Tinubu yayi kira ga Super Eagles su mayar da hankali kan samun nasara a kofin Africa 

Tinubu yayi kira ga Super Eagles su mayar da hankali kan samun nasara a kofin Africa 

Spread the love

Eagles
Daga Muhyideen Jimoh
Abuja, 18 ga Nuwamba, 2025 (NAN) Shugaba Bola Tinubu ya yi yabo ga kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles bisa kokarinsu a wasan cancantar gasar cin kofin kwallon kafa na duniya a 2026 ya bukace su su mayar da hankali kan samun nasara cin kofin Africa.

Tinubu ya ce duk da rashin nasara da aka sha ranar Lahadi a hannun Jamhuriyar Dimokuradiyyar
Congo a Maroko, ‘yanwasan sun cancanci yabo.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Mista Bayo Onanuga, ya bayyana haka a wata sanarwa da aka fitar a Abuja.

Tinubu ya yi kira ga tawagar da su watsar da rashin nasarar da suka fuskanta kuma su mayar da hankali kan shirin tunkarar gasar cin kofin nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025 da aka tsara daga Disamba 2025 zuwa Janairu 2026 a Maroko.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa an fitar da Eagles daga gasar cancantar bayan wasan da ya kare 1-1 a lokacin karin lokaci, wanda aka biyo baya da rashin nasara ta 4-3 a jarrabawar buhu daga kai sai hola a hannun DR Congo.

Ya ce hakan ya zama karo na biyu da Najeriya ta kasa samun cancantar shiga gasar cin kofin duniya a jere.

Shugaban kasa ya ce duk da cewa rashin nasarar ya yi raɗadi, tawagar ta cancanci yabo bisa jajircewarsu, musamman bayan cin nasara a wasan farko na share fage da suka yi da Gabon.

Ya kara da cewa “duk da rashin sa’a da muka yi, dole ne mu yaba wa ‘yan wasa saboda kokarinsu kuma mu ci gaba da tallafa musu.

“Yanzu dole ne mu rufe dukkan gibi. masu kula da kwallon kafa, ‘yan wasa da duk wadanda abin ya shafa dole ne su koma kan tsarin aiki.

“Yanzu lokaci ne da za mu mayar da dukkan kokarinmu kan kofin kasashen Afirka. Dole ne Super Eagles su dawo da darajar da aka rasa.”

NAN ta ruwaito cewa Super Eagles sun kuskura su ci nasara a wasan karshe na AFCON, inda suka sha kashi 2-1 daga kungiyar Côte d’Ivoire a cikin gasa mai tsanani da ta bar Najeriya da kyautar azurfa bayan fafatawa mai wahala. (NAN)(www.nannews.ng)
MUYI/HA
=========
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *