Kwamitin majalisar wakilai ya yaba da sake fasalin kiwon lafiya a jihar Jigawa

Kwamitin majalisar wakilai ya yaba da sake fasalin kiwon lafiya a jihar Jigawa

Spread the love

Kwamitin majalisar wakilai ya yaba da sake fasalin kiwon lafiya a Jigawa

Lafiya

Daga Aisha Ahmed 

Dutse, Aug. 22, 2025 (NAN) Kwamitin majalisar wakilai mai kula da harkokin kiwon lafiya, ya yabawa gwamnatin jihar Jigawa bisa bullo da sabbin tsare-tsare masu inganci a fannin kiwon lafiya. 

Shugaban kwamitin, Mista Amos Gwamna-Magaji, ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi,;a Dutse.

Ya yaba da irin nasarorin da aka samu a shirin kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, musamman kashi 15 na kasafin kudin da aka ware wa fannin.

“Muna alfahari da farin cikin jin cewa sama da kashi 15 cikin 100 na kasafin kudi na shekara bana, don kiwon lafiya ne, wanda abin mamaki ne kuma ya yi tasiri.

“Duk da haka, mun kuma ga cewa sama da kashi 15 cikin 100 na kasafin, ba a takarda kawai yake ba, kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin na yawo tare da sauya yanayin kiwon lafiya yadda ya kamata a jihar Jigawa,” inji shi.

Gwamna-Magaji ya taya gwamnan murnar samun kyautar kudi sama da dala 500,000 na PSC Leadership Challenge Award da jihar ta samu.

Yana mai bayyana hakan a matsayin hujjar daukakar kimarsa a garambawul na kiwon lafiya. 

“Wannan ya nuna jajircewar ku da kuma matsayin da kuka kai, da kuma abin da kuka yi a fannin lafiya,” in ji shi.

Shugaban ya kuma yabawa gwamnatin jihar, kan yadda aka daidaita albashin ma’aikatan lafiya da ma’auni na tarayya.

Ya kara da cewa, wannan wani gagarumin mataki ne na magance dakilewar kwakwalwar kwararrun likitoci.

Da yake mayar da martani, Namadi ya sake jaddada kudurin sauya fannin kiwon lafiya zuwa ga cimma nasarar da ake samu na kula da lafiya ta duniya (UHC) a jihar.

 A cewar Namadi, kiwon lafiya shine tushen ci gaban zamantakewa da bunkasar tattalin arziki da ci gaban al’umma. 

“Mun yi imanin cewa al’umma mai koshin lafiya al’umma ce mai ci gaba, tare da lafiya ne kawai za ku nemi ilimi, kuma ku bunkasa harkokin tattalin arziki don inganta tattalin arziki,” in ji shi.

Ya ce gwamnatinsa ta gudanar da bincike na kwakwaf, don jagorantar tsare-tsare da ba da fifiko a dukkan bangarori, tare da kula da lafiya a matsayin fifiko.

Namadi ya ce jihar ta mayar da hankali ne wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko, da ke zama ginshikin samar da ingantaccen sabis. 

“Dole ne a karfafa kiwon lafiya na farko don samar da lafiya ga mutane. Mun tabbatar akwai bukatar samar da cibiyoyin kiwon daga tushe, inda ma’aikata da ‘yan ƙasa za su yi farin ciki,” in ji shi. 

Gwamnan ya bada tabbacin aniyar gwamnatin sa na zurfafa sauye-sauyen harkokin kiwon lafiya domin cimma nasarar UHC. (NAN) (www.nannews.ng)

 

 AAA// RSA 

Fassarar Aisha Ahmed


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *