NAN HAUSA

Loading

Tinubu zai tafi ƙasar Sin don ziyarar aiki

Tinubu zai tafi ƙasar Sin don ziyarar aiki

Spread the love

Ziyara
Daga Salif Atojoko
Abuja, Agusta 29, 2024 (NAN) Shugaban Kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa Beijing, Kasar Sin, a ranar Alhamis don ziyarar aikin gwamnati da ta shafi Kasa da Kasa.

Jami’in yada labarai na fadar Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale, ya bayyana cewa Tinubu zai yi aiki na ɗan lokaci a Kasar Gamayyar Larabawa (United Arab Emirates) .

Ya kara da cewa “a kasar Sin, Shugaban kasar zai gana da Shugaba Xi Jinping na Kasar Sin kuma ya yi ganawa da shugabannin kasuwancin kasar Sin a kan batun taron hadin kai tsakanin Kasar Sin da yankin Afirka.

“A cikin tawagar akwai jami’an gwamnatin tarayya tare da wasu muhimman mutane da su ka marawa Shugaba Tinubu baya a tafiyar.” (NAN)(www.nannews.ng)

SA/BRM
=======
Bashir Rabe Mani ne ya buga


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *