Tinubu ya yi maraba da nasarar da APC ta samu a zaben gwamnan Edo

Tinubu ya yi maraba da nasarar da APC ta samu a zaben gwamnan Edo

Spread the love

Tinubu ya yi maraba da nasarar da APC ta samu a zaben gwamnan Edo

Nasara

By Salif Atojoko

Abuja, Satumba 23, 2024 (NAN) Shugaban kasa Bola Tinubu ya taya Sanata Monday Okpebholo, dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben gwamnan jihar Edo da aka yi ranar Asabar, murnar nasarar da ya samu a zaben.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben a ranar Lahadin da ta gabata, bayan da ya doke sauran wadanda ke neman kujerar.

Tinubu ya yabawa shugabannin jam’iyyar APC na kasa da shugabannin Edo da gwamnonin jam’iyyar da suka yi aiki tukuru domin samun nasara, in ji Mista Bayo Onanuga, mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru a cikin wata sanarwa.

Shugaban ya ce nasarar ta shaida irin goyon bayan da jama’a ke ba jam’iyya mai mulki, da manufofin ci gaba, da shirin farfado da tattalin arziki da kuma jajircewa wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ya roki Okpebholo da kada ya yi murna da nasarar da ya samu amma ya gan ta a matsayin kira ga hidima.

Ya kara masa kwarin guiwa da ya nuna kwarjini ta hanyar tuntubar abokan hamayyarsa na siyasa da hada kan mutanen Edo don tabbatar da ci gaba.

Tinubu ya kuma yabawa sauran ’yan takarar da suka halarci zaben bisa gudunmawar da suka bayar wajen ciyar da dimokuradiyyar Najeriya gaba, inda ya ce fafatawar siyasa cikin lumana irin ta ranar Asabar tana bayyana Najeriya a matsayin turbar dimokradiyya.

Shugaban ya bukaci duk wadanda sakamakon zaben ya fusata da su nemi hakkinsu ta hanyar doka.

Bugu da kari, shugaban ya yabawa al’ummar Edo kan yadda suka gudanar da zabe cikin tsari da lumana a lokacin zaben, inda ya nuna amsuwar tsarin dimokuradiyyar a kasa bayan shekaru 25.

“Ina yaba wa INEC da jami’an tsaronmu da suke aiki ba dare ba rana domin gudanar da atisayen cikin nasara, cikin lumana da kuma rashin cikas.

Tinubu ya kara da cewa “INEC ta sake nuna cewa ta himmatu wajen shirya zabe mai inganci a kasarmu.” (NAN) (www.nannews.ng)

SA/HA

Hadiza Mohammed-Aliyu ta gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *