NAN HAUSA

Loading

Shugaban kwamitin kiwon lafiya ya gargadi mata da suje gwajin ciwon daji

Shugaban kwamitin kiwon lafiya ya gargadi Mata da suje gwajin ciwon daji

Gwaji
Daga Awayi Kuje
Akwanga (Jihar Nasarawa), Satumba 19, 2024 (NAN) Mr Larry Ven-Bawa, Shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Nasarawa kan kiwon lafiya kuma memba da ke wakiltar yankin Akwanga North, ya gargadi mata da su cigaba da zuwa gwajin ciwon daji na mama da na ciki don sanin matsayinsu.

Ven-Bawa ya bada gardadin ranar alhamis a Akwanga, Jihar Nasarawa, yayin da ake bude yekuwar fadakarwar ta kwana hudu game da ciwon daji ga mata 2, 000 a gundumar Agyaga a karamar hukumar Akwanga.

Shugaban yace “ta hanyar gwajine za’a gano ciwon daji na mama saboda a ceci rayukan mata.’’

Yace za’ayi gwajegwajen a asibitin Kula da Lafiya ta Farko a yankin, ya kara da cewa “nayi tanadin magunguna, kayan aiki don ƙarfafawa tsakanin mutane, kuma a yau ina tallafa wa wannan aikin domin kare lafiyar mata.

“Zan cigaba da ba da fifiko ga lafiyar mutanen yankin Akwanga ta arewa da sauran al’umma.

“Mata da yawa sun mutu daga ciwon daji, saboda haka, ina bukatar mata su fito zuwa wannan gwaji saboda su tsare lafiyarsu.’’

Komishinan Lafiya ta Nasarawa, Likita Gwamna Gaza, da ya bude fara gwajegwajen, yace gwamnati zata cigaba da bada hankali wajen magance ciwon daji da wasu cuttuttaka a kasa.

Gaza, wanda Likita Yahaya Ubam, Sakataren Nasarawa State Health Insurance Agency (NASHIA) ya wakilta, ya yabawa Ven-Bawa saboda mahimmacin da ya baiwa lafiyar mata.

Shugabar kungiyar Mbegir Cancer Initiative, Elisha Mbegir, yace kungiyar a shirye take don kare lafiyar mata masu ciwon daji.

Ta kara da cewa gwajegwajen da za’a yi wa mata 2, 000 na kwana hudun aikin hadin gwiwa ne da kungiyar Mbegir.(NAN)(www.nannews.ng)
AKW/BRM
==========
Bashir Rabe Mani ne ya tace

Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya bukaci likitoci su cigaba da jajircewa

Shugaban kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya bukaci likitoci su cigaba da jajircewa

Likitoci

Daga Habibu Harisu

Sokoto, Satumba 14, 2024 (NAN) Manajan Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), Malam Ali M. Ali, ya bukaci likitoci da su ci gaba da jajircewa, mayar da hankali, da sadaukar da kai wajen yi wa bil’adama hidima.

Ali ya ba da wannan nasihar ne a ranar Asabar a Sakkwato a wajen bikin yaye daliban jami’ar Sudan International University (SIU) da kuma daliban Kwalejin Kiwon Lafiyar Hayat da suka karasa karstu a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato (UDUS) na shekarar 2023.

Ya kuma bukaci daliban da a ka yaye da su rike kyawawan dabi’u, kuma su rika nuna kwazo, mutunci, mutuntawa da tarbiyyar da aka cusa musu a lokacin karatunsu.

Ali ya bukace su da su dauki gwagwarmayarsu ta ilimi da muhimmanci domin tana cike da kalubale duba da irin rikicin da ya barke a Sudan a tsakiyar karatunsu.

”A matsayina na mahaifin ɗaya daga cikin waɗanda suka kammala karatun, ina jin daɗi, alfahari da gamsuwa ganin da tafiyar da aka fara da nisa ta zo ƙarshe.

”Buri ne ya cika ga ɗana, yayin da na so ya karanta Kimiyyar Kwamfuta amma ya nace ya zama Likita.

“Na tuna cewa mahaifina yana son in karanta aikin likita, amma na nace Sai  karanta aikin jarida, don haka mafarkin mahaifina ya bayyana a rayuwar jikansa, na gamsu,” in ji Ali.

Ya ce daliban da suka kammala karatun sun fuskanci kalubale domin a shekararsu ta farko da suka yi karatu, an hambarar da gwamnatin Shugaba Umar Al-Bashir, da. COVID-19 da rikicin shugabanci a Sudan.

Ya bayyana cewa, wani kalubalen da suka fuskanta shi ne kudin da suka fara a lokacin da Dalar Amurka ta kai kusan Naira 250 kuma kafin su kammala karatunsu ya kai kusan N1,300 ko sama da haka.

“Kada ku bar wani shine da zai hana ku neman nasara don ba ta zuwa da sauƙi. Kada ka bari abubuwa da yawa su datse mafarkinku da burinku.

“Ku yi amfani da ilimin da ku ka samu daga malamanku, ku fuskanci nayuwa mai kyau, don kun zama taurari masu haske kuma ku kasance masu dagewa da hidima ga ‘yanuwaku’ yan adam.

“Ba shakka cewa darussan da kuka koya a cikin karatun da kuma daga iyayenku, za su ci gaba da jagorantar ku ta hanyar rayuwa,” in ji Ali.

Wani mahaifin, Haruna Adiya, ya bayyana cewa taron ya kasance abin tunawa don ganin irin jarin da suka dukufa da kuma sadaukarwar da daliban suka yi.

A jawabinsa na bajinta, wani dalibi da ya kammala digiri, Muhammad Ali, dan shugaban NAN, ya bayyana tafiyar a matsayin kalubale.

”Wannan yana nuni da cewa muna da damar samun karin nasarori. Don zama Likitoci kwararru Kuma wanna nasarar wani kira ne don yi wa bil’adama hidima.”

Wata wacce ta kammala digiri, Sakina Mu’azu, ta yaba da sadaukarwar da Farfesoshi da sauran malamai suka yi duk da dimbin kalubalen da suka fuskanta kamar yakin Sudan a lokacin karatunsu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa akalla mutane 64 ne a ka yaye a fannonin likitanci, Pharmacy, Biomedical Engineering, Clinical Sciences da sauran kwasa-kwasai da sauransu. (NAN)(www.nannews.com)

HMH/BRM

Bashir Rabe Mani ne ya tace

Sojoji sun ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, sun kwato makamai da alburusai a Kaduna

Sojoji sun ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, sun kwato makamai da alburusai a Kaduna

Daga Tijjani Mohammad

Sojoji

Kaduna, Sept.14, 2024 (NAN) Dakarun Sector 4 Operation Whirl Punch sun kubutar da wasu mutane 13 da aka yi garkuwa da su a wani wurin masu garkuwa da mutane a karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna.

Kwamishinan tsaron gida da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Kaduna.

Aruwan ya ce “bisa bayanin da rundunar ta samu ga gwamnatin jihar Kaduna, sojojin sun mayar da martani ga sahihan bayanan sirri na ‘yan bindigar da suka yi garkuwa da wadanda aka sace a kauyen Chigulu, karamar hukumar Kachia.”

Ya ce daga baya ne sojojin suka yi hattara domin gudanar da aikin ceto a wurin da ake zargin ‘yan bindigar na da sansani.

Ya kara da cewa “dakarun sun isa wurin inda suka tunkari ‘yan fashin.

“An yi wani kazamin fada da musayar harbin bindigu a gindin wani tsauni da ke yankin.

“An fatattaki ‘yan bindigar sun gudu zuwa cikin daji, suka kuma yi watsi da wadanda suka yi garkuwa da su.

“Jami’an tsaro sun ceto mutanen 13 da aka yi garkuwa da su, wadanda suka hada da maza shida da mata bakwai daga maboyar.”

A cewarsa, sojojin sun tarwatsa sansanin, tare da lalata kayayyaki daban-daban, kamar su tufafi da abubuwan da suka shafi kayan fada a wurin.

Ya ce “an kwato wasu kayayyaki da suka hada da bindiga AK-47 guda daya, bindugu ma su linzami guda hudu, alburusai 87 7.62mm, kananan na’urorin hasken rana guda biyar, wayoyin hannu biyar da tsabar kudi N192,220.”

Aruwan ya bayyana cewa an kai wadanda aka ceto zuwa wani sansanin soji domin duba lafiyar su, kafin a sada su da iyalansu.

Ya ce Gwamna Uba Sani ya bayyana farin cikin sa da rahoton, ya yaba da yadda rundunar ta mayar da martani cikin gaggawa, karkashin jagorancin babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Najeriya/Commander Operation Whir, l Punch (OPWP), Manjo Janar Mayirenso Saraso, kuma ya taya su murnar nasarar aikin.

Ya ce gwamnan ya mika sakon fatan alheri ga wadanda aka ceto yayin da suka fatan su koma cikin iyalansu lafiya. (NAN)(www.nannews.ng)

TJ/BRM

Bashir Rabe Mani ne ya tace

Tinubu ya amince da murabus din Ngelale

Tinubu ya amince da murabus din Ngelale
Murabus
Data Salif Atojoko
Abuja, Satumba 8, 2024 (NAN) Shugaban Kasa Bola Tinubu ya amshi takardar murabus daga Ajuri Ngelale, mai magana da yawunsa kuma wakilin shugaban kasa na musamman kan harkokin yanayi, inda ya sanar da shi murabus dinsa saboda wasu dalilai na kashin kansa da kuma lafiya.
Wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar a ranar Asabar ta ce shugaban 
ya amince da dalilan murabus din Ngelale, ya fahimce su sosai tare da 
tausayawa al’amuran da suka sa ya yanke shawarar.

Yayin da yake mika addu’o’i da fatan alheri ga Ngelale da iyalansa, shugaban 
ya yi fatan samun sauki cikin gaggawa tare da samun cikakkiyar lafiya ga 
iyalansa da suka kalubalanci.

Ya lura da kokarin Ngelale da sadaukarwar da ya yi wajen yi wa kasa hidima, 
ya kuma gode masa da irin gudunmawar da ya bayar, musamman wajen ciyar 
da al’amuran kasa gaba da jagororin kokarin da ake yi kan ayyukan sauyin 
yanayi da sauran muhimman tsare-tsare.

Shugaban ya yi masa fatan alheri a dukkan ayyukansa na gaba.

A cikin wannan lokacin, muna rokon da a mutunta bukatar sirrin Cif 
Ngelale da danginsa," in ji sanarwar. (NAN)(www.nannews.ng)

SA/JPE

=========

Joseph Edeh ne ya gyara shi

Shettima ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya wajen Jana’izar mahaifiyar marigayi Yar’Adua

Shettima ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya wajen
Shettima
Daga Salisu Saniidris
Abuja, Satumba 4, 2024 (NAN) Mataimakin shugaban kasa Kashim 
Shettima a ranar Talata ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya 
domin halartar jana’izar mahaifiyar marigayi shugaban kasa,  Umaru Yar’Adua.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ya ruwaito cewa Hajiya Binta (Dada) 
Yar’Adua mai shekaru 102 ta rasu ne a ranar Litinin a Katsina kuma aka binne 
ta a can ranar Talata.

Da yake magana a madadin shugaban kasa Bola Tinubu, Shettima ya bayyana 
matukar alhinin al’ummar kasar dangane da rasuwar Hajiya Binta.

NAN ta ruwaito cewa marigayiyar ta kuma kasance mahaifiyar marigayi tsohon 
shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin tarayya, Janar Shehu Yar’adua.

Ya ce rasuwar Hajiya Binta rashi ne ba ga dangi ko jihar Katsina kadai ba, har 
ma da al’ummar kasa baki daya.

Ya yaba wa marigayin, yana mai bayyana ta a matsayin "mace mai kyan gani kuma 
kyakkyawa".

“Rashin Hajiya Binta ya shafi al’ummar kasar baki daya. Muna 
nan don jajantawa 'yan uwa kan wannan babban rashi. Ita ce 
mahaifiyarmu kuma kakarmu.

“Allah ya jikanta da rahama, ya saka mata da gidan Aljannah.

“Allah ya baiwa gwamnati da iyalai da al’ummar jihar Katsina 
karfin gwiwar jure wannan rashi da ba za a iya maye gurbinsa ba,” 
inji shi.

Tun da farko dai Sanata Abdulaziz Yar’adua, dan marigayiyar, yay mahaifiyarsa ya yabawa gwamnati domin karramawa.

Yace "mahaifiyarmu ta kasance misali mai haske na alheri da tausayi. 

“Rayuwarta shaida ce ga kimar aiki tukuru, sadaukarwa da hidima ga dan adam.

“A matsayinta na Musulma mai kishin addini, ta yi rayuwa ta bangaskiya, 
a koda yaushe tana neman yardar Allah.

"Rasuwarta ta bar wani gibi da ba za a taba cikawa ba, amma muna samun 
ta'aziyya da sanin cewa ta yi rayuwa mai gamsarwa kuma ta bar gadon 
soyayya, alheri da karamci.(NAN)(www.nannews.ng)

SSI/ETS

Ephraims Sheyin ne ya gyara

 Shettima ya goyi bayan laccar tsaro ta yankin Sahel da NAN zata shirya

 Shettima ya goyi bayan laccar tsaro ta yankin Sahel da NAN zata shirya


Tsaro
Daga Salisu Sani-Idris
Abuja, Satumba 2, 2024 (NAN) Mataimakin shugaban kasa Kashim 
Shettima a ranar Litinin ya yi kira da a kara bayar da tallafi 
ga lacca ta kasa da kasa kan rashin tsaro a yankin Sahel.

Shettima ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin 
shugabannin kamfanin dillancin labarai ta Najeriya (NAN) a 
karkashin jagorancin Manajan Daraktanta, Malam Ali Muhammad Ali, 
a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Mataimakin shugaban kasar ya jaddada muhimmancin hada kai, 
inda ya bayyana cewa shugaba Bola Tinubu na matukar sha’awar 
sha’anin tsaro a Najeriya, kuma ba zai dauki matakin da wasa ba.

Shettima ya kuma yi kira da a yi kokari na shiyya-shiyya da na 
gamayya don magance matsalar rashin tsaro a yankin Sahel na 
yammacin Afirka.

Ya lura cewa yanayin tsaro a yankin Sahel yana da matukar tasiri 
ga Najeriya da kuma kasashe makwabta.

Lakca ta kasa da kasa da NAN ke shirya ya dace sosai, musamman 
kan batun rashin tsaro a yankin Sahel.

“Matsalar tsaro a cikin al’umma abu ne da shugaban kasa ke 
matukar sha’awa kuma ba ya daukar matakin da sauki,” inji shi.

Shettima ya bayyana kwarin guiwar sakamakon taron.

Ya ce"Na yi imanin cewa tare da kimar mutanen da za su yaba da 
lacca, za ku fito da ra'ayoyi da dama kan yadda za a magance 
matsalar rashin tsaro a yankin Sahel ta hanyar da ta dace."

Tun da farko, Ali ya shaida wa mataimakin shugaban kasa 
Shettima cewa, taken taron shi ne "Rashin tsaro a yankin 
Sahel (2008-2024): Rarraba kalubalen Najeriya - Asali, Illoli da hanyoyin zabi".
Ya sanar da cewa, wanda zai jagoranci laccar da za a yi a ranar 
25 ga watan Satumba, shi ne Mohamed Ibn Chambas, tsohon 
shugaban hukumar ECOWAS.

A cewar sa, taron wani bangare ne na kokarin da NAN ke yi na 
fadada rawar da ta ke takawa fiye da yada labarai don ba da 
gudummawa sosai wajen tattaunawa kan kasa da magance matsalolin.

"NAN ta shirya lacca ta farko ta kasa da kasa a matsayin 
wani bangare na rawar da kafafen yada labarai ke takawa na 
fadada iyakokin ilimi da samar da hanyoyin magance matsaloli," 
in ji Ali.

Ya zayyana tsare-tsare da dama da ke da nufin inganta isar 
da sahihancin NAN, ciki har da bullo da yada shirye-shiryen 
yare.

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da Daraktan 
gudanarwa na NAN, Malam Abdulhadi Khaliel; Daraktan ayyuka 
na musamman, Muftau Ojo; Mataimakin Darakta na NAN kafofin yada labarai na zamani, 
Ismail Abdulaziz; da Sakatariyar hukumar, Ngozi Anofochi.
(NAN)(www.nannews.ng)

SSI/AMM

======

Abiemwense Moru ne ta gyara

Hajiya Dada, mahaifiyar marigayi Shugaba ‘Yar’aduwa, ta rasu

 

Hajiya Dada, mahaifiyar marigayi Shugaba 'Yar'aduwa, ta rasu   

Hajiya Dada
Daga Zubairu Idris
Katsina, Satumba 2, 2024 (NAN) Mahaifiyar marigayi shugaban kasa 
Umaru Musa Yar’adua, wacce aka fi sani da Hajiya Dada ta rasu.

Hajiya Dada ta rasu ne a ranar Litinin bayan ta yi fama da 
rashin lafiya. Tana da shekaru 102.

Daya daga cikin ‘ya’yanta, Suleiman Musa-Yar’adua, ya sanar da 
rasuwar ta ranar Litinin a Katsina.

Hajiya Dada ta bar ‘ya’ya da yawa da jikoki da jikoki.

Daga cikin ‘ya’yanta akwai Sanata mai wakiltar Katsina ta 
tsakiya mai wakiltar mazabar Katsina ta tsakiya, Sen. 
Abdulaziz Musa-Yar’adua.

An shirya gudanar da sallar jana'izarta a ranar Talata da 
karfe 1:30 na rana. (NAN)(www.nannews.ng)
ZI/BRM
==========
Bashir Rabe Mani ne ya gyara

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya na taka muhimmiyar rawa fagen yada labarai — Shettima 

Kamfanin Dillancin L

Manajan Darakta / Shugaba, NAN

abarai na Najeriya na taka muhimmiyar rawa fagen yada labarai — Shettima 

NAN

Daga Salisu Sani-Idris

Abuja, Satumba 2, 2024 (NAN) Mataimakin Sugaban kasa Kashim
Shettima ya kamanta Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a matsayin mai taka muhimmiyar rawa a fagen yada labarai.

Shettima ya bayyana haka ne a wajen wani taro da mahukuntan NAN, karkashin jagorancin Manajan Daraktanta, Malam Ali Muhammad Ali, a fadar shugaban kasa a ranar Litinin a Abuja.

Mataimakin shugaban kasar ya kuma bayyana cewa hukumar na taka rawar gani wajen dinke barakar bayanai da kuma tsara yadda za a tattauna batutuwan da suka shafi kasa.

Ya kara da cewa, “NAN na taka muhimmiyar rawa a fagen yada labarai na Najeriya, tare da taimaka wa wajen dinke barakar bayanai da kuma tsara maganganun jama’a kan al’amuran kasa.

“Hukumar ita ce babbar mai samar da abun ciki a nahiyar Afirka.”

”Har yanzu kuna da muhimmiyar rawar da za ku taka domin dukkanmu muna rayuwa kuma muna aiki a duniya bisa hanyoyin sadarwa.

“Ta hanyar sadarwa muke tsara ra’ayin jama’a; ta hanyar sadarwa muna gina gadoji na fahimta da ‘yan uwantaka.”

Shettima ya bayyana nadin Ali da Shugaba Bola Tinubu ya yi a matsayin Babban shugaban na NAN a matsayin “kwargin murabba’i a cikin ramin murabba’i.”

Babban shugaban, NAN, Malam Ali Muhammad Ali, yana mukawa Shettima wata kyauta a wurin taron .
Ya kuma bayyana Ali a matsayin gogaggen dan jarida wanda ya taso a harkar yada labarai, yana mai cewa “Gaskiya na ji dadi matuka lokacin da aka nada ka MD na Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya.

Ya ce, "Kai ƙwararren ƙwararren ƙwararrene kuma kana da tarihin 
magabata masu kyan gani.

“Don haka, a shirye muke mu yi mu’amala da maiikatar ku ku ta kowace 
hanya da kuke ganin ya kamata mu taka rawa kuma taron kasa da 
kasa da kuke shiryawa yana da kyau sosai.

“Musamman, batun da kuke ta faman yi a kai; rashin tsaro a 
yankin Sahel, a gaskiya matsalar rashin tsaro a kasar abu ne 
da ke tada hankalin Shugaba Bola Tinubu.

"Na yi imani tare da kimar mutanen da za su halarci wannan 
taron, za mu fito da batutuwa da dama, da ra'ayoyi da dama kan 
yadda za a magance matsalar rashin tsaro a yankin Sahel ta 
hanyar da ta dace, ba wai kawai ba."

Tun da farko, Ali ya shaida wa mataimakin shugaban kasar cewa 
ziyarar tasu ita ce domin jin ta bakinsa game da shirin lacca 
na farko na hukumar.

“A cikin wasikar da muka aike muku, mun ba ku fahimtar abin 
da laccar ta kunsa, ita ce irinta ta farko cikin kusan shekaru 
50 da kafa hukumar.

Ali yace, “Wannan shi ne karon farko da ake shirya lacca mai girman gaske 
a matsayin wani bangare na nauyin da ya rataya a wuyan kafafen 
yada labarai na bayar da gudunmawa da fadada iyakokin ilimi, 
don ba da gudummawa ga bangaren ilimi da nufin samar da mafita.

Taken lacca shine rashin tsaro a yankin Sahel (2008-2024): 
Rarraba kalubalen Najeriya — Farawa, Tasiri da Zabuka, da 
abin da ke akwai ga Najeriya.

Ali ya bayyana cewa, wanda ya jagoranci laccar da aka shirya 
shi ne wanda ya kware kan harkokin tsaro, tsohon shugaban 
ECOWAS, Mohamed Ibn Chambas.
Yace, "Tuni tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya amince ya zama 
shugaban taron.

“A safiyar yau ne Sarkin Musulmi ya tabbatar da kasancewarsa a 
ranar 25 ga watan Satumba a matsayin uban gidan sarauta.

"Daga cikin manyan manyan baki da ake sa ran akwai Oni na Ife, 
Obin Onitsha da sauran su."

Shubaban NAN din ya ba da tabbacin cewa hukumar ba ta rayuwa ba don 
samun nasarar gudanar da lacca ta duniya.

Ya ce hukumar da ke karkashinsa ta samu wasu gaggarumin ci gaba.

“Tun da muka karbi ragamar mulki watanni biyu da suka gabata, daya daga cikin wadannan shi ne mun fara watsa shirye-shirye a daya daga cikin manyan harsunan kasar nan.

"Mun fara tashar tashar Hausa ta harshen na hukumar kwanaki biyu da suka gabata, muna fatan kafin shekarar ta kare, a mafi akasarin nan da kwata na farko na shekarar 2025, manyan harsuna uku za su bayyana a cikin shirye-shiryen da ake yadawa a fadin kasar."

Ali ya kara da cewa hukumar na aiki tukuru domin sake bude wasu ofisoshinta da aka rufe, musamman a Turai.

“Daya daga cikin wadannan yana da matukar muhimmanci, tare da goyon bayan ku, yallabai, muna fatan sake bude ofishinmu na Landan.

“Kamar yadda kuka sani, Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ita ce babbar mai samar da labarai a nahiyar Afirka. Muna da masu biyan kuɗi da yawa da abokan hulɗar manyan gidajen watsa labarai na duniya." (NAN)

SSI/IS
=======
Ismail Abdulaziz ne ya'' gyara

 

 

 

 

Tinubu ya taya Shettima murnar cika shekaru 58 da haihuwa 

 

Tinubu ya taya Shettima murnar cika shekaru 58 da haihuwa 

Taya murna 
By Salif Atojoko 
Abuja, Satumba 2, 2024 (NAN) Shugaban kasa Bola Tinubu a ranar 
Litinin ya taya mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima murnar 
cika shekaru 58 da haihuwa.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale, shugaban 
kasar ya fitar, ya bayyana Shettima a matsayin malami, kwararren 
ma’aikacin banki, ma’aikaci kuma shugaba.

Shettima ya kasance Gwamnan Borno daga 2011 zuwa 2019 sannan 
kuma Sanata mai wakiltar Borno ta tsakiya daga 2019 zuwa 2023.

“Shugaba Tinubu yana hada kai da ‘yan uwa, abokai, da ‘yan 
majalisar zartaswa na gwamnati don yin bikin babban mai 
gudanarwa, mai magana, da bibliophile a wannan lokaci na 
musamman.

"Shugaban ya yabawa Shettima saboda himma da kuma 
hazaka da yake kawowa kan mulki.

“Shugaba Tinubu ya godewa mataimakin shugaban kasar bisa 
goyon bayan da ya ke bayar wa tare da yi masa fatan samun lafiya 
da kuma karin karfin da zai yi wa kasa hidima,” in ji Ngelale. (NAN) (www.nannews.ng)

SA/JPE

=====

Joseph Edeh ne ya gyara shi

Shettima ya bayyana samuwar zuba jarin dala biliyan 4.8 a fannin kiwon lafiya

Shettima ya bayyana samuwar zuba jarin dala biliyan 4.8 a fannin kiwon lafiya

Lafiya
Daga Salisu Saniidris
Abuja, Agusta 31, 2024 (NAN)Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ta yi a fannin kiwon lafiya ya janyo sama da dala biliyan 4.8 a bangaren zuba jari.