‘Yan sanda ssun cafke wani matasbi kan zargin kisan kakar sa da kawun sa
‘Yan sanda ssun cafke wani matasbi kan zargin kisan kakar sa da kawun sa
Kisa
Daga Suleiman Shehu
Ibadan, Satumba 9, 2024 (NAN) Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da tsare wani mutum mai matsakaicin shekaru dangane da zargin kisan kakansa da kawunsa a unguwar Apete da ke Ibadan.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Oyo, SP Adewale Osifeso, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ya aikewa kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a Ibadan ranar Litinin.
Osifeso ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike domin gano dalilin da ya sa ta aikata wannan aika-aika.
Ya kara da cewa za a ba wa jama’a bayanai bisa ga hakan.
“An fara bincike kan lamarin, yayin da za a ba da bahasin yadda ya kamata,” in ji shi.
NAN ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 6.00 na yammacin ranar Lahadi.
Wanda ake tuhumar, mai suna Ahmed, yana zaune ne a gida daya tare da mahaifinsa mai nakasa da kuma kawunsa mara lafiya. (NAN) (www.nannews.ng)
SYS/KOLE/MAS
==========
Remi Koleoso da Moses Solanke ne suka gyara