Al’ummar Katsina sun yi tir da ayyukan ‘yan Bola-jari

Al’ummar Katsina sun yi tir da ayyukan ‘yan Bola-jari

Spread the love

Al’ummar Katsina sun yi tir da ayyukan ‘yan Bola-jari

Masu fashi
Zubairu Idris
Katsina, Satumba 24, 2024 (NAN) Wasu mazauna jihar Katsina sun yi tir da ayyukan masu aikin Bola-Jari da ke lalata dukiyoyin jama’a don kwashe sandunan karfe da igiyoyin wutar lantarki.
Mazauna garin sun bayyana haka ne a wata tattaunawa daban-daban da suka yi da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ranar Talata a Katsina.
Sun yi nuni da cewa da misalin karfe 6:00 na safe ne irin wadannan ‘yan Bola-jarin ke fitowa daga wannan wuri zuwa wani wuri suna neman karafa, sandar karfe, roba, igiyoyi masu sulke da wutar lantarki, da kuma kayayyakin aluminum.
Mazauna yankin sun kara nuna damuwarsu kan yadda kananan yara da suka isa makaranta na daga cikin wadanda ke yawo a kan tituna domin neman wadannan kayayyaki a dukkan sassan jihar.
Dr. Habibu Kamilu, daya daga cikin mazauna yankin, ya koka kan yadda yara kanana ke shiga gidajen mutane suna satar irin wadannan karafa domin a sayar wa dillalai ko wakilansu masu sarrafa kayan.
Ya ce: “Wani lokaci waɗannan yaran ma suna tsalle-tsalle cikin gine-ginen da ba a kammala su ba don lalata linta da satar sandunan ƙarafa. 
“Abin takaici ne yadda hatta Masallatai ba su tsira daga barnar da irin wadannan mutane ke yi ba.
“Suna shiga gidaje ne domin satar tukwanen karfe da aluminum, makulli, da duk wani nau’in karafa da ya zo hanyarsu, kuma ana zarginsu da sayar da su ga dillalan karafa don samun kudi.”
Ya kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta daukar matakan dakile yaduwar wannan dabi’un tare da hana irin wadannan kananan yara yin sata tun suna kanana.
Kamilu ya kuma bukaci masu sayar da kayan shara da su tsaftace kasuwancinsu “ta hanyar kin kayan kananan yara, mutanen da ke kokwanton halsyensu kuma a daina siyan wadannan kayan da dare.”
Wani mazaunin Garin Katsina, Muhammad Abdullahi, ya koka da yadda irin wa ‘yannan matagari ke lalata tashoshi da sauran kadarorin jama’a domin neman igiyoyi da sandun karafa da kayan aluminium.
Abdullahi ya bukaci gwamnatin jihar da ta gaggauta daukar matakan da za su magance matsalar.
Kabir Umar, wani mazaunin yankin, ya nuna damuwarsa kan lamarin, ya kuma jaddada bukatar gwamnati ta bullo da wasu matakai na kawar da wannan matsalar.
Ya ce matsalar na zama wani lamari da ke damun gidaje musamman da ma al’umma gaba daya.
Don haka ya bukaci gwamnati da ta kara kaimi wajen shirya horar da matasa domin samar da ayyukan yi ta hanyar koyar da sana’o’in hannu domin dogaro da kai. (NAN) ( www.nannews.ng )
ZI/KLM
=====
Muhammad Lawal ne ya gyara

Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *