Wani kamfanin Burtaniya ya ƙaddamar da dandamalin haɓaka harsunan Najeriya, al’adu da kayan tarihi
Wani kamfanin Burtaniya ya ƙaddamar da dandamalin haɓaka harsunan Najeriya, al’adu da kayan tarihi
Al’adu
By Ibukun Emiola
Ibadan, Satumba 11, 2024 (NAN) Wani kamfanin Burtaniya na fasahar zamani mai aiki da na’ura mai kwakwalwa ya ƙaddamar da samfurin karatu na zamani, ‘AE Learning’, don haɓaka harsuna da al’adun Najeriya tare da haɗakar harshen Jamusanci.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa kamfanin mai suna Afro-European Business Services Limited da ke Burtaniya, ya bayyana hakan ne a Ibadan ranar Laraba.
Babban Jami’in Kamfanin, Oluseun Durowoju, ya ce AE Learning shi ne taimaka wa dunkulewar al’adu daban-daban ta hanyar koyar da harsunan asali na Najeriya da sauran na Afirka.
A cewarsa, hanyar koyon an yi ta ne ga duk wanda ke son ya fara daga tushe ko kuma ya fahimci harsuna da al’adu daban-daban.
Ya ce koyon zai fadada zuwa sauran harsunan Afirka don saukaka fahimtar harsunan, da alaka da su da kuma saukakawa ga dalibai.
“Ko dai yaran da aka haifa a wajen Najeriya, wadanda ke da alaka da Najeriya, har ma da yaran da ke cikin Najeriya, wannan samfurin namu da malamanmu za su sa ya zama mai sauki da jin daɗi don koyon kowane yaren,” in ji shi.
Durowoju ya ce samfurin zai bude idanun duniya don fahimtar harsuna da al’adun Afirka da kyau, ta yadda za a inganta jituwa da haɗin kai.
Ya ci gaba da cewa fahimtar harsunan zai ba da ma’ana cika zaman tare, ya kawo canji kuma mafi mahimmanci ya sa mutum ya samu yarda da asalinsu na kakanni.
“Koyon AE an yi niyya ne don samar da samari na yanzu har ma da manya su san harsunansu na asali, baya ga yaren kasuwanci na duniya,” in ji shi.
Durowoju, wanda ya jaddada matsayin Babban Jami’in Ƙirƙirar kafar, ya bayyana cewa kamfanin ya kuma yi niyyar kawo manyan harsunan duniya ga masu sauraro a Afirka cikin sauƙi.
Wannan, in ji shi, zai samar da damammaki ga ‘yan Afirka na gida da waje, don koyo da kuma zama masu mu’amala da fahimtar harsunan waje daban-daban tare da taimakawa cikin saukin fahimtar wasu al’adu.
Babban Manajan Kayayyakin Kamfanin, Oluseyi Sodiya, ya bayyana kyakkyawan fata game da wannan samfurin, yana mai cewa, wani ra’ayi ne da aka tsara na samar da hanyoyin da za a rage matsalolin harshe wajen ciyar da rayuwar bil’adama gaba.
“Zai taimaka wajen inganta zaman lafiya tsakanin kowace kabila ta hanyar fahimtar al’adun juna, haka kuma zai taimaka matuka wajen inganta harkokin kasuwanci, mu’amalar jama’a da kuma alakoki daban-daban,” in ji Sodiya.
Babban manajan samfurin ya sanar da judanya da mutane 100 na farko don yin rajista na watanni biyu da kuma samun ƙarin watanni biyu kyauta.
“Mafi mahimmanci, dandalin yana da sauƙin amfani kuma yana da sauƙin shiga. An shirya kwasa-kwasan nazarin yarurrukan don nazarin kanmu.
“Za ku iya koyo da kan ku da kuma lokacin ku. Darussan gajeru ne, masu dacewa kuma an ƙirƙiresu ta hanyar umarni na gaske, ”in ji shi. (NAN) (www.nannews.ng)
IBK/KOLE/MAS
==========
Remi Koleoso da Moses Solanke ne suka gyara