Zaben cike gurbi: An kama mutane 100 bisa zargin bangar siyasa a Kano

Banga

Daga Aminu Garko

Bagwai (Kano) Aug.16, 2025 (NAN) Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano, ta tabbatar da cewa an kama sama da mutane 100 da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne a karamar hukumar Bagwai yayin zaben cike gurbi da ake gudanarwa a jihar.

Kwamishinan zabe na jihar Kano, Mista Abdu Zango, ya tabbatar da faruwar lamarin, yayin da yake zantawa da manema labarai, bayan ya duba zaben da aka gudanar a garin Bagwai a ranar Asabar.

Ya ce an samu wadanda ake zargin dauke da makamai daban-daban, kuma Zango ya nuna jin dadinsa da yadda zaben ya gudana.

A cewarsa, an samar wa jami’an zabe kayayyakin da suka dace a duk wuraren da aka kebe.

Sai dai ya tabbatar da cewa an samu wasu tsaikon a harkar saboda al’amuran da suka shafi dabarun samun ingantaccen tsaro.

Ya ce akwai jami’an tsaro a dukkan wuraren zabe domin tabbatar da doka da oda tare da gudanar da zabe cikin lumana. (NAN) (www.nannews.ng)

AAG/ISHsa Ishola/Sam Oditah ne ya gya

 

Aisha Ahmed ta fassara

Mamakon ruwan sama yana yi mana barazana – manoman shinkafa a Abakaliki

 Douglas Okoro

Abakaliki, 6 ga Agusta, 2025 (NAN) Manoman shinkafa a Abakaliki, sun koka kan yadda ake samun mamakon ruwan sama, wanda a cewarsu yana barazana ga noman shinkafa a shekarar 2025.

Manoman, sun bayyana damuwar tasu ne a wata tattaunawa da suka yi da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a ranar Laraba a garin Abakaliki.

An dai samu mamakon ruwan sama a bana wanda ya yi sanadin ambaliya da asarar amfanin gona a manyan yankunan da ake noman shinkafa a jihar.

Mista Emmanuel Nwali, wani fitaccen manomin shinkafa a karamar hukumar Izzi, ya ce kusan rabin gonar shinkafarsa ta nutse sakamakon ruwan sama mai yawa.

“Ambaliya ta lalata yawancin gonakinmu, abin da ya rage tuni ya koma tawaya.

“Kusan kullum ana ruwan sama tun tsakiyar watan Yuli. Wataƙila ba za mu yi tsammanin samun girbi mai yawa a wannan kakar ba,” in ji Nwali.

Wani manomi, Mista Chinedu Okenwa, ya ce ya yi asarar gidajen yara na reno sakamakon ambaliyar ruwa, wanda ya yi sanadin asarar manyan albarkatu.

“Ban san yadda zan gyara asarar da aka yi ba, domin a halin yanzu, ba zan iya dasa komai ba don ya lalace.

“Muna fuskantar karancin amfanin gona a wannan kakar, kuma hakan na iya haifar da hauhawar farashin shinkafar gida a shekara mai zuwa,” in ji shi.

Hakazalika, Mista Aloysius Njoku, wani Mai nomana kasuwanci, ya ce ya yi asarar wani kaso mai yawa na gonar shinkafa sakamakon ambaliya, kuma yana fargabar ci gaban zai yi illa ga girbi.

“Damina da ambaliyar ruwa sun yi mummunar barna, idan ba a yi wani abu ba, shinkafa za ta yi karanci da tsada, kuma kowa zai ji ajikinsa,” in ji Njoku.

Misis Sylvia Elom, wata ma’aikaciyar gwamnati kuma mai noman shinkafa, ta bayyana ddamuwarta inda tace barnar da ruwan sama ya yi a gonaki ta yi kamari kuma abun zai shafi mutane da dama da suka dogara da noman shinkafa domin tafiyar da rayuwarsu.

“Shinkafa ita ce babbar hanyar samun kudin shiga ga yawancin mutanenmu wadanda galibi manoma ne, idan ambaliyar ruwa ta lalata mana gonakinmu, ba a bar mu da komai ba kenan,” in ji ta.

A halin da ake ciki, Dr Paul Onwe, wani kwararren manoma mai zaman kansa, ya bayyana cewa akwai gagarumar matsala a noman shinkafa idan damuna ta tsawaita aka samu ambaliya.

Ya kara da cewa ruwan sama kamar da bakin kwarya, yana haifar da babbar barazana ga gonakin shinkafa, musamman wadanda ke cikin fadamu.

Ya shawarci manoma da su mai da hankali sosai kan hasashen yanayi kafin su fara noman shinkafa, yana mai cewa gwamnatin tarayya na bayar da gargadin a farkon kowace kakar noma.

“Filayen da ke cikin ƙasa suna fama da takurewar girma, ƙarancin abinci mai gina jiki, da cututtukan fungal,” Onwe yayi gargaɗi.

Wata majiya daga ma’aikatar noma ta jihar Ebonyi da ta nemi a sakaya sunanta, ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar na bin diddigin illolin da ambaliyar ruwa ta haifar a gonaki a halin yanzu.

Ya kara da cewa gwamnati na kuma tattara rahotanni daga yankunan da abin ya shafa domin daukar matakan da suka dace.

NAN ta ruwaito cewa hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), a hasashenta na yanayi, ta bayyana jihar Ebonyi a matsayin daya daga cikin jihohin da ake sa ran za su fuskanci ambaliyar ruwa a lokacin damuna ta 2025.

Jihar Ebonyi dai na daya daga cikin jihohin da ake noman shinkafa a Najeriya, kuma ‘yan kasuwar shinkafa a manyan kasuwannin Abakaliki, sun bayyana fargabar cewa farashin shinkafar na iya tashi sakamakon rashin girbi da ake sa ran za a samu. (NAN) (www.nannews.ng)

 

Edited by Aisha Ahmed

Kotu ta daure wani mutum saboda laifin satar tukunya

Hukunci

 

By Funmilayo Okunade

Ado-Ekiti, Aug. 6, 2025 (NAN) Wata kotun majistare dake Ado-Ekiti, ta yankewa wani matashi mai shekaru 33, Ige Bola, hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni biyu tare da aiki mai wahala bisa samunsa da laifin satar tukunyar da darajarsu ta kai N100,000.

Yayin hukuncin, a ranar Laraba, Alkalin kotun, Mista Bankole Oluwasanmi, ya yanke wa Bola hukunci ne bayan amsa laifinsa da kuma tabbatar da gaskiyar lamarin.

Dan sanda mai shigar da kara, Sifeto Elijah Adejare, ya shaidawa kotun cewa wanda ake tuhuma, ya aikata laifin ne a ranar 31 ga watan Yuli da misalin karfe 6:30 na yamma a Ilawe-Ekiti.

Adejare ya ce, wanda ake tuhumar ya saci tukwane guda uku da kudinsu ya kai N100,000 mallakar wani mutum mai suna Adenike Temiyemi.

Ya kara da cewa, wanda ake tuhumar a yanzu ya saci tukwanen ne a Ilawe-Ekiti ya kawo ta Ado-Ekiti, inda ya kara da cewa jami’an tsaro na Agro marshal sune suka kama shi.

Mai gabatar da karar yace an kama wanda ake tuhuma a lokacin da yake daukar tukwanen, daga bisani aka mika shi ga ‘yan sanda.

Ya kara da cewa ‘yan sanda sun kwato tukwanen kuma laifin ya ci karo da sashe na 302(1) (a) na dokar laifuka ta jihar Ekiti, 2021.(NAN)( www.nannews.ng )

FOA/DCO

Edited by Aisha Ahmed

Kotu ta daure wata mata yar shekaru 25, bisa zargin satar jariri dan watanni biyu

Daga Olawale Akinremi

Ibadan, Aug. 5, 2025 (NAN) Wata babbar kotun majistare da ke zamanta a Mapo, a Ibadan  ta bayar da umarnin tsare wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Odunayo Odunlade, a gidan gyaran hali na Agodi, bisa zargin satar jariri dan watanni biyu.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa Odunlade ta musanta zargin da aka yi mata, sai dai wanda ake zargin ba ta iya cika sharuddan belin da kotu ta yi mata ba.

Alkalin kotun, Mrs OO Latunji, ta bada belin Odunlade a kan kudi naira 500,000, tare da sa hannun wasu amintattun mutane guda biyu.

Daga bisani Latunji, ta dage zaman shari’ar zuwa ranar 21 ga watan Oktoba, domin yi kammala shari’ar.

Lauya mai shigar da kara, Insp. Oluseye Akinola, ya shaida wa kotun cewa, wadda ake tuhuma ta aikata laifin ne a ranar 24 ga watan Yuli, a unguwar Lascap-Oniyanrin da ke Ibadan.

Akinola ya ce, Odunlada saci yaron ne daga dakin da mahaifiyarsa ta ajiye shi, ya kara da cewa jami’an ‘yan sanda a ofishinsu na Mokola, sun kai daukin gaggawa bayan sun samu bayanai kan ta’asar.

Jami’in ya tabbatar da cewa ‘yan sanda sun yi nasarar bin diddigin wadda ake kara, a wani wurin da bai bayyana ba, kwanaki kadan bayan sace yaron.

A cewar sa, laifin da matar da ake zargi ta aikata, ya ci karo da tanadin sashe na 390(9) na kundin laifuffuka, Cap. 38, Vol. ii, Dokar Jihar Oyo, 2000. (NAN)

Edited by Aisha Ahmed

 

Annoba a Neja: Matar Tinubu ta ba da gudummawar N1bn ga wadanda abin ya shafa

 

Daga Celine-Damilola Oyewole

Ambaliya

Minna, 5 ga Agusta, 2025 (NAN) Matar shugaban kasa, Sen. Oluremi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliyan daya don tallafawa mutanen da annoba ta shafa a fadin jihar Neja.

Tinubu, ta bayar da wannan tallafin ta hanyar aikin da ta kirkiro na Renewed Hope Initiative (RHI) a ranar Talata a Minna, ta ce wadanda za su ci gajiyar su ne wadanda ambaliyar ruwa, gobara, da hatsarin kwale-kwale da wadanda harin ‘yan fashi ya shafa.

Ta bayyana annoba a matsayin abin dubawa, inda ta ce, hakika wadannan lokuta ne masu wahala, ta kuma yi adduar Allah ya jikan wadanda suka rasu, tare da ba marasa lafiya wadanda suka jikkata Lafiya.

Uwargidan ta kuma amince da sa hannun gwamnatin tarayya cikin gaggawa, wajen raba kudade da kayayyakin agaji ga wadanda abin ya shafa.

Bugu da kari ta yi nuni da cewa, tausayi yana inganta al’umma ya na kuma kara mata jajircewa a lokutan wahala, inda ta kara da cewa, ya kamata mutane su koyi tausayawa juna.

“Na yi farin ciki da cewa Shugaba Bola Tinubu, ya amince da gaggauta a saki kudade da kayayyakin abinci don taimakawa wajen farfado da gine-ginen da ambaliyar ruwa ta lalata.

“Na zo nan ne domin in jajanta wa Gwamna Mohammed Bago, da al’ummar Jihar Neja, kan mumunar ambaliyar ruwa da ta addabi karamar hukumar Mokwa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

“Ina kuma yabawa kokarin gwamnan, na tashi tsaye wajen aiki tare da bayar da gudummawar kudade da abinci, domin tallafawa iyalan da suka rasa matsugunansu.

“Don tallafawa kokarin sake gina jihar Neja, majalisar gudanarwar kungiyar Renewed Hope Initiative, ta bayar da gudummawar Naira biliyan daya, tare da kayayyakin agaji.

“Kayayyakin sun hada da tufafi, takalma, da buhunan shinkafa 50,000 ga jihar ta Neja,” inji Uwargidan shugaban kasa Tinubu.

Mai dakin shugaban Kasar ta kuma jajantawa wadanda hatsarin kwale-kwale ya rutsa da su, da wadanda harin ‘yan bindiga ya rutsa da su, kana da wadanda suka ibtila’in gobara a jihar.

“A matsayina na uwa, na yi imanin cewa dukkanmu za mu iya shawo kan wannan bala’i tare da taimakawa al’umma ta wartsake. Allah ya baku lafiya, ya kuma jikan wadanda suka rasu.

“Za a yi amfani da kudaden wajen bada tallafin gidaje da muhimman kayayyaki, don a taimakawa iyalan wadanda suka rasa matsugunansu domin su dawo kan kafafunsu,” Uwargidan ta ce.

Haka kuma, ta jaddada cewa wannan ya yi daidai da manufar shirin nata, kamar yadda yake kunshe a taken su “Ingantacciyar Rayuwa zuwa ga Iyalai”.

Kamfanin Dillancin labarai na kasa (NAN), ya ruwaito cewa, gwamnan Neja, Umar Bago, ya yabawa shugaba Tinubu da matarsa bisa goyon bayan da suke baiwa jama’a. (NAN) (www.nannews.ng)

Edited by Aisha Ahmed