Wata gidauniya ta zaburar da sarakuna domin yaki da cin zarafin mata a Bauchi

Wata gidauniya ta zaburar da sarakuna domin yaki da cin zarafin mata a Bauchi

Spread the love

Daga Amina Ahmed

Ningi (Bauchi srate), Oktoba 23, 2025 (NAN) Wata kungiya mai zaman kanta, Ikra Foundation for Women and Youth Development (IKFWYD), ta fara wani shiri na shekaru biyu, don zaburar da maza wajen magance cin zarafi.(GBV).

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa ana aiwatar da shirin ne a kananan hukumomin Bauchi, Ningi, da Toro.

Jami’in sa ido da tantancewa na gidauniyar, Isma’il Umar ne ya bayyana hakan a wani taron bayar da shawarwari da aka gudanar da hakiman kananan hukumomi a garin Ningi.

Ya ce rawar da cibiyoyin gargajiya ke takawa na yin tasiri mai kyau wajen canza halayya tare da hana wuce gona da iri ba.

“An tsara shirin ne domin jawo hankalin maza, kan batutuwan da suka shafi kare hakkin mata da ‘ya’ya mata baki daya.

“Ba za a iya samun jin daɗin iyali da haɗin kai ba, ba tare da sa hannun maza ba,” in ji shi.

Umar ya lura cewa, kalubale kamar rashin fahimtar juna ta jinsi, rashin fahimtar juna a cikin gida, rashin fahimtar juna a tsakanin ma’aurata, da karancin sanin nauyin da ya rataya a wuyansu na haifar da rashin zaman lafiya a iyali.

“In aka mayar da hankali ga maza a matsayin abokan haɗin gwiwa don inganta zaman lafiya da walwala, wannan shirin yana da nufin ƙarfafa tasirin su a cikin iyalai da al’ummomi,” in ji shi.

Umar ya kara da cewa, shirin zai samar da hadin kai tsakanin maza da mata, wajen wanzar da zaman lafiya a gidajen aure.

Shi ma da yake jawabi, Mista Bamidele Jacobs, Daraktan Shari’a na Lauyoyin Alert, ya ce Lauyoyin ALert da Iqra Foundation, za su aiwatar da shirin na tsawon shekaru biyu.

A cewarsa, maza na da matukar muhimmanci wajen dakile barazanar GBV, ya kara da cewa za a zabi zakarun maza don gudanar da shirin.

A nasu jawabai mabambanta, sarakunan gargajiya sun bayyana goyon bayansu da jajircewarsu ga shirin.

Hakimin Ningi, Alhaji Yusuf Danyaya, ya yi alkawarin zaburar da maza domin gudanar da wannan shiri, inda ya ce “gidan da babu tashin hankali yana haifar da zaman lafiya a cikin al’umma.”

Hakazalika, Hakimin Miri da ke cikin birnin Bauchi, Alhaji Hussaini Uthman, ya ce manufar shirin ta yi daidai da irin rawar da shugabannin al’umma ke takawa wajen samar da sulhu a tsakanin ma’aurata.

A nasa bangaren, Hakimin Toro, Alhaji Umar Adamu, ya ce, yin jawabi akan GBV, wani nauyi ne da ya rataya a wuyansu domin tabbatar da cewa al’umma sun kasance cikin aminci da lumana. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AE/BEKl/KLM

iEdited by Abdulfatai Beki/Muhammad Lawal

Fassarar Aisha Ahmed 

 


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *