Hukumar NESREA ta lalata buuhunan sassan jikin jakuna 700 da Kwastam ta mika mata

Hukumar NESREA ta lalata buuhunan sassan jikin jakuna 700 da Kwastam ta mika mata

Spread the love

Jaki

Doris Esa

Abuja, Oktoba 16, 2025 (NAN) Hukumar Kula da Muhalli ta Kasa (NESREA) ta ce, ta lalata buhunan sassan jikin jakuna 700 da Hukumar Kwastam ta Najeriya ta mika mata a Kaduna.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Misis Nwamaka Ejiofor, mataimakiyar daraktar yada labarai ta NESREA ta fitar a Abuja.

Ta ce hakan ya yi daidai da ka’idojin muhalli da ka’idojin aminci.

Ejiofor ta ce, an lalata kasusuwan jakuna da fatun ne a ranar 3, 4 da 6ga watan Oktoba, a Kaduna.

“An yi amfani da wurare guda biyu don kona kasusuwan, yayin da aka binne fatun a wani wuri da aka kebe.

 “An gudanar da atisayen ne a gaban jami’an tsaro kuma bisa ka’idojin muhalli,” in ji shi.

Ta ce an samu nasarar gudanar da atisayen ne ta hanyar hadin gwiwar hukumar ta NESREA da hukumar Kwatam.

Ejiofor ta kara da cewa, sun tabbatar da cewa an yi aikin ne cikin aminci da kiyaye muhalli.

“Wannan ya nuna gagarumar nasara, a kokarin da ake na yaki da fataucin namun daji da kuma kare nau’o’in su da ke cikin hadari.

 “An gudanar da aikin ne a ƙarƙashin tsauraran ka’idojin hadin gwuiwa, don hana duk wani haɗarin muhalli ko lafiya.

“Ma’aikatun da ke cikin atisayen sun sanya kayan kariya na sirri, kuma an dauki matakan rage hadarin kamuwa da duk wata illar da za ta shafi rayuka,” in ji ta.

Ejiofor ta jaddada cewa hukumar NESREA a watan Yuli ta kona sama da buhu dari na al’aurar jakuna da hukumar kwastam ta Najeriya ta mika a Abuja.

Darakta Janar na Hukumar NESREA, Farfesa Innocent Barikor, ya koka da yadda jakuna ke raguwa a Najeriya, ya yi gargadin cewa sannu a hankali suna mutuwa.

Barikor ya jaddada tsayuwar daka da gwamnatin Najeriya ta ke yi na yaki da safarar jakuna ba bisa ka’ida ba.

Ya ce an dauki jakuna dabbobin gida, amma bukatarsu da masu safarar miyagun kwayoyi suke yi don yin maganin kara karfin sha’awa, ya sa gwamnatin tarayya ta ba da umarnin hana sayar da ita.

Barikor ya ce, lalata sassan jakunan da hukumar NESREA da NCS suka yi, an yi shi ne don hana fataucin jakunan ba bisa kaida ba.

Ya yi godiya ga hukumar ta Kwastam bisa gagarumin goyon baya ga yaki da fataucin miyagun kwayoyi da ke cikin hadari. (NAN) (www.nannews.ng)

 

Chidi Opara ya gyara ORD/CEO

Aisha Ahmed Ta fassara.


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *