Ambaliyar Ruwan Maiduguri: Hukumar NEMA, Sojoji, da sauransu sun kara kaimi wajen ceto, yayin da mutane da dama suka makale

Ambaliyar Ruwan Maiduguri: Hukumar NEMA, Sojoji, da sauransu sun kara kaimi wajen ceto, yayin da mutane da dama suka makale

Spread the love

Ambaliyar Ruwan Maiduguri: Hukumar NEMA, Sojoji, da sauransu sun kara kaimi wajen ceto, yayin da mutane da dama suka makale

Ceto

By Yakubu Uba 

Maiduguri, Satumba 12, 2024 (NAN) Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) da sojoji da sauran kungiyoyi sun kara kaimi wajen ceto jama’a da dama da suka makale ko kuma suka bace, kwanaki biyu bayan ambaliyar ruwa a Maiduguri.

Mukaddashin Shugaban Hukumar NEMA na shiyyar Arewa maso Gabas, Sirajo Garba ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Maiduguri ranar Alhamis.

Ya ce an ceto wasu mutane da dama da suka makale a gidajensu a ranar Alhamis.

“Mun baza, manyan motoci da jiragen ruwa kuma sojoji suna aikin bincike da ceto mutane musamman a unguwannin Abbaganaram, Muna, da kuma gidaje 505.

“A bangaren mu a matsayin NEMA, mun ceto mutane kusan 200 tsakanin jiya da yau.

“A ranar da lamarin ya faru, an ceto sama da mutane 1,000, yayin da sama da 70,000 sun bayyana a sansanoni bakwai.”

Dangane da adadin wadanda suka mutu, Garba ya ce: “Ba za a iya tantance adadin ba a yanzu”, ya kara da cewa kawo yanzu NEMA ta bayar da jakunkuna guda hudu.

“Yayin da ruwa ke ci gaba da ja da baya, za mu iya samun wasu gawarwakin,” in ji Garba.

A halin da ake ciki, mambobin kungiyar gwamnonin Najeriya karkashin jagorancin shugabanta kuma gwamnan jihar Kwara, Alhaji Abdultahman Abdulrazak, sun isa Maiduguri domin jajantawa gwamnati da jama’ar jihar.

Sauran wadanda suka kai ziyarar sun hada da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Ganduje, da ministocin albarkatun ruwa, cikin gida, noma, da wasu ‘yan majalisar dokokin kasar. 

NAN ta ruwaito cewa Gwamna Ahmadu Fintiri a yayin ziyarar ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 50, yayin da dan majalisar wakilai Muktar Betara (APC-Borno) ya bayar da Naira miliyan 100. (NAN)

YMU/ SH

=======
Sadiya Hamza ta gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *