Gwamnatin Tarayya, Kungiyoyin ma’aikatan Mai da kamfanin Dangote sun cimma matsaya kan rikicin matatar mai

Gwamnatin Tarayya, Kungiyoyin ma’aikatan Mai da kamfanin Dangote sun cimma matsaya kan rikicin matatar mai

Spread the love

Gwamnatin Tarayya, Kungiyoyin ma’aikatan Mai da kamfanin Dangote sun cimma matsaya kan rikicin matatar mai

Yarjejeniyar

By Joan Nwagwu

Abuja, 1 ga Oktoba, 2025 (NAN) A ranar Talata ne gwamnatin tarayya ta sasanta tsakanin kungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya (PENGASSAN) da mahukuntan matatar man Dangote.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar da ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Dr Muhammad Maigari-Dingyadi ya fitar tare da sanya wa hannu a karshen taron sulhu na kwanaki biyu da aka gabatar wa manema labarai ranar Laraba a Abuja.

Taron wanda ya gudana a ranakun litinin da talata, ya tattaro mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, ministocin kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, da kuma ma’aikatar man fetur (Gas), tare da hukumar DSS, NIA, NNPC, NMDPRA, NUPRC da shugabannin kwadago.

Idan dai za a iya tunawa, an gudanar da zaman sulhun ne bayan da kungiyar PENGASSAN ta umurci mambobinta da su dakatar da samar da iskar gas tare da janye ayyukan da suke yi daga matatar.

Kungiyar ta zargi kamfanin da dakatar da daukar ma’aikata sama da 800 na mambobinta, lamarin da ya janyo daukar matakin masana’antu.

Matatar Dangote, ta bayyana cewa an kori ma’aikata ne saboda wani aikin sake fasalin da ake yi a kamfanin.

A cewar sanarwar, taron ya yanke shawarar cewa hadakar wani muhimmin hakki ne na ma’aikata a karkashin dokokin Najeriya kuma dole ne kamfanin ya mutunta shi.

An kuma amince da cewa hukumar ta Dangote Group ta gaggauta fara tura ma’aikatan da abin ya shafa zuwa wasu rassan kungiyar ba tare da an yi asarar albashi ba.

Taron ya kuma tabbatar da cewa babu wani ma’aikaci da za a ci zarafinsa saboda shiga rigimar da ke tsakanin PENGASSAN da kamfanin.

Ita kuma PENGASSAN ta amince ta fara shirin janye yajin aikin nata, yayin da bangarorin biyu suka yi alkawarin aiwatar da kudurorin cikin aminci.(NAN)(www.nannews.ng)

JAN/BRM

=========

Edited by Bashir Rabe Mani

 

 


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *