Shafin Labarai

Nnamdi Kanu ya kori kungiyar lauyoyi masu kare shi, ya kalubalanci hurumin kotu

 

By Taiye Agbaje

Abuja, Oktoba 23, 2025 (NAN) Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), a ranar Alhamis, ya bayyana korar tawagar lauyoyinsa, karkashin jagorancin Cif Kanu Again, SAN, a babbar kotun tarayya dake Abuja.

Kanu, ya shaida wa mai shari’a James Omotosho, a zaman da aka ci gaba da zaman, cewa a shirye yake ya kare kansa.

Biyo bayan matakin da shugaban kungiyar ta IPOB ya dauka, dukkan manyan masu fafutuka a cikin kungiyar da suka hada da Cif Agabi, tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), sun janye daga ci gaba da fitowarsu a shari’ar.

Dangane da wannan al’amari, Kanu, wanda a yake gabatar da jawabi a gaban kotun, ya kalubalanci hurumin kotun da ta gurfanar da shi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa Kanu ya sanya hannu a kan korafinsa kuma ya shigar da shi a ranar 21 ga watan Oktoba.

Ya kuma sanya tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami da sauran su, a matsayin shaidu a ci gaba da shari’ar da ake yi na zargin ta’addanci, kuma ya jera manyan mutane da dama a matsayin shaidu.

Daga cikin wadanda Kanu ya lissafa a matsayin “shaidu masu karfi” akwai Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike; tsohon ministan tsaro, Janar Theophilus Danjuma mai ritaya da kuma tsohon babban hafsan sojin kasa, Janar Tukur Buratai mai ritaya.

Sauran sun hada da, Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas, Gwamna Hope Uzodinma na Imo, ministan ayyuka, Dave Umahi, tsohon Gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu, da tsohon Darakta-Janar, Hukumar Leken Asiri ta (NIA), Ahmed Abubakar.

Sauran sun hada da tsohon shugaban hukumar tsaro ta farin kaya, Yusuf Bichi, da kuma shaidu da dama da bai bayyana sunayensu ba.

Kanu, a cikin karar, ya yi alkawarin gabatar da bayanan rantsuwar dukkan shaidun, na son rai ga wannan kotu mai girma, kuma za su sanar da masu gabatar da kara a lokacin da ya  dace.

Hakazalika, NAN ta ruwaito cewa shugaban na IPOB ya yi ganawar sirri da tawagar lauyoyin sa a babbar kotun kasa a Abuja ranar Laraba.

Kanu wanda jami’an hukumar tsaro na farin kaya (DSS) suka gabatar da shi a kotu, ya gana da ‘yan kungiyar llauyoyin nasa a kotun mai shari’a James Omotosho, kamar yadda aka umarta a baya.(NAN)(www.nannews.ng)

TOA/SH

Fassarar Aisha Ahmed 

=====

 

Shugabar wata karamar hukuma a Legas ta haramta cinikin gefen hanya

Gefen hanya

Daga Idris Olukoya

Epe (Lagos), Oktoba 23, 2025 (NAN) Shugabar karamar hukumar Epe ta jihar Legas, Ms. Surah Animashahun, ta yi gargadi da a daina yin ciniki a gefen titi a yankin, saboda hadurran da ke tattare hakan da kuma cunkoson ababen hawa.

Animashahun, ta shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Alhamis cewa, matakin ya zama dole domin inganta zirga-zirgar ababen hawa, da inganta lafiyar jama’a, da kuma maido da tsari a wuraren da jama’a ke cunkoso.

Ta ce, an kai samame ne a kan muhimman wurare kamar; Kasuwar Aiyetoro, Tsohon Garage Ijebu-Ode, Ita-Opo, Kasuwar Inuwa da sauran wuraren da aka gano a cikin al’umma.

“Yan kasuwa a wadannan yankuna sun samu koma bayan tsarin hanya da kuma hanyoyin tafiya, domin hakan  na haifar da hadari mai tsanani.

“Daga yanzu, majalisar ba za ta amince da yin cinikin gefen hanya ba, saboda hadurra da cunkoson ababen hawa,” in ji ta.

Shugaban ya ce jami’an kungiyar yaki da rashin da’a ta Kick Against Indiscipline (KAI), za su zagaya domin gudanar da ayyukan dakile cin hanci da rashawa da ake yi a kan tituna a fadin al’umma.

Animashahun, ta kuma bayyana cewa, an samu hadurra da dama a kan titin Aiyetoro, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi sakamakon tukin ganganci.

“Ba za mu iya ci gaba da jure asarar rayuka da dukiyoyi ba sakamakon rashin da’a daga mutanenmu, saboda hanyoyin mota ne, ba na kasuwanci ba,” in ji ta.

Ta bayyana cewa, karamar hukumar ta samar da wurin da ya dace a bayan kasuwar Aiyetoro domin ‘yan kasuwa su gudanar da harkokinsu lafiya ba tare da hana zirga-zirga ba.

“Mun yi isassun shirye-shirye domin ‘yan kasuwarmu su yi cinikinsu a bayan kasuwa, inda masu ababen hawa ba sa wucewa, a hukumance an kebe wurin domin yin ciniki,” inji ta.

Shugaban karamar hukumar, ta bada tabbacin cewa ana ci gaba da kokarin sake gina kasuwar Aiyetoro, wadda ta ruguje a zamanin gwamnatin tsohon gwamna Akinwunmi Ambode.

Ta kara da cewa, nan ba da dadewa ba, za a sake gina kasuwar a karkashin jagorancin Gwamna Babajide Sanwo-Olu, inda ta cigaba da cewa, tattaunawa da tsare-tsare sun yi nisa.

NAN ta ruwaito cewa, ‘yan kasuwa a wuraren da abin ya shafa kamar, Aiyetoro, Ita-Opo, Shade, Popo Oba, da Papa, an umurce su da su koma kasuwannin da gwamnati ta amince da su.

Karamar hukumar ta kara yi gargadin cewa, duk dan kasuwan da ya karya dokar zai fuskanci takunkumi a atisayen aiwatar dokar a gaba.

Animashahun ta cigaba da cewa ba wai an yi wannan shiri ne don farautar kowa ba, sai don tabbatar da tsari, da’a da kuma tsaron mazauna yankin.

Ta yi kira ga shugabannin kasuwar, da shugabannin al’umma da su wayar da kan ‘ya’yansu akan muhimmancin bin doka da oda, inda ta jaddada cewa gyare-gyaren harkokin gudanar da birane za su ci gaba da samun fifiko a karkashin gwamnatinta. (NAN)(www.nannews.ng).

 

SIO/KOLE/CHOM

========

 

Remi Koleoso/Chioma Ugboma ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara

Wata gidauniya ta zaburar da sarakuna domin yaki da cin zarafin mata a Bauchi

Daga Amina Ahmed

Ningi (Bauchi srate), Oktoba 23, 2025 (NAN) Wata kungiya mai zaman kanta, Ikra Foundation for Women and Youth Development (IKFWYD), ta fara wani shiri na shekaru biyu, don zaburar da maza wajen magance cin zarafi.(GBV).

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa ana aiwatar da shirin ne a kananan hukumomin Bauchi, Ningi, da Toro.

Jami’in sa ido da tantancewa na gidauniyar, Isma’il Umar ne ya bayyana hakan a wani taron bayar da shawarwari da aka gudanar da hakiman kananan hukumomi a garin Ningi.

Ya ce rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa na yin tasiri mai kyau wajen canza halayya tare da hana wuce gona da iri ba.

“An tsara shirin ne domin jawo hankalin maza, kan batutuwan da suka shafi kare hakkin mata da ‘ya’ya mata baki daya.

“Ba za a iya samun jin daɗin iyali da haɗin kai ba, ba tare da sa hannun maza ba,” in ji shi.

Umar ya lura cewa, kalubale kamar rashin fahimtar juna ta jinsi, rashin fahimtar juna a cikin gida, rashin fahimtar juna a tsakanin ma’aurata, da karancin sanin nauyin da ya rataya a wuyansu na haifar da rashin zaman lafiya a iyali.

“In aka mayar da hankali ga maza a matsayin abokan haɗin gwiwa don inganta zaman lafiya da walwala, wannan shirin yana da nufin ƙarfafa tasirin su a cikin iyalai da al’ummomi,” in ji shi.

Umar ya kara da cewa, shirin zai samar da hadin kai tsakanin maza da mata, wajen wanzar da zaman lafiya a gidajen aure.

Shi ma da yake jawabi, Mista Bamidele Jacobs, Daraktan Shari’a na Lauyoyin Alert, ya ce Lauyoyin ALert da Iqra Foundation, za su aiwatar da shirin na tsawon shekaru biyu.

A cewarsa, maza na da matukar muhimmanci wajen dakile barazanar GBV, ya kara da cewa za a zabi zakarun maza don gudanar da shirin.

A nasu jawabai mabambanta, sarakunan gargajiya sun bayyana goyon bayansu da jajircewarsu ga shirin.

Hakimin Ningi, Alhaji Yusuf Danyaya, ya yi alkawarin zaburar da maza domin gudanar da wannan shiri, inda ya ce “gidan da babu tashin hankali yana haifar da zaman lafiya a cikin al’umma.”

Hakazalika, Hakimin Miri da ke cikin birnin Bauchi, Alhaji Hussaini Uthman, ya ce manufar shirin ta yi daidai da irin rawar da shugabannin al’umma ke takawa wajen samar da sulhu a tsakanin ma’aurata.

A nasa bangaren, Hakimin Toro, Alhaji Umar Adamu, ya ce, yin jawabi akan GBV, wani nauyi ne da ya rataya a wuyansu domin tabbatar da cewa al’umma sun kasance cikin aminci da lumana. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AE/BEKl/KLM

iEdited by Abdulfatai Beki/Muhammad Lawal

Fassarar Aisha Ahmed 

 

Gwamnatin Tarayya ta jajantawa Gwamna Bago, al’ummar Nijar bisa fashewar tankar mai

Ta’aziyya

By Collins Yakubu-Hammer

Abuja, Oktoba 23, 2025 (NAN) Gwamnatin tarayya ta jajanta wa gwamnati da al’ummar Neja bisa fashewar wata tankar man fetur a garin Essa, da ke karamar hukumar Katcha a jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar ranar Alhamis a Abuja

Takardar ta bayyana matukar alhininsa bisa afkuwar lamarin da yayi sanadin salwantar rayuka da kuma jikkata wasu da dama.

“Muna tare da gwamnati da al’ummar jihar Neja wajen jimamin wannan rashi.

“Wannan lamari mai ratsa zuciya, ya sake haifar da mummunar illar hadurran tankar mai a cikin al’ummarmu.

“Gwamnatin tarayya, ta yi bakin cikin cewa, duk da cigaba da wayar da kan jama’a tare da gargadi game da illolin kwasar man fetur daga fadowar tankunan man fetur, har yanzu wasu na yin kasadar da ke barazana ga rayuwa.

“Kowane ran dan Najeriya yana da daraja, kuma irin wadannan bala’o’in za a iya kauce musu sun zama izina domin ƙarin kulawa da bin umarnin tsaro,” in ji Idris.

Ya yaba da yadda gwamnatin Neja, hukumomin tsaro da masu bada agajin gaggawa, suka gaggauta daukar matakin kashe gobarar, tare da ceto wadanda suka tsira da rayukansu, kuma suka bayar da tallafi ga iyalan wadanda abin ya shafa.

Ministan ya ce an kuma umurci Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), da ta kara kaimi akan kokarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agaji da magunguna ga wadanda abin ya shafa da iyalansu.

“Gwamnatin tarayyar ta kuma umurci hukumar wayar da kan jama’a ta kasa, da ta kara kaimi wajen wayar da kan jama’a a fadin kasar.

“A kara tsaurara matakan tsaro, musamman a yankunan karkara da masu fama hadariurra, domin hana sake afkuwar irin wannan bala’i.

“Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da wadanda abin ya shafa tare da iyalansu, da daukacin al’ummar Neja a wannan lokaci na bakin ciki.

“Allah Ya jikan wadanda suka rasu, kuma Allah Ya bawa ‘yan’uwansu ikon jure wannan rashi mai raɗaɗi,” in ji Idris. (NAN) (www.nannews.ng)

 

CMY/BEKl/BRM

==============

Edited by Abdulfatai Beki/Bashir Rabe Mani

Fassarar Aisha Ahmed

 

Wata mata ta nemi kotu ta raba aurenta saboda rashin soyayya

Soyayya

By: Mujidat Oyewole

Ilorin, Oct. 23, 2025 (NAN) Wata mata mai suna Misis Hajara Busari, ta roki wata kotu da ke garin Ilorin, da ta raba aurenta da mijinta, Mista Mumini Anafi, shekaru shida da suka gabata, saboda rashin soyayya.

Mai shigar da kara ta shaida wa kotun a ranar Alhamis cewa, ita ba ta da sha’awar auren na bisa addinin Musulunci da mijinta, kuma ta bukaci kotun da ta raba su.

Tace tana neman umarnin a raba aure, kuma a bata hakkin kula da ‘ya’yanta uku, da kuma kudi N50,000, a matsayin kudin kula da ‘ya’yanta.

A halin da ake ciki, mijin da ake kara, ya shaida wa kotun cewa har yanzu yana sha’awar zaman aure da matarsa, kuma ya bukaci kotun da kada ta yi sassauci akan abunda mai shigar da kara ya nema.

Alkalin kotun, Mista Toyin Aluko, ya bukaci maigidan da ya binciko duk wata dama da zai samu, domin samun sulhu cikin lumana kan duk wata takaddama da matarsa.

Kotun ta dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 17 ga watan Disamba, domin samun rahoton sasantawa ko kuma sauraron karar. (NAN)www.nannews.ng

 

MOB/UNS

======

 

Sandra Umeh ta gyara

Aisha Ahmed ta Fassara

Hukumar NESREA ta lalata buuhunan sassan jikin jakuna 700 da Kwastam ta mika mata

Jaki

Doris Esa

Abuja, Oktoba 16, 2025 (NAN) Hukumar Kula da Muhalli ta Kasa (NESREA) ta ce, ta lalata buhunan sassan jikin jakuna 700 da Hukumar Kwastam ta Najeriya ta mika mata a Kaduna.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Misis Nwamaka Ejiofor, mataimakiyar daraktar yada labarai ta NESREA ta fitar a Abuja.

Ta ce hakan ya yi daidai da ka’idojin muhalli da ka’idojin aminci.

Ejiofor ta ce, an lalata kasusuwan jakuna da fatun ne a ranar 3, 4 da 6ga watan Oktoba, a Kaduna.

“An yi amfani da wurare guda biyu don kona kasusuwan, yayin da aka binne fatun a wani wuri da aka kebe.

 “An gudanar da atisayen ne a gaban jami’an tsaro kuma bisa ka’idojin muhalli,” in ji shi.

Ta ce an samu nasarar gudanar da atisayen ne ta hanyar hadin gwiwar hukumar ta NESREA da hukumar Kwatam.

Ejiofor ta kara da cewa, sun tabbatar da cewa an yi aikin ne cikin aminci da kiyaye muhalli.

“Wannan ya nuna gagarumar nasara, a kokarin da ake na yaki da fataucin namun daji da kuma kare nau’o’in su da ke cikin hadari.

 “An gudanar da aikin ne a ƙarƙashin tsauraran ka’idojin hadin gwuiwa, don hana duk wani haɗarin muhalli ko lafiya.

“Ma’aikatun da ke cikin atisayen sun sanya kayan kariya na sirri, kuma an dauki matakan rage hadarin kamuwa da duk wata illar da za ta shafi rayuka,” in ji ta.

Ejiofor ta jaddada cewa hukumar NESREA a watan Yuli ta kona sama da buhu dari na al’aurar jakuna da hukumar kwastam ta Najeriya ta mika a Abuja.

Darakta Janar na Hukumar NESREA, Farfesa Innocent Barikor, ya koka da yadda jakuna ke raguwa a Najeriya, ya yi gargadin cewa sannu a hankali suna mutuwa.

Barikor ya jaddada tsayuwar daka da gwamnatin Najeriya ta ke yi na yaki da safarar jakuna ba bisa ka’ida ba.

Ya ce an dauki jakuna dabbobin gida, amma bukatarsu da masu safarar miyagun kwayoyi suke yi don yin maganin kara karfin sha’awa, ya sa gwamnatin tarayya ta ba da umarnin hana sayar da ita.

Barikor ya ce, lalata sassan jakunan da hukumar NESREA da NCS suka yi, an yi shi ne don hana fataucin jakunan ba bisa kaida ba.

Ya yi godiya ga hukumar ta Kwastam bisa gagarumin goyon baya ga yaki da fataucin miyagun kwayoyi da ke cikin hadari. (NAN) (www.nannews.ng)

 

Chidi Opara ya gyara ORD/CEO

Aisha Ahmed Ta fassara.

Sokoto ta yiwa yara 2.2m alluran rigakafi, ta fadada zirga-zirga zuwa makarantu, wuraren ibada

Sokoto ta yiwa yara 2.2m alluran rigakafi, ta fadada zirga-zirga zuwa makarantu, wuraren ibada

Yin rigakafi

Daga Habibu Harisu

Sokoto, Oct. 14, 2025 (NAN) A kalla yara miliyan biyu da dubu dari biyu ne aka basu alluran rigakafin cutar kyanda, rubella, poliomyelitis, da sauran cututtuka da za a iya rigakafin su a yakin neman rigakafin hadaka da ake yi a jihar Sokoto.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya rawaito cewa gwamnatin jihar Sokoto ta kara kaimi wajen wayar da kan jama’a a majami’u, masallatai, makarantu, kasuwanni, da sauran wuraren da jama’a ke taruwa domin tabbatar da ganin an samu karuwar jama’a.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dakta Faruku Wurno ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin wani taron bita.

Ya kuma bukaci iyaye da masu kula da su da su tabbatar an yi wa ‘ya’yansu da allurar rigakafi, yana mai jaddada cewa wadannan alluran rigakafin na da matukar muhimmanci domin kare su daga kamuwa da cututtuka masu illa ga rayuwa amma wadanda za a iya magance su.

Wurno ya ce gangamin wani bangare ne na wani shiri na kasa baki daya na inganta harkar allurar rigakafi da kuma inganta mallakar al’umma na shirye-shiryen kiwon lafiyar jama’a.

Ya kara da cewa gwamnatin jihar ta dauki kwararan matakai na wayar da kan jama’a da wayar da kan jama’a.

Ya kuma yabawa mahukuntan Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo (UDUTH) bisa hadin kan da suka bayar wajen magance matsalolin da wasu ma’aikatan suka nuna a lokacin yakin neman zabe.

Bugu da kari, ya mika godiyarsa ga sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da kwamishinonin ilimin sakandare, kananan hukumomi da masarautu, da majalisar Sarkin Musulmi, bisa taimakon da suka taimaka wajen magance rashin fahimtar juna a tsakanin al’umma a wajen aikin rigakafin.

Da yake magana kan ci gaban yakin neman zaben, Dr Hamza Yusuf, Manajan yakin neman zaben ya bayyana cewa, atisayen ya samu kusan kashi 65 cikin dari ya zuwa yanzu.

Ya kara da cewa kararrakin rashin bin ka’ida ba su da yawa kuma ana magance su.

Yusuf ya bayyana yankunan da ke fama da matsalar tsaro kamar Tureta, Sabon Birni, da Isa a matsayin yankunan da aka fi ba da fifiko domin kara kaimi.

Ya kuma lura da Wamakko, Sokoto ta Arewa, da Sokoto ta Kudu a matsayin wadanda suka fi kowa yawan rashin bin doka.

“Muna tsara dabarun da suka dace don isa ga al’ummomin da ke nesa da kuma yin aiki kafada da kafada da masu ruwa da tsaki don shawo kan juriya,” in ji Yusuf, yayin da yake yaba wa abokan hadin gwiwa kan goyon baya da karfafa gwiwa.

Wurno ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kiyaye lafiyar kowane yaro, inda ya yi kira ga iyaye, masu kulawa, da shugabannin al’umma da su ba da goyon bayan yakin neman zabe tare da tabbatar da cewa babu wani yaro da ya cancanta da ba a yi masa allurar ba.

A halin da ake ciki kuma, NAN ta ruwaito cewa an kafa wani kwamiti ne biyo bayan tattaunawa da hukumar ta UDUTH, karkashin jagorancin babban daraktan kula da lafiya Farfesa Anas Sabir, domin inganta hada kai a tsakanin al’ummar asibitin.

An sami keɓancewar al’amura a  makarantar firamare ta Rumbukawa da ke karamar hukumar Sakkwato ta Arewa, wasu ‘yan daba sun far wa tawagar masu allurar rigakafin cutar, lamarin da ya yi sanadin jikkatar wadanda suka jikkata tare da kwantar da su a asibiti.

A wani labarin kuma wata yarinya ta kamu da rashin lafiya bayan an yi allurar rigakafin a makarantar Sultan Maccido, kuma a halin yanzu tana jinya a asibitin mata da yara na Maryam Abacha.

An tura tawagar likitoci don tantance lamarin.

Kwamishinan ya ba da umarnin daukar mataki cikin gaggawa kan lamarin biyu, ya kuma ba da tabbacin tabbatar da tsaron lafiyarsu, yana mai cewa an karfafa matakan tsaro a dukkan matakan yakin. (NAN) ( www.nannews.ng )

HMH/AMM

=======

Abiemwense Moru ne ya gyara

Yakubu ya sauka daga mukamin shugaban hukumar zabe, ya mika wa Agbamuche-Mbu

Yakubu ya sauka daga mukamin shugaban hukumar zabe, ya mika wa Agbamuche-Mbu

INEC

Daga Emmanuel Oloniruha

Abuja, Oct. 7, 2025 (NAN) Farfesa Mahmood Yakubu a ranar Talata ya sauka daga matsayin shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Yakubu ya mika wa Mrs May Agbamuche-Mbu, babbar kwamishina ta kasa a matsayin mukaddashin shugabar hukumar, har sai an nada sabon shugaban hukumar.

Yakubu ya bayyana hakan ne a ci gaba da ganawa da kwamishinonin zabe a hedikwatar INEC da ke Abuja, inda ya sanya hannu kan takardar ficewa daga hukumar.

Yayin da yake yaba wa a kan damar da aka ba shi na yin aiki, ya nemi goyon bayan Agbamuche-Mbu har sai an nada shugaban na kasa.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya nada Yakubu shugaban hukumar ta INEC a ranar 21 ga watan Oktoba, 2015 kuma ya sake nada shi a watan Disamba 2020. (NAN)(www.nannews.ng)

OBE/WAS

Edited by ‘Wale Sadeeq

Hanyoyin Arewa, ayyukan layin dogo don za su bunkasa tattalin arziki – mai taimaka wa shugaban kasa

Hanyoyin Arewa, ayyukan layin dogo don za su bunkasa tattalin arziki – mai taimaka wa shugaban kasa

Tattalin Arziki

By Ramatu Garba

Kano, Oct. 1, 2025(NAN) Fadar shugaban kasa ta ce ayyukan tituna da na layin dogo da ake yi a Arewacin Najeriya za su kara habaka harkokin tattalin arziki da inganta kasuwanci a yankin.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa Abdulaziz Abdulaziz ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga mambobin kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) a Kano ranar Talata.

Ya ce hanyar Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano, babbar hanyar Sokoto zuwa Badagry, da layin dogo na Kano-Katsina-Maradi, zai bude sabbin hanyoyin kasuwanci, da saukaka zirga-zirgar kayayyaki, da karfafa cudanya tsakanin al’umma.

“Wadannan ayyuka ba na tituna da gadoji ba ne kawai.

*Labarin tattalin arziki ne da za su hada kasuwanni, gungu-gungu na noma, da kasuwanci, samar da ayyukan yi da habaka yawan aiki,” in ji Abdulaziz.

Ya bayyana cewa da gangan gwamnatin ta ci gaba da gudanar da ayyukan da aka gada tare da kaddamar da wasu sabbi domin tabbatar da daidaiton ci gaban kasa baki daya.

A cewarsa, ayyukan sun nuna imanin shugaba Bola Tinubu kan hada kan kasa da kuma ci gaba mai dorewa ga ‘yan Najeriya.(NAN)(www.nannews.ng)

RG/BRM

==========

Edited by Bashir Rabe Mani

Gwamnatin Tarayya, Kungiyoyin ma’aikatan Mai da kamfanin Dangote sun cimma matsaya kan rikicin matatar mai

Gwamnatin Tarayya, Kungiyoyin ma’aikatan Mai da kamfanin Dangote sun cimma matsaya kan rikicin matatar mai

Yarjejeniyar

By Joan Nwagwu

Abuja, 1 ga Oktoba, 2025 (NAN) A ranar Talata ne gwamnatin tarayya ta sasanta tsakanin kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya (PENGASSAN) da mahukuntan matatar man Dangote.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Dr Muhammad Maigari-Dingyadi ya fitar tare da sanya wa hannu a karshen taron sulhu na kwanaki biyu da aka gabatar wa manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Taron wanda ya gudana a ranakun litinin da talata, ya tattaro mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ministocin kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, da kuma ma’aikatar man fetur (Gas), tare da hukumar DSS, NIA, NNPC, NMDPRA, NUPRC da shugabannin kwadago.

Idan dai za a iya tunawa, an gudanar da zaman sulhun ne bayan da kungiyar PENGASSAN ta umurci mambobinta da su dakatar da samar da iskar gas tare da janye ayyukan da suke yi daga matatar.

Kungiyar ta zargi kamfanin da dakatar da daukar ma’aikata sama da 800 na mambobinta, lamarin da ya janyo daukar matakin masana’antu.

Matatar Dangote, ta bayyana cewa an kori ma’aikata ne saboda wani aikin sake fasalin da ake yi a kamfanin.

A cewar sanarwar, taron ya yanke shawarar cewa hadakar wani muhimmin hakki ne na ma’aikata a karkashin dokokin Najeriya kuma dole ne kamfanin ya mutunta shi.

An kuma amince da cewa hukumar ta Dangote Group ta gaggauta fara tura ma’aikatan da abin ya shafa zuwa wasu rassan kungiyar ba tare da an yi asarar albashi ba.

Taron ya kuma tabbatar da cewa babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa saboda shiga rigimar da ke tsakanin PENGASSAN da kamfanin.

Ita kuma PENGASSAN ta amince ta fara shirin janye yajin aikin nata, yayin da bangarorin biyu suka yi alkawarin aiwatar da kudurorin cikin aminci.(NAN)(www.nannews.ng)

JAN/BRM

=========

Edited by Bashir Rabe Mani