Gwamna Yusuf ya rantsar da sabon Sakataren gwamnati

Gwamna Yusuf ya rantsar da sabon Sakataren gwamnati

Spread the love

Gwamna Yusuf ya rantsar da sabon Sakataren gwamnati
An rantsar da shi
Daga Aminu Garko
Kano, Feb. 10, 2025 (NAN) Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano a ranar Litinin ya rantsar da Umar Farouk-Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar (SSG) a wani biki mai a ofishin gwamna.
Babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a Haruna Isa-Dederi ne ya jagoranci taron.
Nadin Ibrahim ya zo ne bayan da aka sauke magabacinsa Abdullahi Baffa-Bichi daga mukaminsa, tare da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati da wasu kwamishinoni biyar.
A cewar mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature, an zabi Ibrahim ne saboda gogewa da yake da shi, wanda hakan zai taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da manufofin gwamnati gaba.
 Yusuf ya bayyana kwarin gwiwar cewa nadin Ibrahim zai taimaka matuka wajen cimma manufofin gwamnatinsa ga jihar.
Ya kuma jaddada mahimmancin jagoranci wajen tafiyar da jihar domin samun ci gaba mai dorewa.( NAN) ( www.nannews.ng )
AAG/BRM
=========
Edited by Bashir Rabe Mani

Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *