NAN HAUSA

Loading

Damfara : ‘Yansanda sun gargadi yan Nageria akan kutse a shafukkan yanar gizo

Damfara : ‘Yansanda sun gargadi yan Nageria akan kutse a shafukkan yanar gizo

Spread the love

Damfara : ‘Yansanda sun gargadi yan Nageria akan kutse a shafukkan yanar gizo

Gargadi

Damaturu, Satumba 25, 2024 (NAN) Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ta gargadi mazauna jihar da su yi taka-tsan-tsan da wasu mutane masu gayyatar tattaunawar karya a shafukkan zumunta na yanar gizo don gudin damfara.

DSP Dungus Abdulkarim, Kakakin rundunar ‘yan sandan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Damaturu ranar Laraba.

Ya ce wata kungiya ce ta kikiri taron don yin anfani da shi wajen yaudaran jama’a da yi musu zamba cikin aminci.

“Masu satar bayanan jama’a sun kirkiri tarurrukan intanet na karya kuma suna aika sakonnin gayyata ta hanyar yanar gizo ga jama’a.

“Da zarar mutum ya danna hanyar haɗin yanar gizon, sai su yi masa kutse a asusun ajiyar sa na banki da sauran bayanan sirri,” in ji shi.

Kakakin ya ce a wasu lokutan, yan damfaran na fakewa da cewa su maikatan banki ne masu inganta asusun abokan cinikinsu.

” Sukan aika da lambar kalmar sirri ta OTP zuwa kafofin sada zumunta ko kuma wayar hannu, kuma su bukaceku da ku mayar da lambar sirrin don yin rijista ko kuma tabbatar da asusunku.

“Duk wanda ya yi haka, yana baiwa ‘yan damfarar damar cire kudi daga asusunsa cikin mintuna kadan,” in ji shi.

Jami’in ya kuma bukaci jama’a da su yi hattara da masu aikata laifuffukan yanar gizo tare da kaucewa bada bayyanan banki ga duk wanda bai cancanta ba.

Ya shawarci abokan huldar bankin da su tabbatar da irin wadannan bukatu ta hanyar kiran waya ko ziyartar bankunan su ko cibiyoyin hada-hadar kudi don karin bayan.

“Kada ka taɓa aika lambobin OTP ko mahimman bayanai zuwa wuraren da ba a tantance ba. Yi hattara da tarukan yanar gizo ko sabunta asusunka.

“Ku sa ido akan asusunku akai-akai kuma ku kai rahoton duk wani abun da ba daidai ba ga jamian tsaro,” in ji shi.

A cewarsa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya gargadi masu laifin da su daina aikata hakan ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani. (NAN) (www.nannews.ng)

NB/RSA

======

Rabiu Sani-Ali ya gyara


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *