NELFUND za ta fadada lamuni zuwa ga dalibai masu horon sana’o’i

NELFUND za ta fadada lamuni zuwa ga dalibai masu horon sana’o’i

Spread the love

 

Lamuni

By Funmilayo Adeyemi

Abuja, Nuwamba 18, 2025 (NAN) Asusun bada lamunu na ilimin Najeriya (NELFUND), ya sanar da shirin tsawaita shirin ba da lamuni na dalibai don shirye shiryen koyon sana’o’i.

Manajan Darakta na NELFUND, Akintunde Sawyerr ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a Abuja.

Sawyerr ya ce tsarin fadadawar ya yi dai-dai da shirin gwamnatin tarayya na bunkasa ilimi da fasaha.

Ya kara da cewa matakin ya nuna yadda shugaban kasa Bola Tinubu, ya kuduri aniyar samar da ci gaban jarin masu sana’o’i fiye da ilimin jami’a na gargajiya.

“Babu wata al’umma da masana suka gina su kadai.

“Yana da matukar muhimmanci a sami mutanen da za su iya amfani da hannayensu, a kara masu kuzari, ƙarfafa su, da basira don aiwatar da dabaru masu wayo da ke fitowa daga waɗanda ke fitowa daga cibiyoyin ilimi,” in ji shi.

Sawyerr ya bayyana cewa, yayin da NELFUND ta fi mayar da hankali kan bayar da tallafin kudi ga dalibai a manyan makarantu tun lokacin da aka kaddamar da shi, aka fara shirye-shiryen fadada shi ga masu sana’a da fasaha a fadin kasar.

A cewarsa, mataki na gaba na ci gaban Najeriya yana bukatar daidaito tsakanin kwarewar ilimi da fasaha.

“A NELFUND, muna da hurumin yin sana’o’i.

“Ba mu fara ba tukuna, amma na san cewa gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ta tabbatar da cewa an samu cikakken bayani kan batun.

” Ma’aikatar ci gaban matasa tana yin sana’o’i, ma’aikatar Ilimi ta shiga sana’o’i da kuma ma’aikatar tattalin arziki ta dijital ta shiga cikin dabarun IT.

“Don haka, fasaha wani abu ne da aka sa ma’aikatun gwamnati da yawa da aikatawa.

“Kuma ina ganin a fili yake cewa injiniyan da zai iya yin gini, ya fi injiniyan da zai iya zane kawai.

“Matakin da muke a kasar nan a yanzu, shine abin da zan kira, tsarawa, ginawa, da sarrafa matakin,” in ji shi.

(NAN)( www.nannews.ng )

FAK/ROT

=======

Rotimi Ijikanmi ne ya gyara shi

Aisha Ahmed ta fassara shi.


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *