Wadatar abinci ita ce fifikon Gwamnatin Tarayya – Minista

Wadatar abinci ita ce fifikon Gwamnatin Tarayya – Minista

Spread the love

Wadatar abinci ita ce fifikon Gwamnatin Tarayya – Minista

Abinci

By David Adeoye

Iseyin (Jihar Oyo) Satumba 11, 2024 (NAN) Ministan Albarkatun Ruwa da Tsaftar muhalli, Mista Joseph Utsev, ya ce wadatar abinci a Najeriya shi ne abin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta sa gaba.

Utsev ya bayyana haka ne a ranar Larabar da ta gabata a yayin wani rangadin tantancewa a sashen kula da noman rani na ” Centre Pivot Irrigation Project” da ke Iseyin a jihar Oyo.

A cewar ministan, aikin samar da abinci, samar da ayyukan yi da inganta tattalin arzikin kasa ya yi daidai da ajandar manufofin shugaban kasa.

Ya kuma jaddada kudirin gwamnatin tarayya na samar da kayayyakin da ake bukata wadanda za su bunkasa samar da abinci.

Ya ce ci gaba da bai wa sashen noman rani na jihar Ogun hadin gwiwa da cibiyar samar da wutar lantarki ta kasa, wani bangare ne na kokarin karfafa noman rani.

“An fara aikin noman rani na Middle Ogun a shekarar 1990, kuma manufar aikin shine a samar da fili kimanin hekta 12,000 a noman.

“Lokacin da aka fara aikin an yi amfani da man dizal ne wajen samar da wutar lantarki amma yanzu mun canza tsarin samar da wutar lantarkin zuwa hasken rana da wutar lantarki ta kasa saboda tsadar mai na dizal da wasu dalilai,” inji shi. .

Ministan ya bayyana cewa an kai kashi 95 cikin 100 na aikin hada cibiyar da cibiyar sadarwa ta kasa, yayin da aikin bayar da agajin gaggawa ya kai matakin kamala na kashi 85 cikin 100.

“Daga abin da muka gani a yanzu, za mu iya cewa tsarin da ke gudana zai iya kai ga kammalluwar ayyukan.

“ Kuma, za a fara gyaran dukkan sauran wuraren ban ruwa nan ba da jimawa ba, kuma cibiyar za ta fara aiki gadan-gadan nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa.

“Don haka, za a fara aiki da dukkan fadin hecta 12,000 na fili da muka yi niyyar samarwa,” in ji shi.

Alhaji Dauda Ademola, shugaban kungiyar manoman aikin noman rani ta Ogun ta tsakiya, Iseyin, ya yabawa gwamnatin Tarayya bisa gaayyukan da take gudanarwa a cibiyar.

Ademola ya bukaci gwamnati da ta kara himma wajen ganin an gaggauta kammala ayyukan da sauran kayayyakin da za su bunkasa noman rani. (NAN) (www.nannews.ng)

DAK/CHOM/MAS

===========

Chioma Ugboma da Moses Solanke ne suka gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *