Gwamna Radda ya bada sanarwar ranar Talata da karfe 2 na rana don jana’izar Buhari a Daura

Gwamna Radda ya bada sanarwar ranar Talata da karfe 2 na rana don jana’izar Buhari a Daura

Spread the love

Gwamna Radda ya sanar yau Talata da karfe 2 na rana don jana’izar Buhari a Daura

Jana’iza
Daga Abbas Bamalli
Katsina, Yuli 15, 2025 (NAN) Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ya sanar da ranar Talata,
15 ga Yuli, 2025,
domin jana’izar marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a mahaifarsa, Daura.

Gwamnan ya tabbatar da haka a Katsina a ranar Litinin yayin da yake zantawa da manema labarai a gidan gwamnati,
dangane da yadda za’a yi jana’izan aka binne shi.

Buhari yana da shekaru 82 a duniya, ya rasu ne a ranar Lahadin da ta gabata a wani asibitin Landan inda yake jinya,
tun da farko ya tafi neman duba lafiyarsa a cikin watan Afrilu.

Ya yi shugabancin Najeriya daga 2015 zuwa 2023, bayan ya yi fice a aikin soja, ciki har da takaitaccen lokaci a matsayin shugaban kasa daga 1983 zuwa 1985.

Ya rasu ya bar matarsa Hajiya A’isha Buhari da ‘ya’ya takwas. Gwamnan jihar Katsina ya bayyana cewa an dauki matakin binne ne bayan tattaunawa da iyalai da sauran wadanda abin ya shafa a Landan.

Ya ce a ranar Talata  yau ne ake sa ran gawar tsohon shugaban kasar ta isa Katsina, yayin da za a yi jana’izar da misalin karfe biyu na rana.

Radda yayi addu’ar Allah ya sakawa tsohon shugaban kasar da Aljannar Firdaus.(NAN)(www.nannews.ng)
AABS/HA

========

Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *