Kotu ta daure wani mutum saboda laifin satar tukunya

Kotu ta daure wani mutum saboda laifin satar tukunya

Spread the love

Hukunci

 

By Funmilayo Okunade

Ado-Ekiti, Aug. 6, 2025 (NAN) Wata kotun majistare dake Ado-Ekiti, ta yankewa wani matashi mai shekaru 33, Ige Bola, hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni biyu tare da aiki mai wahala bisa samunsa da laifin satar tukunyar da darajarsu ta kai N100,000.

Yayin hukuncin, a ranar Laraba, Alkalin kotun, Mista Bankole Oluwasanmi, ya yanke wa Bola hukunci ne bayan amsa laifinsa da kuma tabbatar da gaskiyar lamarin.

Dan sanda mai shigar da kara, Sifeto Elijah Adejare, ya shaidawa kotun cewa wanda ake tuhuma, ya aikata laifin ne a ranar 31 ga watan Yuli da misalin karfe 6:30 na yamma a Ilawe-Ekiti.

Adejare ya ce, wanda ake tuhumar ya saci tukwane guda uku da kudinsu ya kai N100,000 mallakar wani mutum mai suna Adenike Temiyemi.

Ya kara da cewa, wanda ake tuhumar a yanzu ya saci tukwanen ne a Ilawe-Ekiti ya kawo ta Ado-Ekiti, inda ya kara da cewa jami’an tsaro na Agro marshal sune suka kama shi.

Mai gabatar da karar yace an kama wanda ake tuhuma a lokacin da yake daukar tukwanen, daga bisani aka mika shi ga ‘yan sanda.

Ya kara da cewa ‘yan sanda sun kwato tukwanen kuma laifin ya ci karo da sashe na 302(1) (a) na dokar laifuka ta jihar Ekiti, 2021.(NAN)( www.nannews.ng )

FOA/DCO

Edited by Aisha Ahmed


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *