NAN HAUSA

Loading

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista 

Spread the love

 

 

Manoman chitta sun yi asarar biliyan N12 a 2023 – cewar Minista

 

Asara

 

Daga Doris Esa

 

Abuja, Aug. 22, 2024 (NAN) Gwamnatin Tarayyan Najeriya tace manoman chitta a kasar sun yi asarar kudi kimanin biliyan N12 a sanadiyar annobar chutar chitta da ta afkawa gonaki a 2023.

 

Sanata Aliyu Abdullahi, karamin Ministan, a ma’aikatar Gona, da Tattalin Abinci, ya sanar da hakan yayin kaddamar da taron ba da hora wa masu horar wa, wanda hukumar inshora ta gona ta shirya a ranar Alhamis a Abuja.

 

Ministan ya haska kadan daga cikin matsalolin da manoman suka fuskanta a yayin noman damina na 2023, inda manoman chitta a JIhar Kaduna suka yi asara mai matukar yawa sanadiyar annobar chutar chittan.

 

Abdullahi yace manoman sun rasa kimanin kashi 90 daga cikin dari na amfanin gonarsu a noman da suka yi a daminar bara.

 

“Kadan daga cikin manoman chittan  da suka yiwa gonakin su garkuwan inshora ne suka  karbi diyya na daga asarar da suka yi sanadiyar annobar chutar chittan.

 

“Wa dannan jerin manoman za su yi alfaharin komawa gona ba tare da wani tallafin kudi dan kadan ba, kuma ba kamar yan uwansu manoman da basu yiwa gonakinsu garkuwan inshora ba, wadanda a yanzu sai sun kwashe duk abun dake cikin asusun su, dan komawar su zuwa gona.

 

“Wannan shine darasin da yazama dole akanmu; kamar yadda make a dukkan lokuta mukan samu kanmu a cikin asara sanadiyar zuwan mummunar damuna daya ko biyu, wannan be shafi karancin abinci ba,” a cewar sa.

 

Abdullahi yace alkalumman hashashe na ambaliyar ruwan sama na 2024 wanda maikatar ruwa da tsaftace muhalli ta fitar, ta hankaltar da kananan hukumomi 148 a jihohi 31 ha suke cikin barazanar ambaliyar ruwan sama a yankunan su.

 

Ya ci gaba da cewa rahotonni na watanin farkon shekara da ake ciki sunyi nuni da cewa kananan hukumomi 249 a jahohi 36 tare da birnin tarayya sun shigo cikin jerin yankuna da suke da saukin samun hadarin ambaliyar.

 

“A sauka ke, kananan hukumomi 397 daga cikin 774 a Najeriya, ko kuma kashi 51 daga cikin wajajen noma a kasar na cikin hadarin samun ambaliyar ruwan sama,” a cewar sa.

 

“Hakika muna sheda wa a bayyane a yanzu ba a wani lokaciba babbar barazanar dumamar yanayi da illar da ke tare da ita a tattare da amfanin gonakinmu na gida a tsarikanmu na kasa baki daya,” a bayanin da ya kara,” ministan ya fada.

 

Abdullahi yace tsare-tsaren na gaba gaba, na maikatar gwamnatin tarayya tare da hadinkan kamfanoni masu zaman kansu, da kuma hukumar NAIC da ta PULA, wanda sune mashawartan  kamfanin inshoran gona wanda suke gudanar da tsare tsaran National Agricultural Growth Scheme Agro-Pocket (NAGS-AP).

 

Ya kuma kara da cewa ya tabbata cewa dumamar yanayi gaskiyace ta tabbata dolene a shigar da tsarin inshora cikin harkar noma a matsayin ta ta abokiyar tafiya a cikin tsarin gwamnatin ta NASG dan tabbatar da dorewa da kuma masu buƙatar wadatar abinci sosai a kasa.

 

Ministan yace tsarin NAGS-AP wanda ya fara a 2023 yayin noman rani na alkama ya haifar da amfanin gona mai yawa. (NAN) (www.nannews.ng)

 

ORD/JPE

 

=======

 

Edita Joseph Edeh

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *