Kotu ta daure wata mata yar shekaru 25, bisa zargin satar jariri dan watanni biyu

Kotu ta daure wata mata yar shekaru 25, bisa zargin satar jariri dan watanni biyu

Spread the love

Daga Olawale Akinremi

Ibadan, Aug. 5, 2025 (NAN) Wata babbar kotun majistare da ke zamanta a Mapo, a Ibadan  ta bayar da umarnin tsare wata mata ‘yar shekara 25 mai suna Odunayo Odunlade, a gidan gyaran hali na Agodi, bisa zargin satar jariri dan watanni biyu.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN), ya ruwaito cewa Odunlade ta musanta zargin da aka yi mata, sai dai wanda ake zargin ba ta iya cika sharuddan belin da kotu ta yi mata ba.

Alkalin kotun, Mrs OO Latunji, ta bada belin Odunlade a kan kudi naira 500,000, tare da sa hannun wasu amintattun mutane guda biyu.

Daga bisani Latunji, ta dage zaman shari’ar zuwa ranar 21 ga watan Oktoba, domin yi kammala shari’ar.

Lauya mai shigar da kara, Insp. Oluseye Akinola, ya shaida wa kotun cewa, wadda ake tuhuma ta aikata laifin ne a ranar 24 ga watan Yuli, a unguwar Lascap-Oniyanrin da ke Ibadan.

Akinola ya ce, Odunlada saci yaron ne daga dakin da mahaifiyarsa ta ajiye shi, ya kara da cewa jami’an ‘yan sanda a ofishinsu na Mokola, sun kai daukin gaggawa bayan sun samu bayanai kan ta’asar.

Jami’in ya tabbatar da cewa ‘yan sanda sun yi nasarar bin diddigin wadda ake kara, a wani wurin da bai bayyana ba, kwanaki kadan bayan sace yaron.

A cewar sa, laifin da matar da ake zargi ta aikata, ya ci karo da tanadin sashe na 390(9) na kundin laifuffuka, Cap. 38, Vol. ii, Dokar Jihar Oyo, 2000. (NAN)

Edited by Aisha Ahmed

 


Spread the love

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *