Wata mata ta nemi kotu ta raba aurenta saboda rashin soyayya

Wata mata ta nemi kotu ta raba aurenta saboda rashin soyayya

Spread the love

Soyayya

By: Mujidat Oyewole

Ilorin, Oct. 23, 2025 (NAN) Wata mata mai suna Misis Hajara Busari, ta roki wata kotu da ke garin Ilorin, da ta raba aurenta da mijinta, Mista Mumini Anafi, shekaru shida da suka gabata, saboda rashin soyayya.

Mai shigar da kara ta shaida wa kotun a ranar Alhamis cewa, ita ba ta da sha’awar auren na bisa addinin Musulunci da mijinta, kuma ta bukaci kotun da ta raba su.

Tace tana neman umarnin a raba aure, kuma a bata hakkin kula da ‘ya’yanta uku, da kuma kudi N50,000, a matsayin kudin kula da ‘ya’yanta.

A halin da ake ciki, mijin da ake kara, ya shaida wa kotun cewa har yanzu yana sha’awar zaman aure da matarsa, kuma ya bukaci kotun da kada ta yi sassauci akan abunda mai shigar da kara ya nema.

Alkalin kotun, Mista Toyin Aluko, ya bukaci maigidan da ya binciko duk wata dama da zai samu, domin samun sulhu cikin lumana kan duk wata takaddama da matarsa.

Kotun ta dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 17 ga watan Disamba, domin samun rahoton sasantawa ko kuma sauraron karar. (NAN)www.nannews.ng

 

MOB/UNS

======

 

Sandra Umeh ta gyara

Aisha Ahmed ta Fassara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *