NAN HAUSA

Loading

Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya bukaci likitoci su cigaba da jajircewa

Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya bukaci likitoci su cigaba da jajircewa

Spread the love

Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya bukaci likitoci su cigaba da jajircewa

Likitoci

Daga Habibu Harisu

Sokoto, Satumba 14, 2024 (NAN) Manajan Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), Malam Ali M. Ali, ya bukaci likitoci da su ci gaba da jajircewa, mayar da hankali, da sadaukar da kai wajen yi wa bil’adama hidima.

Ali ya ba da wannan nasihar ne a ranar Asabar a Sakkwato a wajen bikin yaye daliban jami’ar Sudan International University (SIU) da kuma daliban Kwalejin Kiwon Lafiyar Hayat da suka karasa karstu a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato (UDUS) na shekarar 2023.

Ya kuma bukaci daliban da a ka yaye da su rike kyawawan dabi’u, kuma su rika nuna kwazo, mutunci, mutuntawa da tarbiyyar da aka cusa musu a lokacin karatunsu.

Ali ya bukace su da su dauki gwagwarmayarsu ta ilimi da muhimmanci domin tana cike da kalubale duba da irin rikicin da ya barke a Sudan a tsakiyar karatunsu.

”A matsayina na mahaifin ɗaya daga cikin waɗanda suka kammala karatun, ina jin daɗi, alfahari da gamsuwa ganin da tafiyar da aka fara da nisa ta zo ƙarshe.

”Buri ne ya cika ga ɗana, yayin da na so ya karanta Kimiyyar Kwamfuta amma ya nace ya zama Likita.

“Na tuna cewa mahaifina yana son in karanta aikin likita, amma na nace Sai  karanta aikin jarida, don haka mafarkin mahaifina ya bayyana a rayuwar jikansa, na gamsu,” in ji Ali.

Ya ce daliban da suka kammala karatun sun fuskanci kalubale domin a shekararsu ta farko da suka yi karatu, an hambarar da gwamnatin Shugaba Umar Al-Bashir, da. COVID-19 da rikicin shugabanci a Sudan.

Ya bayyana cewa, wani kalubalen da suka fuskanta shi ne kudin da suka fara a lokacin da Dalar Amurka ta kai kusan Naira 250 kuma kafin su kammala karatunsu ya kai kusan N1,300 ko sama da haka.

“Kada ku bar wani shine da zai hana ku neman nasara don ba ta zuwa da sauƙi. Kada ka bari abubuwa da yawa su datse mafarkinku da burinku.

“Ku yi amfani da ilimin da ku ka samu daga malamanku, ku fuskanci nayuwa mai kyau, don kun zama taurari masu haske kuma ku kasance masu dagewa da hidima ga ‘yanuwaku’ yan adam.

“Ba shakka cewa darussan da kuka koya a cikin karatun da kuma daga iyayenku, za su ci gaba da jagorantar ku ta hanyar rayuwa,” in ji Ali.

Wani mahaifin, Haruna Adiya, ya bayyana cewa taron ya kasance abin tunawa don ganin irin jarin da suka dukufa da kuma sadaukarwar da daliban suka yi.

A jawabinsa na bajinta, wani dalibi da ya kammala digiri, Muhammad Ali, dan shugaban NAN, ya bayyana tafiyar a matsayin kalubale.

”Wannan yana nuni da cewa muna da damar samun karin nasarori. Don zama Likitoci kwararru Kuma wanna nasarar wani kira ne don yi wa bil’adama hidima.”

Wata wacce ta kammala digiri, Sakina Mu’azu, ta yaba da sadaukarwar da Farfesoshi da sauran malamai suka yi duk da dimbin kalubalen da suka fuskanta kamar yakin Sudan a lokacin karatunsu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa akalla mutane 64 ne a ka yaye a fannonin likitanci, Pharmacy, Biomedical Engineering, Clinical Sciences da sauran kwasa-kwasai da sauransu. (NAN)(www.nannews.com)

HMH/BRM

Bashir Rabe Mani ne ya tace


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *