Shugabar wata karamar hukuma a Legas ta haramta cinikin gefen hanya

Shugabar wata karamar hukuma a Legas ta haramta cinikin gefen hanya

Spread the love

Gefen hanya

Daga Idris Olukoya

Epe (Lagos), Oktoba 23, 2025 (NAN) Shugabar karamar hukumar Epe ta jihar Legas, Ms. Surah Animashahun, ta yi gargadi da a daina yin ciniki a gefen titi a yankin, saboda hadurran da ke tattare hakan da kuma cunkoson ababen hawa.

Animashahun, ta shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Alhamis cewa, matakin ya zama dole domin inganta zirga-zirgar ababen hawa, da inganta lafiyar jama’a, da kuma maido da tsari a wuraren da jama’a ke cunkoso.

Ta ce, an kai samame ne a kan muhimman wurare kamar; Kasuwar Aiyetoro, Tsohon Garage Ijebu-Ode, Ita-Opo, Kasuwar Inuwa da sauran wuraren da aka gano a cikin al’umma.

“Yan kasuwa a wadannan yankuna sun samu koma bayan tsarin hanya da kuma hanyoyin tafiya, domin hakan  na haifar da hadari mai tsanani.

“Daga yanzu, majalisar ba za ta amince da yin cinikin gefen hanya ba, saboda hadurra da cunkoson ababen hawa,” in ji ta.

Shugaban ya ce jami’an kungiyar yaki da rashin da’a ta Kick Against Indiscipline (KAI), za su zagaya domin gudanar da ayyukan dakile cin hanci da rashawa da ake yi a kan tituna a fadin al’umma.

Animashahun, ta kuma bayyana cewa, an samu hadurra da dama a kan titin Aiyetoro, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi sakamakon tukin ganganci.

“Ba za mu iya ci gaba da jure asarar rayuka da dukiyoyi ba sakamakon rashin da’a daga mutanenmu, saboda hanyoyin mota ne, ba na kasuwanci ba,” in ji ta.

Ta bayyana cewa, karamar hukumar ta samar da wurin da ya dace a bayan kasuwar Aiyetoro domin ‘yan kasuwa su gudanar da harkokinsu lafiya ba tare da hana zirga-zirga ba.

“Mun yi isassun shirye-shirye domin ‘yan kasuwarmu su yi cinikinsu a bayan kasuwa, inda masu ababen hawa ba sa wucewa, a hukumance an kebe wurin domin yin ciniki,” inji ta.

Shugaban karamar hukumar, ta bada tabbacin cewa ana ci gaba da kokarin sake gina kasuwar Aiyetoro, wadda ta ruguje a zamanin gwamnatin tsohon gwamna Akinwunmi Ambode.

Ta kara da cewa, nan ba da dadewa ba, za a sake gina kasuwar a karkashin jagorancin Gwamna Babajide Sanwo-Olu, inda ta cigaba da cewa, tattaunawa da tsare-tsare sun yi nisa.

NAN ta ruwaito cewa, ‘yan kasuwa a wuraren da abin ya shafa kamar, Aiyetoro, Ita-Opo, Shade, Popo Oba, da Papa, an umurce su da su koma kasuwannin da gwamnati ta amince da su.

Karamar hukumar ta kara yi gargadin cewa, duk dan kasuwan da ya karya dokar zai fuskanci takunkumi a atisayen aiwatar dokar a gaba.

Animashahun ta cigaba da cewa ba wai an yi wannan shiri ne don farautar kowa ba, sai don tabbatar da tsari, da’a da kuma tsaron mazauna yankin.

Ta yi kira ga shugabannin kasuwar, da shugabannin al’umma da su wayar da kan ‘ya’yansu akan muhimmancin bin doka da oda, inda ta jaddada cewa gyare-gyaren harkokin gudanar da birane za su ci gaba da samun fifiko a karkashin gwamnatinta. (NAN)(www.nannews.ng).

 

SIO/KOLE/CHOM

========

 

Remi Koleoso/Chioma Ugboma ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *