NAN HAUSA

Loading

Zulum ya sake tsugunar da iyalai 424 da B’Haram ta raba da gidajensu a karamar hukumar Konduga

Zulum ya sake tsugunar da iyalai 424 da B’Haram ta raba da gidajensu a karamar hukumar Konduga

Spread the love

Zulum ya sake tsugunar da iyalai 424 da B’Haram ta raba da gidajensu a karamar hukumar Konduga

Matsugunni

By Yakubu Uba

Maiduguri, Oct. 7, 2024 (NAN) Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya sake tsugunar da iyalai 424 da rikicin Boko Haram ya shafa a sabbin gidaje 500 da aka gina a garin Konduga.

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya rawaito cewa mutanen da aka sake tsugunar da su sun fito ne daga garuruwan Towuri, Modu Amsamiri, Goniri, Mairamiri, Lawanti Grema Gogobe, Bula Bowuri, Zarmari, Amusari, Bula Bakaraye da kuma Furi, al’ummomin da mayakan Boko Haram suka raba da gidajensu.

NAN ta ruwaito cewa gidajen da aka tsugunar da matsugunan na da kayayyakin kamar makarantu, cibiyar kula da lafiya a matakin farko, wuraren samar da ruwa da sauran bukatu.

Da yake jawabi a wajen mika gidajen a ranar Lahadi a garin Konduga, Zulum ya lura cewa, sake tsugunar da mutanen ya nuna mafarin rufe sansanonin ‘yan gudun hijira a karamar hukumar Konduga.

Baya ga gidajen, kowane iyali ya kuma sami kayan abinci, barguna, tabarbare, katifa, bokitin roba da nannade.

Hakazalika, kowane mai gidan ya karbi Naira 50,000; yayin da matan gidan suka karbi Naira 20,000 a matsayin wani bangare na shirin sake tsugunar da su don tallafa musu wajen dibar kayan rayuwarsu.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatin jihar na sake tsugunar da duk wadanda rikicin tada kayar baya ya raba da muhallansu da har yanzu suna sansanoni.

“Bukatar rufe sansanonin ya zama dole a bisa yadda wasu sansanonin ke rikidewa zuwa wuraren aikata laifuka da cibiyoyin munanan dabi’u iri-iri.

“Masu aikata laifuka sun kasance suna kwana a wasu sansanonin ciki har da ‘yan Boko Haram. Wannan ba abin yarda ba ne, ”in ji Zulum.

Gwamnan ya ce gwamnatin jihar tana kuma gina gidaje 500 a unguwar Dalwa da za a kammala cikin watanni shida, a lokacin da za a sake tsugunar da su.

“Mun kuma ba da umarnin a ba da katangar Naira miliyan 100 don sake gina wasu gidaje a unguwar Aulari.”

Ya kuma gargadi wadanda suka amfana da su guji sayar da gidajen da aka ware musu.

Zulum ya bukace su da su dasa itatuwa domin yaki da hayakin Carbon da kwararowar Hamada. (NAN)YMU/SH

Edita Sadiya Hamza

Fassara daga Nabilu Balarabe

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *