NAN HAUSA

Loading

Shugaban kwamitin kiwon lafiya ya gargadi mata da suje gwajin ciwon daji

Shugaban kwamitin kiwon lafiya ya gargadi Mata da suje gwajin ciwon daji

Gwaji
Daga Awayi Kuje
Akwanga (Jihar Nasarawa), Satumba 19, 2024 (NAN) Mr Larry Ven-Bawa, Shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Nasarawa kan kiwon lafiya kuma memba da ke wakiltar yankin Akwanga North, ya gargadi mata da su cigaba da zuwa gwajin ciwon daji na mama da na ciki don sanin matsayinsu.

Ven-Bawa ya bada gardadin ranar alhamis a Akwanga, Jihar Nasarawa, yayin da ake bude yekuwar fadakarwar ta kwana hudu game da ciwon daji ga mata 2, 000 a gundumar Agyaga a karamar hukumar Akwanga.

Shugaban yace “ta hanyar gwajine za’a gano ciwon daji na mama saboda a ceci rayukan mata.’’

Yace za’ayi gwajegwajen a asibitin Kula da Lafiya ta Farko a yankin, ya kara da cewa “nayi tanadin magunguna, kayan aiki don ƙarfafawa tsakanin mutane, kuma a yau ina tallafa wa wannan aikin domin kare lafiyar mata.

“Zan cigaba da ba da fifiko ga lafiyar mutanen yankin Akwanga ta arewa da sauran al’umma.

“Mata da yawa sun mutu daga ciwon daji, saboda haka, ina bukatar mata su fito zuwa wannan gwaji saboda su tsare lafiyarsu.’’

Komishinan Lafiya ta Nasarawa, Likita Gwamna Gaza, da ya bude fara gwajegwajen, yace gwamnati zata cigaba da bada hankali wajen magance ciwon daji da wasu cuttuttaka a kasa.

Gaza, wanda Likita Yahaya Ubam, Sakataren Nasarawa State Health Insurance Agency (NASHIA) ya wakilta, ya yabawa Ven-Bawa saboda mahimmacin da ya baiwa lafiyar mata.

Shugabar kungiyar Mbegir Cancer Initiative, Elisha Mbegir, yace kungiyar a shirye take don kare lafiyar mata masu ciwon daji.

Ta kara da cewa gwajegwajen da za’a yi wa mata 2, 000 na kwana hudun aikin hadin gwiwa ne da kungiyar Mbegir.(NAN)(www.nannews.ng)
AKW/BRM
==========
Bashir Rabe Mani ne ya tace

Shettima ya bayyana samuwar zuba jarin dala biliyan 4.8 a fannin kiwon lafiya

Shettima ya bayyana samuwar zuba jarin dala biliyan 4.8 a fannin kiwon lafiya

Lafiya
Daga Salisu Saniidris
Abuja, Agusta 31, 2024 (NAN)Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ta yi a fannin kiwon lafiya ya janyo sama da dala biliyan 4.8 a bangaren zuba jari.

Najeriya ta karbi kashin farko na rigakafin cutar kyandar biri

Najeriya ta karbi kashin farko na rigakafin cutar kyandar biri

Rigakafi
Daga Racheal Abujah
Abuja, Agusta. 31, 2024 (NAN) Kasar Amurka ta baiwa Najeriya tallafin allurar
rigakafin da kamfanin kasar Denmark, Bavarian Nordic ya samar, da manufar dakile yaduwar nau’in cutar kyandar birin ta Clade ll.

Allurar rigakafin, guda dubu 10 ya isa Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Talata.

Kamfanin dillancin labarai ta Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa cutar kyandar biri cuta ce da ba ta da illa sosai, wadda kuma take yaduwa a kasar tun shekarar 2017.

Najeriya dai ta samu mutum fiye da 700 da a ke zargin sun kamu da cutar, kuma an tabbatar da kamuwar mutum fiye da 40.

A cikin karin bayanin da ta fita ranar Jumma’a, ma’aikatar kula da yaduwar cututtuka watau Nigeria Centre for Disease Control (NCDC) ta ruwaito karuwar yaduwar cutar.

Ma’aikatar tace an tabbatar da cutar a jikin mutane 48 daga kananan hukumomi guda 35 na kasar da kuma birnin tarayya, Abuja. (NAN)(www.nannews.ng)
AIR/HA
=======
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta tace

Gidauniyar Sultan Foundation ta bayar da tallafin magungunan da kudinsu ya kai N1.7bn ga Sokoto, Kebbi

Kyauta
Daga Habibu Harisu
Sokoto, Aug. 30, 2024 (NAN) Wata kungiya mai zaman kanta mai suna Sultan Foundation for Peace and Development (SFPD), ta bayar da tallafin magunguna da kayayyakin masarufi na Naira biliyan 1.7 ga gwamnatocin Sokoto da Kebbi.
Da yake mika kayayyakin, Shugaban Gunarwarwa na Gidauniyar kuma Mai Martaba Sarkin Argungu, Alhaji Muhammad Mera, ya ce gidauniyar kungiya ce mai zaman kanta bisa jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar.
“Magungunan da kayayyakin kiwon lafiya an samar dasu domin kara kaimi ga kokarin ma’aikatun lafiya na jihohin Sakkwato da Kebbi kan harkokin kiwon lafiya musamman ga mata da kananan yara.
” An samu magungunan ne daga kungiyar MAP International, wata kungiyar lafiya ta duniya da ke da hedkwata a Amurka, wacce ke ba da tallafin magunguna na ceton rayuwa da kuma kayayyakin kiwon lafiya ga al’ummomin da me da bukata a duniya.
“Mr Aminu Yaro, dan Najeriya da Nell Diallo, wanda dan kasar Senegal su ka tallafa wajen samun tallafin kudi daga gidauniyar Reed,” in ji Mera.
Shugaban gudanarwar ya yabawa Gwamnatin Tarayya bisa yadda ta yi dage da harajin jami’an shige da fice na kwastan da ya kai Naira miliyan 254 domin saukaka shigo da kayayyakin da aka bayar a kasar.
Daga nan ya bukaci gwamnatocin jihohin da su raba magunguna da kayayyaki ga asibitoci da wuraren kiwon lafiya domin amfanin majinyatan da suka cancanta da sauran wadanda suka amfana a jihar.
Ya bayyana fatansa na cewa wasu jihohi za su ci gajiyar tallafin a na gaba. 
Da yake mayar da martani a madadin gwamnatin jihar Sokoto, Malam Umar Attahiru, Darakta-Janar na Hukumar Kula da Magunguna da Magunguna ta Jihar Sakkwato (DMSMA), ya yaba da wannan tallafin.
Ya yabawa kyakkyawan jagoranci na Sultan Abubakar bisa jajircewar irin wannan kokarin tare da bada tabbacin yin amfani da kayayyakin yadda ya kamata ga jama’a.
Wakilin gwamnatin jihar Kebbi kuma babban sakatare a ma’aikatar lafiya ta jihar, Dakta Shehu Nuhu-Koko, ya ce magungunan da kayayyakin da ake amfani da su na da matukar muhimmanci ga al’umma.
Nuhu-Koko ya ce hakan zai yi tasiri mai kyau ga rayuwar ‘yan kasa, yana mai jaddada cewa, kayan na kunshe da magunguna da ake bukata lokaci-lokaci musamman a tsakanin mata masu juna biyu da yara a fadin jihohin kasar nan.
Kamfanin Dillancin Labarai na NAN ya ruwaito cewa, mika kyautar ya samu halartan Galadiman Garin Sokoto, Alhaji Attahiru Aliyu-Galadanchi, Malam Muhammad Lawal Maidoki Sadaukin Sokoto, Shugaban Hukumar Zakka da Waqaf na Jihar Sakkwato da Malam Aminu Inuwa Muhammad Darakta Shirye-shirye. na Sultan Foundation da sauransu. (NAN) (www.nannews.com)
HMH/SH
=======
edita Sadiya Hamza
.

Najeriya za ta iya cin gajiyar dala Amruka biliyan 100 a kasuwannin magani a duniya – cewar Masaniya

Najeriya za ta iya cin gajiyar dala Amruka biliyan 100 a kasuwannin magani a duniya – cewar Masaniya

Magani

Daga Alaba Olusola Oke

Ondo (Jihar Ondo), 30 ga Agusta, 2024 (NAN) Wata Ma’aikaciyar harhada magunguna, Misis Zainab Shariff, ta ce Najeriya za ta iya cin gajiyar dalar Amruka biliyan 100 a kasuwannin magani ta duniya.

Ta bayyana hakan ne a yayin bikin ranar maganin gargajiya na Afirka, wanda Cibiyar Nazarin Magungunan Gargajiya da Bincike ta Jami’ar Kimiyyar Lafiya (UNIMED) Ondo ta shirya a ranar Alhamis.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron mai suna “Hadawa da Inganta Magungunan Gargajiya na asali don Saukake Kiwon Lafiyar ” wanda a ka shirya a garin Ondo.

Shariff, wadda wata kwararriyar mai fafutuka ce na inganta Magungunan Gargajiya da na Asali (TCAM) Najeriya ce ta bayyana haka.

Masaniyar ta ce yin amfani da kasuwannin duniya don samar da irin magungunan zai samar da kusan dala tiriliyan biyar nan da shekarar 2050 a duniya.

A cikin makalarta ta mai taken “Haɓaka da Ci gaban Tsirrai na Magani don Samar da Kiwon Lafiya a Duniya”   ta jaddada buƙatar ƙara darajar magungunan da ake da su a ƙasar nan don fitar da su zuwa kasashen waje.

Gaskiyar halin da ake ciki yanzu, a cewarta, ba a nuna kasar Najeriya wajen fitar da tsire-tsire masu magani zuwa kasashen waje ba, duk da dimbin albarkatun da take da su.

Sai dai ta kara da cewa har yanzu akwai fata ga kasar idan har al’ummar kasar za su iya tantance filayen noman tsire-tsire na magani don kara darajarsu.

Masaniyar harhada magungunan ta ce kasar za ta iya samar da magungunan ganye da ire-iren su da za su shiga jerin amicewar hukumar ta NAFDAC zuwa kantuna daban-daban don tallafawa ci gaba da bincike.

Ta ba da shawarar cewa ya kamata kasar ta fadada hadin gwiwarta da masu ruwa da tsaki tare da aiwatar da shirye-shiryen digiri a fannin likitancin tsire-tsire.

A nasa jawabin, mataimakin shugaban Jami’ar UNIMED ta Ondo, Farfesa Adesegun Fatusi, ya ce tuni cibiyar ta dauki nauyin gudanar da karatun digiri na uku a fannin likitancin tsire-tsire.

Ya ce “a wani bangare na habakar huldar, cibiyar ta bayyana fa’idar magungunan ganye da tsire-tsire, ta kuma kafa Sashen fannin Magungunan da za su fara digiri na farko a shirin a watan Oktoba 2024.”

A nasa bangaren, Dokta Oghale Ovuakporie-Uvo, Darektan riko na cibiyar kula da magungunan tsire-tsire da ganye tare da gano magunguna, ya nanata kudurin cibiyar na gano magungunan ganye da tsire tsire domin saukaka harkokin kiwon lafiya a duniya.

Ovuakporie-Uvo ya ce fahimtar shirin shine tushe da kuma amfani da hankali na magungunan gargajiya na asali, musamman al’adun gargajiya da na lafiya dangane da amfani da tsire-tsire da ganye wanda ke da mahimmanci samar da cikakkiyar lafiya a yanayin mutanen Afirka. (NAN) (www.nannews.ng)

OKEO/HA

=======

Hadiza Mohammed-Aliyu ta gyara

Muna neman taimakon gwamnati – Masu ciwon sugar

Muna neman taimakon gwamnati – Masu ciwon sugar

Taimako
Daga Christian Njoku
Calabar, Aug. 29, 2024 (NAN) Wata kungiya mai suna — National Association of Persons Living with Diabetes – tayi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka wa masu cutar sugar saboda kudin abinci da magani sun hau.

Kungiyar tayi kiranne a wata hira da Mr Bernard Enyia, mai kula da harkar kungiyar yayi da kamfanin dillancin labarai na Nigeria (NAN) ranar alhamis a Calabar.

Enyia yace da yawa daga cikin masu fama da cutar sun rasa wayukansu saboda rashin kudin sayan magani da wadataccen abinci.

Ya kara da cewa dayawa a cikin masu fama da ciwon sun koma ga maganin gargajiya saboda bazasu iya sayan maganin asibiti ba.

Yace yawancin maganin ciwon sugar sai an kawosu ne daga kasashen ketare, shi yasa suke tsada, sai ya bukaci gwamnati da ta tallafa wa al’umma.

Enyia ya kara da cewa kudin alluran insulin da masu cutan suke amfani dashi wanda yake yi musu sati daya kacal, ya haura zuwa N19,000 ko N24,000 daga N4000 da suke saye a 2022.

Mai kula da al’amuran kungiyan yace har farashin alluran syringe da masu cutar suke amfani dashi ya hau daga N50 zuwa N600, kuma ana bukatar ayi anfani da guda biyu a kowane rana.

Yace masu cutar sugar suna cikin mawuyacin hali, sai ya nemi taimakon gwamnati da sauran al’umma wajen tabbatar da sun samu magani cikin sauki.(NAN)(www.nannews.ng)
CBN/HA
========
Hadiza Mohammed-Aliyu ce ta tace


Uwargidan shugaban kasa ta hada gwiwa da NPC, UNICEF kan rijistar haihuwa

Sanata Oluremi Tinubu

Uwargidan shugaban kasa ta hada gwiwa da NPC, UNICEF kan rijistar haihuwa

 

 

 

Rijista

 

Daga Celine-Damilola Oyewole

Abuja, Agusta 26, 2024(NAN) Ofishin Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu, Renewed Hope Initiative (RHI), na hada gwiwa da Hukumar Kididdiga ta Kasa (NPC) da UNICEF don kaddamar da na’urar rijistar haihuwa ga yara.

Shugaban NPC Nasir Kwarra ne ya bayyana hakan ga Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a ranar Litinin bayan wani taron share fage da uwargidan shugaban kasar a Abuja.

Ya ce, yin rajistar ya nuna aniyar gwamnatin Tinubu na karfafa rijistar haihuwar jarirai a kasar nan.

“Na zo ne domin tattaunawa da uwargidan shugaban kasa kan shirye-shiryen kaddamar da ranar rajista da takardar shaidar haihuwa ta 2024 da kuma yunkurin yin rijistar haihuwa a Najeriya.

“Muna so mu gode wa uwargidan shugaban kasa saboda amincewa da yin hakan tare da mu ta hanyar RHI. Duk da cewa rajistar haihuwa abu ne na duniya, muna ƙaddamar da shi a hukumance a ranar 29 ga Agusta tare da uwargidan shugaban kasa.

“Na yi imanin cewa wannan taron zai yi cikakken kwarin gwiwa na yin rajistar haihuwa don ba wa yaranmu asalinsu na farko da karramawa, don baiwa yaranmu damar samun ayyukan gwamnati musamman ilimi da kiwon lafiya.

Shugaban Hukumar Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, Mista Ibrahim Sessay, ya ce yunkurin na da matukar muhimmanci a Najeriya, wanda ke da yara sama da 244,000 da ake haifa a kullum.

“Duk da haka, abin da a zahiri ya ba yaron shaidar zama dan Najeriya, shaidar dan kasa ta dogara ne akan takardar haihuwa bayan rajista da NPC.

“Wannan taron shine don tabbatar da cewa duk yaron da aka haifa a Najeriya yana da rajista da NPC; suna da alhakin doka don tabbatar da cewa an yi rajistar haihuwarsu tare da takaddun shaida don tallafawa.

“Idan kuka duba shirinmu na ci gaba, idan ba ku san inda yaran suke ba, ta yaya za mu gina makaranta don yin hidima ga wannan jama’a da gaske ciki har da ayyukan kiwon lafiya. Yayin da suke girma, za su sami damar yin amfani da wasu ayyuka kamar inshora.”

Ya ce takardar haihuwa za ta taimaka wa UNICEF wajen sanin adadin yaran da za su yi hidima.

“Game da mallakar kadarori, wannan takardar shaidar ta sa ka zama dan Najeriya. Abin da ke da mahimmanci shi ne cewa mun kasance muna kasa kaiwa ga wannan wajibi.

“Uwargidan shugaban kasa, ta hanyar RHI, wani dandali ne da muke amfani da shi don tabbatar da cewa an fara haihuwar kowane yaro a Najeriya daga ranar 29 ga watan Agusta, ranar da za a fara aikin RHI don hanzarta yin rijistar haihuwa a fadin kasar.” (NAN)

OYE/IS

======

 

Edita Ismail Abdulaziz

Sabon wajen gwajegwan chututtuka zai fadada karfin sa na gwajin tarin fuika a Najeriya

 

Sabon wajen gwajegwan chututtuka zai fadada karfin sa na gwajin tarin fuika a Najeriya

 

 

Gwaji

Daga Wakiliyar mu  –Deborah Coker

Abuja, Aug. 22, 2024 (NAN) Col. Eli Lozano, Kwamandan Chibiyar Nazarin Binchike mai suna Walter Reed, ta Rundunar Sojan Amurka ya bayyana cewa sabon wajen gwajegwajan chutattukasu dake barikin sojan Najeriya na Mogadishu, A Birnin Abuja zai fadada karfinsa na gwajin tarin fuka.

 

Lozano ya bayyana hakan ne yayin kadamar da sabon wajen gwajegwan chutattukan A Birnin Tarayyan Najeriya dake Abuja A ranar Talata.

 

“Wannan na’urar gwajin tarin fuka da kuke gani, zata fadada karfin Najeriya wajan gwajegwan ciwon, wanda hakan zai inganta gano chutar wajan sauki a chikin kasarku mai ban sha’awa,” A chewar sa.

 

Kwamandan Ya kara da cewa kaddamar da wannann na’urar gwajin, na nuni d juriya Da Jajarcewa Da Himma, Da Hukumar Tsaron Najeriya Ta Bangaran Gudanar Da Tsarin Lafiya Da Chibiyar Nazarin Binchike, Walter Reed, Ta Rundunar Sojan Amurka, Sukayi.

 

“Hakika am’martani da bani Hazikai Kuma Gwarazan Shuwaga banin Soja Dana Farar Hula, A nan Dan Gudanar da mahimmancin wannan lamarin.

 

“Rundunar Sojan Amurka Nada dogon tarihin lamarir’rikan starin kiwan lafiya a Kasashen ketare.

 

“Dalilin Hakan ya jawomana karin Fadada Aikinmu tagefan kare lafiya da samun wal-wala na maikatanmu dake karkadhin Rundunar Sojan Amurka tare da Jimlar Rundunar Sojojin Kasar, Dan tabbatar da zama a cikin sherin ko takwana, Akowane lokaci A kan Iya turasu Ko Ina A Duniya Wajan kare martabar kasar Amurka.

 

“Chibiyar Nazarin Binchike, Ta Rundunar Sojan Amurka, (Walter Reed Army Institute)

Nayin ayyuka, a mastayin shugaban duniya wajan nazari, da kiyaye da magance chutuka da suka hada da malaria, da HIV cuta mai karya garkuwan jiki, da Ebola da Tarin Fika.

 

“A wannan Chibiyar Ta Walter Reed Army Institute of Research, Jajartan masananmu na ilimin kimiya sun fahimci cewa kariyar lafiya itace duniya lafiya.

 

“Yau shekaru 131, sojojinmu na Chibiyar Walter Reed da ma’aikatanmu na farar Hula, sunyi aiki tukuru batare dagajiyaba Dan gwaji da Fadada fitar da kayayyakin zasu rage illar Chutattukan da ake kamuwa dasu tahanyar saduwa damakamansu.

 

“Iyalinmu na Walter Reed a cike suke da farincikin cigaba da wannan kyakyawar a’laka da mutanen Najeriya a cikin wannan mahimman Bangaran Gudanar Da binciken Chutattukan da ake kamuwa dasu tahanyar saduwa da makamantansu.

 

“Mu da ku zama tabbatar da kiwan lafiya da wal-wala a Najeriya, tare da sojojin masu mutunci dama dukkan yan Adam.”

 

Dafarko, acikin takay tataccen bayaninsa, Birgediya Janar Nathan Okeji mai murabus, Babban Daracta, a Maikatar Tsaron Najeriya Bangaran Gudanar Da Tsarin Lafiya

Ministry of Defence Health Implementation Programme (MODHIP), a cewar sa Chibiyar Nazarin Binchike Ta Sojan Najeriya an kafatane a 2012 tare da Chibiyar Nazarin Binchiken Ta Amurka, Walter Reed Army Institute of Research Africa a 2005.

 

Okay yace dangantakar ankafatane musanman dan samarda waraka ga masu chutar HIV daga cikin sojoji da iyalansu da kuma ma’ikatan farar hula dake zaune dasu dama al-uman dake makokantaka da su.

 

“Bayan lokaci mai yawa dangantaka ta dada fadada ta hanyar bada agaji wajan cutar malaria da tarin fuka da ma binchike mai zurfi.

 

“Tarin fuka ya zamo chutar da masu HIV/AIDS cuta mai kashe garkuwan jiki suke dauke da ita, tana kuma saurin kashe majinyata in har ba’a gano ta ba da wuri ba dan fara kula da majinyata.

 

“Idan tarin fuka bai samu kula da kyau ba, magungunta na bijire inganchin amfani ga majinyata. Tarin fuka ya bayyana

mahimmancin kiwan lafiya a kan cutar,” a cewar sa.

 

Babban Daracta MODHIP din ya bayyana cewa alkalumma daga hukumar kula da lafiyar jama’a ta duniya (WHO), sun nuna cewa kasashe takwas na da mafi rinjaye na masu da daukar cutar tarin fuka da kashi uku daga cikin fiyar na masu cutar a duniya.

Najeriya kuma na cikin kasashe shidda daga cikin takwas din kuma kasa ta fari a Afirka da yawan kiyasi 4.4 .

 

“Kasar Jamhuriyar Kongo na biya da kaso 2.9. Wannan alkalumman na da ban tsoro, har da yake zai iya raguwa in har an hada kai  wajan na wadanda suke da alhaki akan lamarin dan ganin an gano cutar da wuri an kuma fara bada kula wa majinyata.

 

“Tara da himma da kuma kokarin Gwajegwaje tin farko na tarin fuka daga Chibiyar (Multi-Drug Resistant (MDR), aka fara gina TBML a 2018.

 

“Da wannan kaddamar da saban wajan gwajegwan chutattuka yau, muna da yakinin azazzala karfin binchiken tarin da ma kula da majinyata da kuma bada horo tarin fuka a bisa tsarin dabarun kasa akan dakile tarin na shekara ta 2021 -2025,” a cewar Okeji.

.(NAN)(www.nannews.ng)

 

DCO/SH/BRM

============

 

Edita Sadiya Hamza

 

Fassara daga Abdullahi Mohammed/Bashir Rabe Mani

 

Wata Ƙungiya ta jaddada mahimmancin ƙidayar jama’a don cimma muradun SDGs

ƙididdiga

By Folasade Akpan

Abuja, Aug. 3, 2024 (NAN) Kungiyar Tattalin Arzikin Kasa ta Najeriya (NESG) ta jaddada muhimmancin gudanar da kidayar gidaje da yawan jama’a ta kasa domin cimma  muradun ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya (SDGs).

Babban jami’in kungiyar, Dr Tayo Aduloju, ya jaddada mahimmancin hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a ranar Asabar a Abuja.

Aduloju ya ce amintattu kuma akan lokaci da kuma bayanan alƙaluma suna da mahimmanci wajen sa ido kan ci gaban SDG.

Ya kara da cewa, kwazon da Najeriya ta samu a cikin rahoton ci gaba mai dorewa na 2024, ya nuna matukar kalubalen da ke tattare da tsarin SDG daban-daban, inda ta samu maki 54.6, inda ta zo ta 146 a cikin kasashe 167.

Ya ce “mahimman bayanai sun nuna yawan talauci, rashin abinci mai gina jiki da rage yara, tare da batun sakamakon kiwon lafiya, karancin samun ilimi da kuma rashin daidaito tsakanin jinsi.

“Rahoton SDGs ya nuna cewa kusan rabin al’ummar kasar na rayuwa cikin talauci (kashi 31.4 a kasa da dala 2.15 a kowace rana da kashi 49.0 cikin dari kasa da dala 3.65 a rana).

“Kashi 15.9 cikin 100 na rashin abinci mai gina jiki (kashi 15.9) da raguwar yara (kashi 31.5 cikin 100), dangane da sakamakon kiwon lafiya kamar yawan mace-macen mata masu juna biyu na 1,047 a cikin 100,000 da suka haihu da kuma tsawon rayuwa na shekaru 52.7 kacal.

“Samar da ilimi yana da iyaka, tare da adadin masu shiga makarantun farko na kashi 64.4, kuma daidaiton jinsi ya kasance kalubale, inda kashi 3.9 cikin 100 na kujerun majalisar dokoki ke da mata”.

Babban jami’in ya bayyana cewa ƙidayar ƙidayar na iya yuwuwar samar da ingantaccen bayanai game da alamomin SDG kusan 90, ko dai kai tsaye ko ta hanyar hasashen yawan jama’a dangane da bayanai.

Ya kara da cewa, bayanan kidayar da Najeriya ta yi a baya na kawo cikas wajen sa ido da kuma cimma manufofinta yadda ya kamata, wanda ke kawo cikas ga ci gaba mai dorewa.

Ya lura cewa “wani muhimmin al’amari da ya kamata a yi la’akari da shi shi ne jinsi da haɗa kai da jama’a. Rashin ingantattun bayanan ƙidayar jama’a yana shafar ƙoƙarin haɓaka daidaiton jinsi (SDG 5) da haɗa kai da jama’a.

“Fahimtar rarraba yawan jama’a ta hanyar jinsi yana da mahimmanci don magance bambance-bambancen jinsi, kuma ba tare da cikakkun bayanai ba, ƙoƙarin na iya kuskure ko kuma ya gaza.

“Kaddamar da SDGs game da ‘barin kowa a baya’ da ingantattun bayanan alƙaluma suna da mahimmanci don tabbatar da cewa ƙungiyoyi masu rauni kamar naƙasassu, ƙaura da waɗanda ke zaune a cikin tarkace suna samun isassun wakilci a tsare-tsaren ci gaba da manufofin.

“Ba tare da sabbin bayanai ba, an lalata yunƙurin samun ci gaba mai ma’ana da daidaito.”

Aduloju, ya bayyana cewa gudanar da kidayar jama’a na da matukar muhimmanci ga Najeriya, inda ya kara da cewa  idan aka kammala kidayar cikin lokaci kuma cikin nasara zai magance kalubale da dama.

NAN ta ruwaito cewa Najeriya ta gudanar da kidayar jama’a ta karshe a shekarar 2006.

Dangane da shawarwarin shirin aiwatar da ayyuka na taron kasa da kasa kan yawan jama’a da ci gaba (ICPD) (PoA), yakamata a sake gudanar da wani kidayar a shekarar 2016.

A shekarar 2023, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da gudanar da kidayar daga ranar 3 ga watan Mayu zuwa 7 ga watan Mayu, amma aka dage zaben, inda ake sa ran shugaba Bola Tinubu zai tsaida sabuwar ranar.

Sai dai shugaban hukumar kidaya ta kasa Alhaji Nasir Kwarra ya ce ana ci gaba da kokarin ganin an gudanar da kidayar jama’a nan ba da dadewa ba.

Kwarra ya ce hukumar ta shirya kuma tana jiran amincewar shugaban kasa don gudanar da kidayar kuri’un. (NAN)( www.nannews.ng )

FOF/TAK/HA 

Edited by Tosin Kolade/Hadiza Mohammed-Aliyu