Shugaba Tinubu ya tafi kasar Faransa gabanin taron yankin Afrika da zai gudana a Addis Ababa
Shugaba Tinubu ya tafi kasar Faransa gabanin taron yankin Afirka da zai gudana a Addis Ababa
Faransa
Daga Salif Atojoko
Abuja, Fabrairu 5, 2025 (NAN) Shugaba Bola Tinubu zai bar Abuja ranar Laraba zuwa birnin Paris na kasar Faransa,
a wata ziyarar aiki da zai kai Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.
A Birnin Addis Ababa, shugaba Tinubu zai bi sahun shugabannin Afirka a taron majalisar zartarwa karo na 46
da kuma zaman taro na 38 na shugabannin kasashen kungiyar Afrika wanda aka shirya yi daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairu.
Mista Bayo Onanuga, kakakin shugaban kasar, a wata sanarwa, ya kara da cewa “shugaban zai isa birnin Addis Ababa a farkon mako mai zuwa don halartar taron AU.
“Yayin da yake kasar Faransa, shugaba Tinubu zai gana da takwaransa na Faransa, shugaba Emmanuel Macron. (NAN)(www.nannews.ng)
SA/SOA
========
Oluwole Sogunle ne ya gyara