Shafin Labarai

Shugaban NIA yayi murabus

Shugaban NIA yayi murabus

Murabus

Daga Salif Atojoko

Abuja, August. 25, 2024 (NAN) Mista Ahmed Abubakar, Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), ya mika takardar murabus dinsa ga Shugaba Bola Tinubu a ranar Asabar.

Abubakar ya mika takardar murabus dinsa ga shugaban kasa, bayan wani taron tattaunawa da aka saba yi wanda ya samu karbuwa.

Shugaban Hukumar NIA, wanda yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa, ya nuna godiya ga shugaban kasar bisa damar da ya ba Najeriya na tsawon watanni 15, gata da ba kasafai ba.

“Na sami karramawa na yi wa Shugabanni biyu hidima a jere. Na gode masa da damar da ya bani,” inji shi.

Abubakar ya bayyana dalilansa na kashin kansa na yin murabus din, inda ya ki yin karin bayani, domin hakan zai zama saba ka’ida.

Ya bayyana cewa mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA) da shugaban kasa zasu bayyana dalilan yin murabus idan ya cancanta.

Abubakar ya bayyana jin dadinsa da jajircewar shugaban kasa, da kwarin gwiwa, da kuma kwarin guiwar hidimar sa.

Ya bayyana damar da aka ba wa jami’ai da ma’aikata a tsawon shekaru bakwai da ya yi a matsayin Darakta Janar, yana mai cewa, “Wannan wani muhimmin ci gaba ne a gare ni, kuma ina godiya da gogewar da aka samu.”

(NAN) (www.nannews.ng)

SA/AMM

======

Abiemwense Moru ce ta tace

Gwamnatin Borno za ta rufe makabartu biyu saboda da cunkoso

Gwamnatin Borno za ta rufe makabartu biyu saboda cunkoso

Makabarta
Daga Nabilu Balarabe
Damaturu, Aug 24, 2024 (NAN) Gwamnatin Jahar Borno ta ce a ranar 1 ga Satumba za ta rufe manyan makabartu biyu da suka cika a Birnin Maiduguri don guje wa barkewar annoba.

Makabartun sun hada da Makabartar Musulmai ta Gwange ta da ke Hanyar Bama da Makabartar Kirista da ke tsohuwar GRA.

Wannan na kunshe a cikin wata sanarwa da ke dauke da sa hannun Alhaji Mohammed Abubakar, Babban Sakataren Hukumar Harkokin Addinai ta jihar a ranar Jumma’a a Maiduduguri.

Ya ce gwamnatin ta samar da sabbin makabartu biyu da suka hada da Makabartar Dalori ta kan Hanyar Bama ga Musulmai, da kuma Makabartar alumar Kirista Mai Matsanancin Tsaro da ke kan Hanyar Baga.

Abubakar ya ce samar da sabbin makabartun ya biyo bayan bukatar yin hakan da ga alummai daba daban na jihar.

Babban Sakataren ya kara da cewa gwamnati za ta ci gaba da bude sabbin makabartu a fadin jihar a duk inda akwai bukatar yin hakan.

Ya ce tuni gwamnatin ta sayo motocin guda shida da za ta bayar da su ga alumar Musulmi da na kirista don daukan gawawwaki.(www.nannews.ng)(NAN)NB

Rubutawa: Nabilu Balarabe

An ceto daliban likitanci 20 da akayi garkuwa da su

An ceto daliban likitanci 20 da akayi garkuwa da su

Ceto
Daga Emmanuel Anstwen
Makurdi, Aug 24, 2024 (NAN) Hukumar Yan Sanda a jihar Benue ta tabbatar da sakin daliban jamio’in Maiduguri da Jos da aka sace a jihar da ke Arewa Maso Tsakia a ranar 15 ga Augusta.

Jamiin Yada Labaru na Yan sandan, Mista Sewuese Anene, ne ya tabbatar sakin daliban wa kampanin Dillancin Labarun Nageria (NAN) a Makurdi ranar Jumma’a.

Kamfanin Dillacin Labarai Na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa daliban an sace su ne a garin Oturkpo yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Enugu don taron shekara-da-shekara na gamayyar daliban likitanci na katolica ( FECAMDS).

Rahoton ya kara da cewa wani jamiin kiwon lafiya da ke tare da daliban shima an sace shi.

Sai dai Anene bai bada Karin haske ga ceton daliban da akayi ba.

“ An sako wadanda aka kama. Za‘a bada karin bayani a gobe ( Azabtar) da safe,” ya ce.

Sako daliban na zuwa ne kwana biyar bayan Shugaban Yansandan Nigeria, Mista Olukayode Egbetokun, ya turo zaratan Yansanda zuwa Benue, ya kuma ba wa Shugaban Yansandan jihar umurnin ya ta fi Oturkpo.

NAN ta gano cewa wata hadakar jamian tsaro bisa jagorancin Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara Akan Harkokin Tsaro ne ta ceto daliban.(www.nannews.ng)(NAN)AEB/ETS
Fassara daga Nabilu Balarabe

 

 

 

 

 

 

Yan kasuwa sunyi alwashin bada gudumawa wajen bunkasar tattalin arzikin Afrika

picture of maize

Yan kasuwa sunyi alwashin bada gudumawa wajen bunkasar tattalin arzikin Afrika

Kasuwanci

Daga Aderogba George

Abuja, Aug. 24, 2024 (NAN) Taron shugabannin kasuwanci da zuba jari na Afrika (ABLIS) 2024 da aka shirya gudanar wa a birnin Kigali na kasar Rwanda, ya ce taron zai ba da gudunmawa sosai wajen mayar da Afirka ta zama cibiyar kasuwanci ta duniya.

 

Shugaban ABLIS, Shirley Hills, ce ta bayyana haka a taron dabarun hadin gwiwar da aka yi a Abuja ranar Alhamis, cewa taron zai gudana a tsakanin 7 ga Oktoba zuwa 12 ga Oktoba.

Hills ta ce shirin na kwanaki shida zai mayar da hankali ne kan inganta gasa tsakanin ‘yan kasuwa a Afirka.

A cewar ta, taron zai samar da wani tsari na inganta harkokin kasuwanci a Afirka da hadin gwiwar tattalin arziki da ba a taba yin irinsa ba a Afirka, da kuma yadda za a bunkasa tattalin arzikin nahiyar.

Ta ce taron zai ba da dama ga shugabannin ‘yan kasuwa na Afirka su ba da labarin yadda suke tafiyar da harkokin kasuwanci da wadata.

“Taron zai yi tasiri a kan shugabannin siyasar nahiyar musamman kan yadda za su bunkasa hanyoyin samun ci gaban tattalin arzikin kasar su (GDP), da kuma bunkasa tattalin arzikin Afirka.

“Taron da ke tafe zai nuna mahimmancin himma tare da jaddada bukatar ‘yan kasuwan Afirka su rungumi kyawawan dabi’u a duniya tare da bunkasa kasuwancin tsakanin nahiyoyi.

“Muna kawo sauye-sauyen harkokin kasuwanci a duniya da hadewar kasashen Afirka saboda muna son ‘yan Afirka su yi kasuwanci da ‘yan Afirka don Afirka.

“Yana da matukar muhimmanci mu sanya tsarin sauye-sauyen harkokin kasuwanci a duniya, da tabbatar da cewa kasuwancin Afirka sun samar da ingantattun ayyuka na duniya,” hills ta kara da cewa.

Ta kuma yi kira ga Najeriya da ta yi amfani da tsarin da taron ya samar, inda ta kara da cewa kasar na da tarin ribar da za ta samu daga taron.

Mista Paul Abbey, abokin huldar dabarun ABLIS, ya ce kamata ya yi Najeriya ta yi amfani da damar taron don tallata arzikinta na albarkatun kasa,.

“Tabbas ta hanyar hadin gwiwa da kuma bayyana irin karfin da Najeriya ke da shi, nahiyar za ta ci moriyarta, ita ma Nijeriya za ta amfana, muna da albarkatun kasa da yawa da ya kamata a yi kasuwa a can.

“ABLIS yana shirye don ƙirƙirar dandamali don bayyani; ‘Yan kasuwa da yawa za su san cewa Najeriya na da albarkatun kasa; za su hada kai da gwamnati don kara inganta kasuwancin kasa da kasa,” in ji shi.

Mista Obinna Simon, wani abokin hadin gwiwa, ya jaddada bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen Afirka, don bunkasa karfin kasuwancin su, yana mai cewa, babu wata kasa da za ta iya tsayawa kanta.

Ya ce hadin gwiwar ya ba da dama ga kasashe su shiga harkokin kasuwanci na wasu kasashe, yana mai cewa yana taimakawa wajen musayar ra’ayi.

“Hadin gwiwar wani mataki ne na ci gaban kasa, zai samar da damammaki masu yawa ga matasa, kere-kere da damar saka hannun jari”, in ji Simon. (NAN)(nannews.ng)

AG/KUA

======

 

Uche Anunne ne ya gyara

 

Fassarawa: Abdullahi Mohammed

Tinubu ya rantsar da Kekere-Ekun a matsayin babbar me Shari’a ta Najeriya 

Labarai da dumi dumi: Tinubu ya rantsar da Kekere-Ekun a matsayin babbar me Shari’a ta Najeriya

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya rantsar da me Shari’a Kudirat Kekere-Ekun a matsayin Alkaliya ta 23 kuma mace ta biyu da aka bawa mikamin babbar Alkaliya ta Najeriya, a matsayin rikon kwarya kafin tabbatar mata da kujerar.

Ta karbi mukamin ne daga me Shari’a Olukayode Ariwoola,wanda yayi murabus ranar Alhamis, 22 ga watan Agusta yana da shekaru 70.(NAN) (www.nannews.ng)

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed

 

 

 

Matawalle ya bukaci shugaban hafsoshin Najeriya ya gaggauta kamo ma kisan Sarkin Gobir 

Matawalle ya bukaci shugaban hafsoshin Najeriya ya gaggauta kamo ma kisan Sarkin Gobir

 

 

Kisa

Daga Deborah Coker

Abuja, Aug. 23, 2024 (NAN) Dakta Bello Matawalle, Karamin Ministan Tsaron Najeriya, ya bukaci shugaban rundunar hafsoshin sojojin Najeriya, Janar Christopher Musa, da ya gaggauta kamo waɗanda suka kashe Sarkin Gobir na Gatawa a Jahar Sakkwato, Alhaji Isa Bawa.

 

Matawalle ya bada umarnin ne a wata sanarwa da jami’in yada labarai da ke Ma’aikatar Tsaron Najeriya, kuma  Mista Henshaw Ogubike, ya fitar a ranar Juma’a a Abuja.

 

A cewar sa, ministan wanda yayi Allah wadai da kisan gillar da yan bindigar suka yiwa sarkin Gobir din ya jadadda cewa gwamnati ba zata taba aminta da wannan ta’addanci ba.

 

“Kisan Bawa rashin tunanin ne, kuma ta’addanci ne da ba za’a amunce da shi ba. Zamuyi bakin kokarin mu da tabbatar da hukunta waɗanda suka aikata laifin.

 

“A dalilin hakan ne ya zama dole shugaban hafsoshin sojojin Najeriya ya gaggauta kaddamar da nadin masu binciken wannan aika aikar a kuma tabbatar da cewa an gurfanar da su a gaban kotu.

 

“Tsaro na gaba gaba cikin kudirin gwamnatin shugaban Najeriya, Bola Tinubu, wanda kuma ya bai wa rundunar sojojin Najeriya cikakken gooan baya,” a cewar ministan.

 

Matawalle ya kuma tabbatar wa da al’ummar Najeriya cewa babu shakka Rundunar Sojojin Kasar Najeriya ba zasu bar baya da kura ba wajen zakulo waɗanda suka aikata wannan mummunar ta’addancin dan ganin an hukunta su a bisa tsarin dokokin kasa.

 

“Zamu ci gaba da aiki batare da gajiya ba dan tabbatar da tsaro da kwanciyar hankalin al’ummar Najeriya,” a cewar jawabin ministan.

 

Matawalle ya kuma mika ta’aziyarsa zuwa ga iyalan marigayi me martaba Sarkin Gobir tare da dukan al’ummar Gatawa, da na jahar Sakkwato baki daya da kuma gwamnatin jahar.

 

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya yayi rahoton cewa an sace Sarkin ne da daya daga cikin ya’yan sa a lokacin da suke kan hanyar su ta kowowa gida daga Sakkwato yau kwana 26 dai dai tsakanin sace she da kisan gillar da waɗanda suka sace shi suka yi masa.

(NAN)(www.nannews.ng)

 

DCO/SH

========

 

edita by Sadiya Hamza

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Yadda mace yar shekara 40 ta sawa kanta wuta a Jigawa 

Yadda mace yar shekara 40 ta sawa kanta wuta a Jigawa

 

 

 

Kuna

Daga Muhammad Nasir Bashir

 

Dutse, Aug. 23, 2024 (NAN) Wata mace me shekaru 40 a Karamar Hukumar Guri dake Jahar Jigawa ta bankadawa kanta wuta sanadiyar bakin cikin sakin da mujin ta ya yi mata.

 

Jami’i mai magana da miryan rundunar yan sandan jahar, DSP Lawan Shiisu ne ya tabbatar da mummunan labarin a wani jawabi da ya fitar a ranar Juma’a.

 

A cewar Shiisu, macen dake zama a kauyen Malam, ta yi amfani da man fetur wajen sawa kanta wuta.

 

“A ranar Alhamis misalin 7: 40 na safe ne hukumar yan sandar ta samu mummunan labarin me ban tausayi daga karamar hukumar Guri, cewa mace yar shekaru 40 a kauyan Malam ta kuza man fetur a jikinta da kanta a wajen gari, sanadiyar hakan ta samu mummunar kuna.

 

“Take da samun bayanin, kwararrun yan sanda dake hedikwatar ofishin Guri suka bazama zuwa inda hadarin ya faru.

 

“Jami’an yan sandan sun dauki gawar macen dake kone zuwa asibiti daga bisani kuma suka mika ta zuwa wajen iyalan  ta domin yi mata sutura,” cewar Shiisu.

 

Mai magana da miryan yan sanda ya kara da cewa hukumar ta su take ta fara bincike dan gano gaskiyar lamarin, du da an san marigayiyar ta shiga mummunan yanayin bakin ciki da damuwa a watannin baya, sanadiyar mutuwar auren ta.

 

Ya kara da cewa Kwamishinan yan sanda na Jahar Jigawa, Ahmadu Abdullahi, ya shawarci Jama’a da su rika mika lamuransu ga ubangiji dan samun mafita.

 

Abdullahi ya jaddada shawaran da cewa mutane su kuma rika neman shawaran magabata a cikin yanayin kunci do damuwa  domin gujewa fadawa yin aika aika.

(NAN) (www.nannews.ng)

 

MNB/SH

 

=======

 

edita Sadiya Hamza

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Tinubu da Abdulsalam sun kalubalanchi shashen shari’a da samar da adalchi ga kowa 

Tinubu da Abdulsalam sun kalubalanchi shashen shari’a da samar da adalchi ga kowa

Shari’a
By Taye Agbaje
Abuja, Aug.22,2024(NAN) Shugaban Kasa Bola Tinubu a ranar Alhamis yayi kira ga mambobin shashem Shari’a da su jajirce a wajen yin ayyukan su na tabbatar da adalchi ga kowa.
Tinubu yayi magana a wurin kaddamar da wani littafin tarihi kan tsohon Babban Alkalin Alkalan Najeria, Mai Shari’a Olukayode Ariwoola mai ritaya.
Kamfanin Dillanchin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Mai Shari’a Kudirat Kekere-Edun ke zata maye gurbin Ariwoola a yau Juma’at.
Ariwoola yayi ritaya ne a ranar 22 ga watan Agusta bayan ya cimma shekaru 70 da haihuwa Kamar yadda dokar kasa ta samar.
Maitamakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya wakilchi Tinubu a wurin taron mai cike da tarihi.
Shugaban kasar yayi kira ga maakatan shashem shari’a da kada suyi kasa guiwa domin domin tunanin wadansu yan masu ganin cewa sashen shariar bai yin aiki yadda ya kamata madamar dai baa yi masu abunda suke so ba.
Timibu ya kuma jinjina ma shashen shariar kan wadansu hukunche hukunche da suka yanke kamar irin wanda suka zartas kwanan nan kan yancin cin gashin kai na kananan hukumomin Najeriya.
Ya yaba wa Ariwoola kan chanje chanje da ya samar a sashen sharia wadanda suka kara inganta samar da adalchi ga yan kasa.
Tinubu ya kuma nuna jin dadin sa ga wannan ci gaban ya kuma yi fatar cewa wadda zata gaje shi zata dore da wadannan chanje chanjen.
Tinubu Kuma ya kara jinjina ma Ariwoola yana mai jinjina masa kan dogewar sa da zurfin tunani wanda ya kara taimakawa wurin samar da adalchi ga yan kasa.
Shi ma tsohon shugaban kasar Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar, wanda shine shugaban taron, yayi kira ga Alkalai da su tabbatar da samar da adalchi ga kowa.
Yace ya kamata su yi hakan ba tare da nuna bambanchin yare, adding ko siyasa ba.
Abubakar ya kuma yaba wa Ariwoola kan dunbin nasarorin da ya samu a cikin shekarun biyu da ya jagoranchi shahen shariar kasar nan.
Ya kuma yi kira ga yan Najeriya da su kwaikwayi kyawawan halaye na Ariwoola wajen nuna gaskiya da daidaito a dukkan harkokin su.
Shima Shugaban Kotun Maikata ta Kasa watau Industrial Court, Mai Shari’a Benedict Kanyip yace littafin wani kundi tarihi ne da kowa ya kamata ya karanta.
Ita ma wadda zata gaji Ariwoola , Kekere-Ekun ta jinjina Wanda zata gadar da cewa shi gwarzo ne kuma mai dinbin kamala.
Shima babban Sarki, Ooni na Ife, Oba Adeyeye Ogunwusi, Ojaja 11, ya ce Ariwoola ya bar misalai na kwarai da za’a yi kwaikwaya a shashen shari’ar Najeriya. ( NAN) (www.nannews.ng)
TOA/SH
===============
Edited by Sadiya Hamza
Tace wa : Bashir Rabe Mani

Hukumar zaɓen Malawi ta kudiri yin zaɓen 2025 da sabun na’urar kimiya 

Hukumar zaɓen Malawi ta kudiri yin zaɓen 2025 da sabun na’urar kimiya

 

Zaɓe

Lilongwe, Aug. 22, 2024 (Xinhua/NAN) Hukumar zaɓen kasara Malawi (MEC) ta aje sabuwar na’urar kimiya (Electoral Management Devices (EMDs), wajan dai dai ta tsarikan hanyoyin babban zaɓen kasar da za’yi a watan Satumba na shekarar 2025.

 

Jami’iin da ke magana da yawun hukumar, Sangwani Mwafulirwa, ya sanar da cewa hukumar ta sayo na’urorin EMDs kimanin 6,500 daga wani kamfanin da ke zaune a kasar Netherlands me suna (Smartmatic International Holdings B.V. Company).

 

Sabuwar na’urar kimiyar zata maye gurbin na’ura me dauke da bayanan mutane na registan zaɓe wadda ake kira (Biometric Voter Registration System), wanda aka yi amfani da ita a babban zaɓen kasar na shekarar 2029, da kuma zaɓen nanata kammala zaɓen shugaban kasa.

 

Ana sa ran Kwamishinan zaɓen kasar zai yi amfani da sabuwar na’urar wajen rajistar kuri’u da tsare tsaren masu bukatar canjin wajan yin zaɓe da kuma ziyarce ziyarce duba wajen yin rajistar zaɓe.

 

Mwafulirwa yace gabatar da sabuwar na’urar MEDs na cikin tsarin dabarun hukumar MEC ta wajen bunkasa tsarin hanyoyin gudanar da babban zaɓen kasar.

 

(Xinhua/NAN)(www.nannews.ng)

UMD/HA

========

Editoci sune

Ummul Idris/Hadiza Mohammed-Aliyu

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista 

 

 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista

 

Asara

 

Daga Doris Esa

 

Abuja, Aug. 22, 2024 (NAN) Gwamnatin Tarayyan Najeriya tace manoman chitta a kasar sun yi asarar kudi kimanin biliyan N12 a sanadiyar annobar chutar chitta da ta afkawa gonaki a 2023.

 

Sanata Aliyu Abdullahi, karamin Ministan, a ma’aikatar Gona, da Tattalin Abinci, ya sanar da hakan yayin kaddamar da taron ba da hora wa masu horar wa, wanda hukumar inshora ta gona ta shirya a ranar Alhamis a Abuja.

 

Ministan ya haska kadan daga cikin matsalolin da manoman suka fuskanta a yayin noman damina na 2023, inda manoman chitta a JIhar Kaduna suka yi asara mai matukar yawa sanadiyar annobar chutar chittan.

 

Abdullahi yace manoman sun rasa kimanin kashi 90 daga cikin dari na amfanin gonarsu a noman da suka yi a daminar bara.

 

“Kadan daga cikin manoman chittan  da suka yiwa gonakin su garkuwan inshora ne suka  karbi diyya na daga asarar da suka yi sanadiyar annobar chutar chittan.

 

“Wa dannan jerin manoman za su yi alfaharin komawa gona ba tare da wani tallafin kudi dan kadan ba, kuma ba kamar yan uwansu manoman da basu yiwa gonakinsu garkuwan inshora ba, wadanda a yanzu sai sun kwashe duk abun dake cikin asusun su, dan komawar su zuwa gona.

 

“Wannan shine darasin da yazama dole akanmu; kamar yadda make a dukkan lokuta mukan samu kanmu a cikin asara sanadiyar zuwan mummunar damuna daya ko biyu, wannan be shafi karancin abinci ba,” a cewar sa.

 

Abdullahi yace alkalumman hashashe na ambaliyar ruwan sama na 2024 wanda maikatar ruwa da tsaftace muhalli ta fitar, ta hankaltar da kananan hukumomi 148 a jihohi 31 ha suke cikin barazanar ambaliyar ruwan sama a yankunan su.

 

Ya ci gaba da cewa rahotonni na watanin farkon shekara da ake ciki sunyi nuni da cewa kananan hukumomi 249 a jahohi 36 tare da birnin tarayya sun shigo cikin jerin yankuna da suke da saukin samun hadarin ambaliyar.

 

“A sauka ke, kananan hukumomi 397 daga cikin 774 a Najeriya, ko kuma kashi 51 daga cikin wajajen noma a kasar na cikin hadarin samun ambaliyar ruwan sama,” a cewar sa.

 

“Hakika muna sheda wa a bayyane a yanzu ba a wani lokaciba babbar barazanar dumamar yanayi da illar da ke tare da ita a tattare da amfanin gonakinmu na gida a tsarikanmu na kasa baki daya,” a bayanin da ya kara,” ministan ya fada.

 

Abdullahi yace tsare-tsaren na gaba gaba, na maikatar gwamnatin tarayya tare da hadinkan kamfanoni masu zaman kansu, da kuma hukumar NAIC da ta PULA, wanda sune mashawartan  kamfanin inshoran gona wanda suke gudanar da tsare tsaran National Agricultural Growth Scheme Agro-Pocket (NAGS-AP).

 

Ya kuma kara da cewa ya tabbata cewa dumamar yanayi gaskiyace ta tabbata dolene a shigar da tsarin inshora cikin harkar noma a matsayin ta ta abokiyar tafiya a cikin tsarin gwamnatin ta NASG dan tabbatar da dorewa da kuma masu buƙatar wadatar abinci sosai a kasa.

 

Ministan yace tsarin NAGS-AP wanda ya fara a 2023 yayin noman rani na alkama ya haifar da amfanin gona mai yawa. (NAN) (www.nannews.ng)

 

ORD/JPE

 

=======

 

Edita Joseph Edeh

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani