Tinubu ya taya Shettima murnar cika shekaru 59 a duniya
Tinubu ya taya Shettima murnar cika shekaru 59 a duniya
Murna
Daga Muhydeen Jimoh
Abuja, Satumba 2, 2024 (NAN) Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayyana farin cikinsa ga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, bisa cikarsa shekaru 59 a duniya, inda ya yaba da amincinsa, da hadin gwiwarsa, da kuma sadaukarwar sa wajen gina kasa Nijeriya.
A cikin wani sako na mussamman, Tinubu ya yi murnar zagayowar ranar haihuwar Shettima, inda ya kira shi amintacce abokin aiki musassamman wajen sabunta kasa.
Ya ce “yau, Satumba 2, 2025, ta ba da wata dama ta musamman don murnar ranar haihuwar ɗan’uwana, abokin tafiya kuma mataimakin
shugaban ƙasa.
“Tun da muka fara wannan tafiya, tare da hadin kai tare da hangen nesa na gina kasa mai ci gaba, jajircewarka, dagewar ka da kuma imani.da daukakar Najeriya ba su girgiza ba.
“Ina matukar godiya da irin hazaka, aminci, hadin kai, da goyon bayanka a matsayin mataimakina,” in ji Tinubu.
Shugaban ya yi tunani a kan shawarar da ya yanke na zabar Shettima a matsayin abokin takararsa, inda ya bayyana cancantarsa, jagoranci, da kuma daidaiton aikinsa.
Tinubu ya ce “a lokacin na zaɓe ka zama matsayin abokin tarayya, na zaɓi ƙwarewa da sauran halaye waɗanda Najeriya za ta dogara da su.
“Kowace rana, a matsayinka na Mataimakin Shugaban kasa, ka tabbatar da wannan zabi ta hanyar karfafa aikinmu, kawo sabbin ra’ayoyi,
da kuma tabbatar da kudurinmu ga ‘yan Najeriya.
“Kaddamar da kai ya tabbatar min da cewa ban yi kuskure ba wajen zaɓe ka a matsayin mataimaki na ba.”
Tinubu ya yaba da tafiyar siyasar Shettima daga Gwamnan Borno zuwa Sanata, inda ya yaba wa hidimar da ya yi wajen fuskantar kalubale.
“Ka yi wa al’ummar Borno hidima, jiharka ta haihuwa, da kyau a matsayin Gwamna na tsawon shekaru takwas, sannan a matsayin Sanata mai wakiltar Borno ta tsakiya a Majalisar Dokoki ta kasa.
“A dukkan ayyukan biyu, ka nuna cewa jagoranci hidima ne, ba gata ba, ko da a cikin manyan kalubale,” in ji shi.
Duba kuma WAFCON: Tinubu yayi alkawarin karrama Super Falcons Ya jaddada kudirinsu na hadin gwiwa kan Ajenda Renewed Hope, da nufin isar da ribar dimokuradiyya ga ‘yan Najeriya. Tare, mun fara aza harsashi na Sabunta Bege Agenda.
“Daga samar da sabbin kawancen duniya a fadin Tekun Atlantika zuwa inganta samar da abinci da sauye-sauyen saka hannun jari a gida, kawancen ku na da muhimmanci ga nasararmu.
“A watanni masu zuwa, yayin da muke buɗe sabbin hanyoyin kasuwanci tare da samar da ƙarin makarantu, asibitoci, da ayyukan yi, haɗin gwiwarmu zai ci gaba da samar da sakamako da ‘yan Najeriya za su iya gani da ji.
“Dole ne mu ci gaba da yin aiki don ganin an tabbatar da shirin sabunta bege, wanda zai samar da ci gaba a kasar da kuma inganta rayuwar jama’armu,” in ji shi.
Tinubu ya lura cewa dangantakar su ta wuce siyasa, wakiltar haɗin kai a yankuna da al’adu. Dangantakarmu ta zarce ayyukan hukuma, gada ce ta yankuna da al’adu, hade da manufa da hidima.
“Kuna tunatar da mu abin da zai yiwu idan Najeriya ta zo na farko, misali da ya cancanci a yi koyi da masu burin shugabanci.”
Shugaban ya yi fatan Shettima ya ci gaba da samun karfin gwiwa, hikima da shekaru masu tasiri a hidimar Najeriya. (NAN)(www.nannews.ng)
MUYI/KTO
==========
Kamal Tayo Oropo ne ya gyara