta a karshen taron masu ruwa da tsaki a ranar Laraba a Sokoto.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron mai taken “Fahimtar Dabarun Tsaretsaren Tsaro na Kasa, Samar da Ingantaccen Yanayi ga Ma’aikatan gwamnati da wadanda ba na Gwamnati ba”, wata kungiya ce mai zaman kanta ta CLEEN Foundation ce ta shirya tare da tallafi daga gidauniyar MacArthur.
Ya ce bisa la’akari da shawarwarin da masu ruwa da tsaki suka bayar, akwai bukatar alkalai a kowane mataki su rika amfani da zabukan yanke hukunci kamar ayyukan al’umma da sauran hukunce-hukunce, ba zaman gidan yari ba a kodayaushe.
Ya bayyana cewa mafi yawan kashi na hukunce-hukuncen dauri sun sanya wuraren gyaran Hali cikin cunkoso, yana mai jaddada cewa yin amfani da zabin zai rage cunkoso.
Gandi ya kuma shawarci bangaren shari’a da ‘yan majalisar dokokin kasar da su saukaka tsarin sahhalewa masu laifi da sharadin kimtsuwa a mulkin kasar domin inganta tsarin.
Ya kuma kara jaddada mahimmancin tsarin sahhalewa fursunonin a Najeriya, wanda zai rage matsin lamba ga wuraren da ake tsare da su, da yawan barkewar gidan yari da korafe-korafe a tsakanin fursunonin.
A cewarsa, wakilan hukumomin tabbatar da doka a wurin taron sun ba da bayanai da shawarwari daban-daban kan mafi kyawun hanyoyin inganta ayyukansu da kuma kalubalen da suke fuskanta a kasar.
Yayin da ya yabawa gidauniyar CLEEN bisa wannan kokarin, Gandi ya ce za a tattara bayanan tare da mikawa hukumomi na gaba domin tantancewa da aiwatar da su.
Da yake jawabi, jami’in shirin na gidauniyar, Mista Ebere Mbaegbu, ya ce taron tattaunawar wani bangare ne na hadakar ‘yan kasa da masu ruwa da tsaki na gwamnati da wadanda ba na gwamnati ba a kan sauye-sauyen aikin ‘yan sanda da shari’a, gudanar da hukunce hukuncen laifuka da shari’a ta tanadar, gaskiya da rikon amana.
Mbaegbu ya bukaci aiwatar da tsarin sahhalewa fursunoni a matsayin mabudin rage cunkoso a gidajen yari da dabarun gyara masu laifi.
Ya jaddada cewa gudanar da adalci shi ne ginshikin duk wata al’umma da ta tabbatar da bin doka da oda.
Ya kara da cewa kokarin hadin gwiwa na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da cewa wannan ginshikin ya kasance mai karfi da inganci.
“ Sahhalewa fursunoni wani muhimmin bangare ne na tsarin shari’ar mu, da nufin gyara masu laifi da kuma mayar da su cikin al’umma a matsayin ‘yan kasa masu bin doka da oda.
“Yana nuna ma’auni tsakanin matakan ladabtarwa da kuma buƙatar gyarawa, sanin cewa yuwuwar yin gyare-gyare da canji mai kyau yana samuwa a cikin kowane rayuwar bil’adama,” in ji shi.
Wani bangare na mahalarta taron sun nuna godiya ga wadanda suka shirya taron, inda suka ce taron ya samar musu da wani dandali mai kima da za su iya shiga tattaunawa mai mahimmanci.
Mahalarta taron sun bayyana ra’ayoyinsu tare da tantance halin da tsarin shari’a ke ciki game da sahhalewa fursunoni da kuma babban tasirinsa kan gudanar da shari’ar laifuka a Najeriya.
NAN ta ruwaito cewa mahalarta taron sun hada da kungiyoyin fararen hula, ‘yan sanda, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Hukumar Kula da Gyaran Hali ta Kasa (NCoS), Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), masu gabatar da kara da lauyoyi, da dai sauransu.(NAN) ( www.nannews .ng )
HMH/BRM
=========
Tace wa: Bashir Rabe Mani
Hajji
Daga Salisu Sani-Idris
Abuja, Augusta 28, 2024 (NAN) Hon. Femi Gbajabiamila, Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, ya jaddada bukatar yin garambawul a cikin hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) domin dakile almundahana da kudade, sakaci da kuma musgunawa maniyyata.
Gbajabiamila ya yi wannan kiran ne a ranar Larabar da ta gabata yayin wata ziyarar gani da ido da ya kai hedikwatar kula da aikin Hanji ta kasa wato NAHCON da ke Abuja.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa ziyarar na daga cikin kokarin tattaunawa da hukumomin gwamnati a karkashin kulawar fadar gwamnati.
Ya ce bai kamata hukumar NAHCON ta shiga cikin wata rigima ba saboda muhimmacin aikinta da abin da take wakilta.
“Hukumar addini ce. Kwamiti ne da aka kafa don cika wajibai na addini da na ruhi ga maza da mata masu imani.
“Alhazai na tafiya kowace shekara domin sauke wani farilla na Musulunci. Ba wannan kadai ba, idan suna can, suna nan a matsayin jakadun Najeriya.
“A matsayinsu na jakadun Najeriya, ana sa ran za su dabbaka kishin kasarsu Najeriya, domin su wakilce mutanensu tare da nuna hali da dabi’a nagari.
“Mun yi nadamar yadda galibi ana cin zarafin alhazai saboda rashin tsari da NAHCON ke yi a lokacin aikin hajji,” in ji shi.
A cewarsa, a wasu lokutan alhazai ba sa gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba, don haka dole ne hukumar ta dauki nauyin gudanar da aikin hajjin cikin inganci a Najeriya da Saudiyya.
Ya kuma bukaci mahukunta da ma’aikatan hukumar da su hada kai da ofishin mataimakin shugaban kasa mai kula da hukumar domin gano kura-kuran da aka yi a baya, da yin gyara da kuma tabbatar da gudanar da ayyukan alhazai ba tare da wata matsala ba.
“Abin da ya faru ya faru, kuma muna nan don tsara hanyar da za a bi.
“Lokaci ya yi da za a sake fasalin tsarin hukumar ta yadda zai dace da ajandar sabunta salon muradai na Shugaba Bola Tinubu,” in ji shi.
Har ila yau, Sen. Ibrahim Hadejia, mataimakin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, ya yi na’am da matsayin shugaban ma’aikatan, inda ya jaddada bukatar yin shiri da wuri domin aikin Hajji.
“Hajji babban aiki ne da ke bukatar tsari da kayan aiki. Na shiga cikin aikin 2024, kuma ɗayan mahimman darussan da aka koya shine buƙatar shiri da wuri.
“Najeriya ce tafi kowacce kasa yawan alhazai daga Afirka, kuma muna da kasashen da adadinsu bai kai adadin mahajjata daga wata jiha a Najeriya ba.
“Hukumar Hajji tana kuma bukatar ta kara fito da gaskiya wajen sanar da mahajjata abin da suke biya,” in ji Hadeija.
Da yake mayar da martani, Prince Aliu Abdulrazak, Kwamishinan Zartarwa na Hukumar Kula da Ma’aikata da Kudi ta NAHCON, ya yi kira da a yi garambawul ga tsarin lissafin hukumar.
Ya kuma yi kira da a inganta wakilcin tarayya a cikin kungiyar.
“An kwatanta hukumar a matsayin ta kasa baki daya, amma tsarin wakilcin tarayya bai cika kammaluwa ba.
Abdulrazak ya ce “Idan ka shiga cikin jerin sunayen, wani yanki ne ya mamaye shi.”
Hakazalika, shugaban ma’aikatan ya ziyarci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) inda ya jaddada bukatar sauya yadda ake tafiyar da aikin Jin Kai daga ib’til’i daga halin da ake ciki zuwa matakin da ya dace.
Ya kuma jaddada mahimmancin Shirin ko ta kwana kan rage kai Bata taimako bayan ib’til’i ya bayyana cewa za a iya kaucewa aukuwar bala’o’i da dama a kasar tare da kyakkyawan shiri da gargadin wuri.
“Hukumar NEMA tana da abubuwa biyu ne: rigakafin ib’til’i da rage bala’ai.
“Amma da alama mun fi mai da hankali kan ragewa tare da barin wani bangare na umarnin, wanda shi ne rigakafin.
“Dole ne mu kara duba fannin rigakafin saboda yawancin wadannan bala’o’i ana iya hana su,” in ji shi. (NAN) (www.nannews.ng)
SSI/SA
================femi gbajabiamila
Salif Atojoko ne ya gyara
Shugaba Tinubu ya raba tallafin taki da shinkafa ga marasa galihu a Gombe
Kyauta
Daga Hajara Leman
Gombe, Agusta 29, 2024 (NAN) Shugaban kasa Bola Tinubu, a ranar Laraba ya bayar da gudummawar tireloli guda biyu kowannen cike da shinkafa da taki ga marasa galihu a jihar Gombe.
Alhaji Saidu Alkali, Ministan Sufuri ne ya raba kayan a madadin Shugaba Tinubu.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN, ya ruwaito cewa motocin taki da shinkafa kowanne yana dauke da buhu 1,200.
Da yake jawabi a wajen taron, Alkali ya ce shugaban kasar ya yi hakan ne da nufin rage wahalhalun da masu karamin karfi ke fuskanta.
A cewar ministan, wannan karimcin wata shaida ce ta alherin da Tinubu ke nunawa al’ummar Gombe, da ya ke rike da zuciyarsa.
Da yake karbar kayayyakin a madadin gwamnatin jihar Gombe, wani dattijo kuma jigo a jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a Gombe, Alhaji Abba Sadiq, ya nuna jin dadinsa ga shugaban kasa kan wannan karimcin.
Sadiq ya kara da cewa hakan zai taimaka matuka wajen bayar da gudunmawar bunkasa noma a jihar, da kuma tabbatar da samun isasshen abinci ga mutanen Gombe.
Ya kuma bai wa gwamnatin tarayya tabbacin cewa kayayyakin za su kai ga wadanda za su amfana. (NAN) (www.nannews.ng)
HUL/DOR
========
Nyisom Fiyigon Dore ta gyara
Muna neman taimakon gwamnati – Masu ciwon sugar
Taimako
Daga Christian Njoku
Calabar, Aug. 29, 2024 (NAN) Wata kungiya mai suna — National Association of Persons Living with Diabetes – tayi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa masu cutar sugar saboda kudin abinci da magani sun hau.
Kungiyar tayi kiranne a wata hira da Mr Bernard Enyia, mai kula da harkar kungiyar yayi da kamfanin dillancin labarai na Nigeria (NAN) ranar alhamis a Calabar.
Enyia yace da yawa daga cikin masu fama da cutar sun rasa wayukansu saboda rashin kudin sayan magani da wadataccen abinci.
Ya kara da cewa dayawa a cikin masu fama da ciwon sun koma ga maganin gargajiya saboda bazasu iya sayan maganin asibiti ba.
Yace yawancin maganin ciwon sugar sai an kawosu ne daga kasashen ketare, shi yasa suke tsada, sai ya bukaci gwamnati da ta tallafa wa al’umma.
Enyia ya kara da cewa kudin alluran insulin da masu cutan suke amfani dashi wanda yake yi musu sati daya kacal, ya haura zuwa N19,000 ko N24,000 daga N4000 da suke saye a 2022.
Mai kula da al’amuran kungiyan yace har farashin alluran syringe da masu cutar suke amfani dashi ya hau daga N50 zuwa N600, kuma ana bukatar ayi anfani da guda biyu a kowane rana.
Yace masu cutar sugar suna cikin mawuyacin hali, sai ya nemi taimakon gwamnati da sauran al’umma wajen tabbatar da sun samu magani cikin sauki.(NAN)(www.nannews.ng)
CBN/HA
========
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta tace