Tinubu ya bar Abuja zuwa Turai domin hutun shekara
Tinubu ya bar Abuja zuwa Turai domin hutun shekara
Hutu
Daga Muhyideen Jimoh
Abuja, 4 ga Satumba, 2025 (NAN) Shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja 4 ga watan Satumba, don fara hutun aiki a Turai a wani bangare na hutun shekara ta 2025.
Mai magana da yawun shugaban kasa, Mista Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.
Onanuga ya bayyana cewa hutun zai dauki kwanaki 10 na aiki.
Ya kara da cewa Tinubu zai shafe tsawon lokaci tsakanin Faransa da Birtaniya sannan ya dawo kasar.
(NAN)(www.nannews.ng)
MUYI/JPE
========
Joseph Edeh ne ya gyara