NAN HAUSA

Loading

An ceto daliban likitanci 20 da akayi garkuwa da su

An ceto daliban likitanci 20 da akayi garkuwa da su

Spread the love

An ceto daliban likitanci 20 da akayi garkuwa da su

Ceto
Daga Emmanuel Anstwen
Makurdi, Aug 24, 2024 (NAN) Hukumar Yan Sanda a jihar Benue ta tabbatar da sakin daliban jamio’in Maiduguri da Jos da aka sace a jihar da ke Arewa Maso Tsakia a ranar 15 ga Augusta.

Jamiin Yada Labaru na Yan sandan, Mista Sewuese Anene, ne ya tabbatar sakin daliban wa kampanin Dillancin Labarun Nageria (NAN) a Makurdi ranar Jumma’a.

Kamfanin Dillacin Labarai Na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa daliban an sace su ne a garin Oturkpo yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Enugu don taron shekara-da-shekara na gamayyar daliban likitanci na katolica ( FECAMDS).

Rahoton ya kara da cewa wani jamiin kiwon lafiya da ke tare da daliban shima an sace shi.

Sai dai Anene bai bada Karin haske ga ceton daliban da akayi ba.

“ An sako wadanda aka kama. Za‘a bada karin bayani a gobe ( Azabtar) da safe,” ya ce.

Sako daliban na zuwa ne kwana biyar bayan Shugaban Yansandan Nigeria, Mista Olukayode Egbetokun, ya turo zaratan Yansanda zuwa Benue, ya kuma ba wa Shugaban Yansandan jihar umurnin ya ta fi Oturkpo.

NAN ta gano cewa wata hadakar jamian tsaro bisa jagorancin Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara Akan Harkokin Tsaro ne ta ceto daliban.(www.nannews.ng)(NAN)AEB/ETS
Fassara daga Nabilu Balarabe

 

 

 

 

 

 


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *