NAN HAUSA

Loading

Najeriya ta karbi kashin farko na rigakafin cutar kyandar biri

Najeriya ta karbi kashin farko na rigakafin cutar kyandar biri

Spread the love

Najeriya ta karbi kashin farko na rigakafin cutar kyandar biri

Rigakafi
Daga Racheal Abujah
Abuja, Agusta. 31, 2024 (NAN) Kasar Amurka ta baiwa Najeriya tallafin allurar
rigakafin da kamfanin kasar Denmark, Bavarian Nordic ya samar, da manufar dakile yaduwar nau’in cutar kyandar birin ta Clade ll.

Allurar rigakafin, guda dubu 10 ya isa Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai ta Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa cutar kyandar biri cuta ce da ba ta da illa sosai, wadda kuma take yaduwa a kasar tun shekarar 2017.

Najeriya dai ta samu mutum fiye da 700 da a ke zargin sun kamu da cutar, kuma an tabbatar da kamuwar mutum fiye da 40.

A cikin karin bayanin da ta fita ranar Jumma’a, ma’aikatar kula da yaduwar cututtuka watau Nigeria Centre for Disease Control (NCDC) ta ruwaito karuwar yaduwar cutar.

Ma’aikatar tace an tabbatar da cutar a jikin mutane 48 daga kananan hukumomi guda 35 na kasar da kuma birnin tarayya, Abuja. (NAN)(www.nannews.ng)
AIR/HA
=======
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta tace


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *