Kotu ta dakatarda jam’iyyun siyasa 19 kawo cikasga zaben kananan hukimomin Kano

Kotu ta dakatarda jam’iyyun siyasa 19 kawo cikasga zaben kananan hukimomin Kano

Spread the love

Kotu ta dakatarda jam’iyyun siyasa 19 kawo cikasga zaben kananan hukimomin Kano

Zabe
By Ramatu Garba
Kano, Sept.24, 2024(NAN) Wata babbar kotun jihar Kano a ranar Talata, ta hana jam’iyyun siyasa 19 daukar duk wani mataki da zai kawo cikas ga zaben kananan hukumomin jihar da ke tafe.
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kano (KANSIEC), ta hannun Lauyanta Rilwanu Umar, ta shigar da kara a ranar 20 ga Satumba.
Kotun da ta hana wadanda ake kara kawo cikas ga harkokin zabe a kananan hukumomi 44 (LGAs).

Wadanda ake kara sun hada da Accord Party, Action Alliance, Action Democratic Party, African Democratic Congress, All Progressives Congress, Allied Peoples Movement, All Progressive Grand Alliance, Boot Party da Labour Party.

Sauran sun hada da National Rescue Movement, New Nigeria Peoples Party, Peoples Democratic Party, Peoples Redemption Party, Social Democratic Party, Young Progressive Party, Young Party da Zenith Labour Party.
Mai shari’a Sunusi Ado-Ma’aji, ya bayar da umarnin wucin gadi da ya haramta wa wadanda ake kara yin duk wani mataki da zai hana mai shigar da kara daga gudanar da aikinsa na shari’a.

Ado-Ma’aji ya dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 10 ga watan Oktoba domin sauraron karar.(NAN)(www.nannews.ng)
RG/SH

=======
Sadiya Hamza ta gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *