Ambaliyar ruwa: WHO ta mika wa gwamnatin Borno kayan tallafin kariyar cutar kwalara da na abinci mai gina jiki 

Ambaliyar ruwa: WHO ta mika wa gwamnatin Borno kayan tallafin kariyar cutar kwalara da na abinci mai gina jiki 

Spread the love

Ambaliyar ruwa: WHO ta mika wa gwamnatin Borno kayan tallafin kariyar cutar kwalara da na abinci mai gina jiki 

Jami’an gwamnatin Borno da na WHO, a wajen karbar tallafin cutar kwalara da na abinci mai gina jiki a Maiduguri ranar Asabar

Gabatarwa

By Yakubu Uba

Maiduguri, Satumba 21, 2024 (NAN) Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta gabatar da magungunan kariya da na kula da cutar kwalara da tamowa ga Gwamnatin Jihar Borno domin shawo kan kalubalen kiwon lafiya da ke iya samuwa sakamakon bala’in ambaliyar ruwa a Maiduguri.

Wakilin WHO na kasa, Dr Walter Kazadi, ya bayyana haka a lokacin da ake gabatar da kayayyakin a ranar Asabar a Maiduguri.

Ya ce matakin zai karfafa jihar wajen daukar matakan gaggawa.

Jami’ar hukumar Dr Mary Brantuo ce ta wakilci Kazadi ta kuma jaddada bukatar hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki domin dakile kalubalen kiwon lafiya da ambaliyar ruwa ta haddasa.

“Yayin da muka taru a nan, yana da muhimmanci mu gane cewa ambaliyar ruwa ta jawo wa al’ummar jihar Borno wahalhalun da ba a taba gani ba.

“Wannan bala’i ba kawai iyalai sun rasa muhallansu ba, har ma da kara haɗarin cututtuka masu saurin kisa kamar kwalara da kuma ta’azzarar yanayin abinci mai gina jiki na yara waɗanda ke fama da rashin abinci mai gina jiki,” in ji Kazadi.

A cewarsa, kayan aikin kwalara za su kasance masu mahimmanci wajen shawo kan cutar da kuma rigakafin barkewar cutar, yayin da nau’ukan abinci mai gina jiki za su taimaka wa ma’aikatan kiwon lafiya na wajen yaki da matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara.

“Kowanne daga kayan aikin kwalarar na da iya bada damar kula da masu cutar kwalara har 100, ma’ana jimillar kayayyakin da aka bayar a yau za su iya kula da mutane masu yaww da ke fama da cutar.

“Kayayyakin SAM za su samar da muhimman kayan warkewa don kula da yaran da ke fuskantar matsalar rashin abinci mai gina jiki. Kowane kati na iya kula da yara 1,607 da ke fama da tamowa mai tsanani, wanda hakan zai sa a kai ga kai ga yara 225,000 a yankunan da abin ya shafa,” inji shi.

Da yake mayar da martani, Farfesa Baba Malum-Gana, kwamishinan lafiya na jihar Borno, ya yaba wa hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya kan wannan daukin da aka yi a kan lokaci, inda ya kara da cewa kawo yanzu babu tabbacin cutar kwalara a jihar.

Malum-Gana ya ce cutar zazzabin cizon sauro na ci gaba da kasancewa Babba kalubalen kiwon lafiya, inda ya kara da cewa samar da na’urar gano cutar zazzabin cizon sauro cikin gaggawa zai taimaka matuka wajen dakile cutar. (NAN) (www.nannews.ng)

YMU/RSA

========

Rabiu Sani-Ali ya gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *