NAN HAUSA

Loading

Sojoji sun ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, sun kwato makamai da alburusai a Kaduna

Sojoji sun ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, sun kwato makamai da alburusai a Kaduna

Spread the love

Sojoji sun ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, sun kwato makamai da alburusai a Kaduna

Daga Tijjani Mohammad

Sojoji

Kaduna, Sept.14, 2024 (NAN) Dakarun Sector 4 Operation Whirl Punch sun kubutar da wasu mutane 13 da aka yi garkuwa da su a wani wurin masu garkuwa da mutane a karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna.

Kwamishinan tsaron gida da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Kaduna.

Aruwan ya ce “bisa bayanin da rundunar ta samu ga gwamnatin jihar Kaduna, sojojin sun mayar da martani ga sahihan bayanan sirri na ‘yan bindigar da suka yi garkuwa da wadanda aka sace a kauyen Chigulu, karamar hukumar Kachia.”

Ya ce daga baya ne sojojin suka yi hattara domin gudanar da aikin ceto a wurin da ake zargin ‘yan bindigar na da sansani.

Ya kara da cewa “dakarun sun isa wurin inda suka tunkari ‘yan fashin.

“An yi wani kazamin fada da musayar harbin bindigu a gindin wani tsauni da ke yankin.

“An fatattaki ‘yan bindigar sun gudu zuwa cikin daji, suka kuma yi watsi da wadanda suka yi garkuwa da su.

“Jami’an tsaro sun ceto mutanen 13 da aka yi garkuwa da su, wadanda suka hada da maza shida da mata bakwai daga maboyar.”

A cewarsa, sojojin sun tarwatsa sansanin, tare da lalata kayayyaki daban-daban, kamar su tufafi da abubuwan da suka shafi kayan fada a wurin.

Ya ce “an kwato wasu kayayyaki da suka hada da bindiga AK-47 guda daya, bindugu ma su linzami guda hudu, alburusai 87 7.62mm, kananan na’urorin hasken rana guda biyar, wayoyin hannu biyar da tsabar kudi N192,220.”

Aruwan ya bayyana cewa an kai wadanda aka ceto zuwa wani sansanin soji domin duba lafiyar su, kafin a sada su da iyalansu.

Ya ce Gwamna Uba Sani ya bayyana farin cikin sa da rahoton, ya yaba da yadda rundunar ta mayar da martani cikin gaggawa, karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Najeriya/Commander Operation Whir, l Punch (OPWP), Manjo Janar Mayirenso Saraso, kuma ya taya su murnar nasarar aikin.

Ya ce gwamnan ya mika sakon fatan alheri ga wadanda aka ceto yayin da suka fatan su koma cikin iyalansu lafiya. (NAN)(www.nannews.ng)

TJ/BRM

Bashir Rabe Mani ne ya tace


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *