NAN HAUSA

Loading

Yadda mace yar shekara 40 ta sawa kanta wuta a Jigawa 

Yadda mace yar shekara 40 ta sawa kanta wuta a Jigawa

 

 

 

Kuna

Daga Muhammad Nasir Bashir

 

Dutse, Aug. 23, 2024 (NAN) Wata mace me shekaru 40 a Karamar Hukumar Guri dake Jahar Jigawa ta bankadawa kanta wuta sanadiyar bakin cikin sakin da mujin ta ya yi mata.

 

Jami’i mai magana da miryan rundunar yan sandan jahar, DSP Lawan Shiisu ne ya tabbatar da mummunan labarin a wani jawabi da ya fitar a ranar Juma’a.

 

A cewar Shiisu, macen dake zama a kauyen Malam, ta yi amfani da man fetur wajen sawa kanta wuta.

 

“A ranar Alhamis misalin 7: 40 na safe ne hukumar yan sandar ta samu mummunan labarin me ban tausayi daga karamar hukumar Guri, cewa mace yar shekaru 40 a kauyan Malam ta kuza man fetur a jikinta da kanta a wajen gari, sanadiyar hakan ta samu mummunar kuna.

 

“Take da samun bayanin, kwararrun yan sanda dake hedikwatar ofishin Guri suka bazama zuwa inda hadarin ya faru.

 

“Jami’an yan sandan sun dauki gawar macen dake kone zuwa asibiti daga bisani kuma suka mika ta zuwa wajen iyalan  ta domin yi mata sutura,” cewar Shiisu.

 

Mai magana da miryan yan sanda ya kara da cewa hukumar ta su take ta fara bincike dan gano gaskiyar lamarin, du da an san marigayiyar ta shiga mummunan yanayin bakin ciki da damuwa a watannin baya, sanadiyar mutuwar auren ta.

 

Ya kara da cewa Kwamishinan yan sanda na Jahar Jigawa, Ahmadu Abdullahi, ya shawarci Jama’a da su rika mika lamuransu ga ubangiji dan samun mafita.

 

Abdullahi ya jaddada shawaran da cewa mutane su kuma rika neman shawaran magabata a cikin yanayin kunci do damuwa  domin gujewa fadawa yin aika aika.

(NAN) (www.nannews.ng)

 

MNB/SH

 

=======

 

edita Sadiya Hamza

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Hukumar zaɓen Malawi ta kudiri yin zaɓen 2025 da sabun na’urar kimiya 

Hukumar zaɓen Malawi ta kudiri yin zaɓen 2025 da sabun na’urar kimiya

 

Zaɓe

Lilongwe, Aug. 22, 2024 (Xinhua/NAN) Hukumar zaɓen kasara Malawi (MEC) ta aje sabuwar na’urar kimiya (Electoral Management Devices (EMDs), wajan dai dai ta tsarikan hanyoyin babban zaɓen kasar da za’yi a watan Satumba na shekarar 2025.

 

Jami’iin da ke magana da yawun hukumar, Sangwani Mwafulirwa, ya sanar da cewa hukumar ta sayo na’urorin EMDs kimanin 6,500 daga wani kamfanin da ke zaune a kasar Netherlands me suna (Smartmatic International Holdings B.V. Company).

 

Sabuwar na’urar kimiyar zata maye gurbin na’ura me dauke da bayanan mutane na registan zaɓe wadda ake kira (Biometric Voter Registration System), wanda aka yi amfani da ita a babban zaɓen kasar na shekarar 2029, da kuma zaɓen nanata kammala zaɓen shugaban kasa.

 

Ana sa ran Kwamishinan zaɓen kasar zai yi amfani da sabuwar na’urar wajen rajistar kuri’u da tsare tsaren masu bukatar canjin wajan yin zaɓe da kuma ziyarce ziyarce duba wajen yin rajistar zaɓe.

 

Mwafulirwa yace gabatar da sabuwar na’urar MEDs na cikin tsarin dabarun hukumar MEC ta wajen bunkasa tsarin hanyoyin gudanar da babban zaɓen kasar.

 

(Xinhua/NAN)(www.nannews.ng)

UMD/HA

========

Editoci sune

Ummul Idris/Hadiza Mohammed-Aliyu

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista 

 

 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista

 

Asara

 

Daga Doris Esa

 

Abuja, Aug. 22, 2024 (NAN) Gwamnatin Tarayyan Najeriya tace manoman chitta a kasar sun yi asarar kudi kimanin biliyan N12 a sanadiyar annobar chutar chitta da ta afkawa gonaki a 2023.

 

Sanata Aliyu Abdullahi, karamin Ministan, a ma’aikatar Gona, da Tattalin Abinci, ya sanar da hakan yayin kaddamar da taron ba da hora wa masu horar wa, wanda hukumar inshora ta gona ta shirya a ranar Alhamis a Abuja.

 

Ministan ya haska kadan daga cikin matsalolin da manoman suka fuskanta a yayin noman damina na 2023, inda manoman chitta a JIhar Kaduna suka yi asara mai matukar yawa sanadiyar annobar chutar chittan.

 

Abdullahi yace manoman sun rasa kimanin kashi 90 daga cikin dari na amfanin gonarsu a noman da suka yi a daminar bara.

 

“Kadan daga cikin manoman chittan  da suka yiwa gonakin su garkuwan inshora ne suka  karbi diyya na daga asarar da suka yi sanadiyar annobar chutar chittan.

 

“Wa dannan jerin manoman za su yi alfaharin komawa gona ba tare da wani tallafin kudi dan kadan ba, kuma ba kamar yan uwansu manoman da basu yiwa gonakinsu garkuwan inshora ba, wadanda a yanzu sai sun kwashe duk abun dake cikin asusun su, dan komawar su zuwa gona.

 

“Wannan shine darasin da yazama dole akanmu; kamar yadda make a dukkan lokuta mukan samu kanmu a cikin asara sanadiyar zuwan mummunar damuna daya ko biyu, wannan be shafi karancin abinci ba,” a cewar sa.

 

Abdullahi yace alkalumman hashashe na ambaliyar ruwan sama na 2024 wanda maikatar ruwa da tsaftace muhalli ta fitar, ta hankaltar da kananan hukumomi 148 a jihohi 31 ha suke cikin barazanar ambaliyar ruwan sama a yankunan su.

 

Ya ci gaba da cewa rahotonni na watanin farkon shekara da ake ciki sunyi nuni da cewa kananan hukumomi 249 a jahohi 36 tare da birnin tarayya sun shigo cikin jerin yankuna da suke da saukin samun hadarin ambaliyar.

 

“A sauka ke, kananan hukumomi 397 daga cikin 774 a Najeriya, ko kuma kashi 51 daga cikin wajajen noma a kasar na cikin hadarin samun ambaliyar ruwan sama,” a cewar sa.

 

“Hakika muna sheda wa a bayyane a yanzu ba a wani lokaciba babbar barazanar dumamar yanayi da illar da ke tare da ita a tattare da amfanin gonakinmu na gida a tsarikanmu na kasa baki daya,” a bayanin da ya kara,” ministan ya fada.

 

Abdullahi yace tsare-tsaren na gaba gaba, na maikatar gwamnatin tarayya tare da hadinkan kamfanoni masu zaman kansu, da kuma hukumar NAIC da ta PULA, wanda sune mashawartan  kamfanin inshoran gona wanda suke gudanar da tsare tsaran National Agricultural Growth Scheme Agro-Pocket (NAGS-AP).

 

Ya kuma kara da cewa ya tabbata cewa dumamar yanayi gaskiyace ta tabbata dolene a shigar da tsarin inshora cikin harkar noma a matsayin ta ta abokiyar tafiya a cikin tsarin gwamnatin ta NASG dan tabbatar da dorewa da kuma masu buƙatar wadatar abinci sosai a kasa.

 

Ministan yace tsarin NAGS-AP wanda ya fara a 2023 yayin noman rani na alkama ya haifar da amfanin gona mai yawa. (NAN) (www.nannews.ng)

 

ORD/JPE

 

=======

 

Edita Joseph Edeh

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

Tsohon mai magana da miryan yan sanda na neman taimakon N25m na dashin koda 

 

 

Tsohon mai magana da miryan yan sanda na neman taimakon N25m na dashin koda

 

Koda

Daga Moses Omorogieva

Lagos, Aug. 22, 2024 (NAN)Tsohon mai magana da miryan yan sanda na rundunar Jahar Legas, kuma matemakin Kwamishinan Yan sanda, Chike Oti, wanda yake fama da chutar koda, yayi kira da yan Najeriya da su temaka masa da gudunmawar kudi Naira milyan N25 dan yin dashin koda.

 

Bayani ya fito ne a wata sanarwa da Oti ya fitar wacce yamika wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a ranar Alhamis a birnin  Legas.

 

A cewar majinyacin, binciken da akayi masa a dan tsakanin nan, ya tabbatar da yana dauke da cutar kodar a matakin hawa na biyar mafi hadari.

 

“Ya ku yan u wanna mazanku da matanku, sunana matemakin kwamishinan yansanda Chike Godwin Oti, wanda akayimin canjin wajan aiki zuwa rundunar yansanda dake kula da harkokin jiragan kasa hedikwatar ta dame Ebutte Meta a jahar Legas,” a cewar.

 

“Inna so na sanar daku cewa anyi min gwajin cutar koda me matakin hawa nabiyar (kidney failure) mafi hadari, wanda ake masa suna da cewa matakin karshen cutar koda.

”Ya kuma zamo da nau’iin hawan jini mafi hadari a asibitin Lagoon dake unguwar Lagoon Bourdillion na Ikoyi, dake birnin Legas.

 

“Shawarwarin kwararru shine yin wankin koda na (hemodialysis) so biyu a mako shine kadai dama ta na kasancewa a raye kafin samun kuɗin dashin kodar da ake neman miliyan N25.

 

“A karin kaina kawo yanzu na kashe kuɗin da kimaninsu yakai miliyan 3.5 acikin mako daya da na kwanta a wannan asibitin.

 

“A dadin kuɗin da zai sa na kasance a raye a wuce samu na nesa ba kusa ba. A nan ne nake mika kokon bara na zuwa ga yan uwana maza da mata da samun ganin cin nasara wajen yakar wannan cutar,” cewar Oti.

 

Ya yi bayanin cewar me san ya temakesa na iya aikawa da kudi ta  asusun ajiya kamar haka:

 

Acct. No: 2016631487, Bank: UBA PLC, Name: CHIKE OTI, Phone No: 07065246927. (NAN) (www.nannews.ng)

MIO/CHOM/IKU/

=============

Editoci sune:

Chioma Ugboma/Tayo Ikujuni

 

Fassara daga

Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

 

 

 

 

Sabon wajen gwajegwan chututtuka zai fadada karfin sa na gwajin tarin fuika a Najeriya

 

Sabon wajen gwajegwan chututtuka zai fadada karfin sa na gwajin tarin fuika a Najeriya

 

 

Gwaji

Daga Wakiliyar mu  –Deborah Coker

Abuja, Aug. 22, 2024 (NAN) Col. Eli Lozano, Kwamandan Chibiyar Nazarin Binchike mai suna Walter Reed, ta Rundunar Sojan Amurka ya bayyana cewa sabon wajen gwajegwajan chutattukasu dake barikin sojan Najeriya na Mogadishu, A Birnin Abuja zai fadada karfinsa na gwajin tarin fuka.

 

Lozano ya bayyana hakan ne yayin kadamar da sabon wajen gwajegwan chutattukan A Birnin Tarayyan Najeriya dake Abuja A ranar Talata.

 

“Wannan na’urar gwajin tarin fuka da kuke gani, zata fadada karfin Najeriya wajan gwajegwan ciwon, wanda hakan zai inganta gano chutar wajan sauki a chikin kasarku mai ban sha’awa,” A chewar sa.

 

Kwamandan Ya kara da cewa kaddamar da wannann na’urar gwajin, na nuni d juriya Da Jajarcewa Da Himma, Da Hukumar Tsaron Najeriya Ta Bangaran Gudanar Da Tsarin Lafiya Da Chibiyar Nazarin Binchike, Walter Reed, Ta Rundunar Sojan Amurka, Sukayi.

 

“Hakika am’martani da bani Hazikai Kuma Gwarazan Shuwaga banin Soja Dana Farar Hula, A nan Dan Gudanar da mahimmancin wannan lamarin.

 

“Rundunar Sojan Amurka Nada dogon tarihin lamarir’rikan starin kiwan lafiya a Kasashen ketare.

 

“Dalilin Hakan ya jawomana karin Fadada Aikinmu tagefan kare lafiya da samun wal-wala na maikatanmu dake karkadhin Rundunar Sojan Amurka tare da Jimlar Rundunar Sojojin Kasar, Dan tabbatar da zama a cikin sherin ko takwana, Akowane lokaci A kan Iya turasu Ko Ina A Duniya Wajan kare martabar kasar Amurka.

 

“Chibiyar Nazarin Binchike, Ta Rundunar Sojan Amurka, (Walter Reed Army Institute)

Nayin ayyuka, a mastayin shugaban duniya wajan nazari, da kiyaye da magance chutuka da suka hada da malaria, da HIV cuta mai karya garkuwan jiki, da Ebola da Tarin Fika.

 

“A wannan Chibiyar Ta Walter Reed Army Institute of Research, Jajartan masananmu na ilimin kimiya sun fahimci cewa kariyar lafiya itace duniya lafiya.

 

“Yau shekaru 131, sojojinmu na Chibiyar Walter Reed da ma’aikatanmu na farar Hula, sunyi aiki tukuru batare dagajiyaba Dan gwaji da Fadada fitar da kayayyakin zasu rage illar Chutattukan da ake kamuwa dasu tahanyar saduwa damakamansu.

 

“Iyalinmu na Walter Reed a cike suke da farincikin cigaba da wannan kyakyawar a’laka da mutanen Najeriya a cikin wannan mahimman Bangaran Gudanar Da binciken Chutattukan da ake kamuwa dasu tahanyar saduwa da makamantansu.

 

“Mu da ku zama tabbatar da kiwan lafiya da wal-wala a Najeriya, tare da sojojin masu mutunci dama dukkan yan Adam.”

 

Dafarko, acikin takay tataccen bayaninsa, Birgediya Janar Nathan Okeji mai murabus, Babban Daracta, a Maikatar Tsaron Najeriya Bangaran Gudanar Da Tsarin Lafiya

Ministry of Defence Health Implementation Programme (MODHIP), a cewar sa Chibiyar Nazarin Binchike Ta Sojan Najeriya an kafatane a 2012 tare da Chibiyar Nazarin Binchiken Ta Amurka, Walter Reed Army Institute of Research Africa a 2005.

 

Okay yace dangantakar ankafatane musanman dan samarda waraka ga masu chutar HIV daga cikin sojoji da iyalansu da kuma ma’ikatan farar hula dake zaune dasu dama al-uman dake makokantaka da su.

 

“Bayan lokaci mai yawa dangantaka ta dada fadada ta hanyar bada agaji wajan cutar malaria da tarin fuka da ma binchike mai zurfi.

 

“Tarin fuka ya zamo chutar da masu HIV/AIDS cuta mai kashe garkuwan jiki suke dauke da ita, tana kuma saurin kashe majinyata in har ba’a gano ta ba da wuri ba dan fara kula da majinyata.

 

“Idan tarin fuka bai samu kula da kyau ba, magungunta na bijire inganchin amfani ga majinyata. Tarin fuka ya bayyana

mahimmancin kiwan lafiya a kan cutar,” a cewar sa.

 

Babban Daracta MODHIP din ya bayyana cewa alkalumma daga hukumar kula da lafiyar jama’a ta duniya (WHO), sun nuna cewa kasashe takwas na da mafi rinjaye na masu da daukar cutar tarin fuka da kashi uku daga cikin fiyar na masu cutar a duniya.

Najeriya kuma na cikin kasashe shidda daga cikin takwas din kuma kasa ta fari a Afirka da yawan kiyasi 4.4 .

 

“Kasar Jamhuriyar Kongo na biya da kaso 2.9. Wannan alkalumman na da ban tsoro, har da yake zai iya raguwa in har an hada kai  wajan na wadanda suke da alhaki akan lamarin dan ganin an gano cutar da wuri an kuma fara bada kula wa majinyata.

 

“Tara da himma da kuma kokarin Gwajegwaje tin farko na tarin fuka daga Chibiyar (Multi-Drug Resistant (MDR), aka fara gina TBML a 2018.

 

“Da wannan kaddamar da saban wajan gwajegwan chutattuka yau, muna da yakinin azazzala karfin binchiken tarin da ma kula da majinyata da kuma bada horo tarin fuka a bisa tsarin dabarun kasa akan dakile tarin na shekara ta 2021 -2025,” a cewar Okeji.

.(NAN)(www.nannews.ng)

 

DCO/SH/BRM

============

 

Edita Sadiya Hamza

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani