Jihar Kaduna ta fadada hanyoyin karkara domin bunkasa noma

 

Hanya

 

By Mustapha Yauri

 

Zaria (Jihar Kaduna) Satumba 8, 2025 (NAN) Gwamnatin jihar Kaduna ta fara aikin gina titunan karkara a fadin jihar domin bunkasa harkokin noma a jihar.

Yunkurin dai na nufin saukaka zirga-zirgar kayan amfanin gona, tare da inganta kasuwannin manoma da kuma karfafuwar samar da abinci a fadin jihar.

Babban sakataren ma’aikatar noma, Alhaji Umar Abba ne, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a Zariya, cewa, shirin na da nufin rage asarar da ake samu bayan girbi.

Ya ce, gwamnatin Gwamna Uba Sani, ta jajirce wajen samar da hanyoyin shiga karkara, domin karfafa ayyukan noma da bunkasa zamantakewa da tattalin arziki, tare da ci gaban al’umma baki daya.

Abba ya kara da cewa, shirin na hadin gwiwa ne tsakanin bankin duniya da gwamnatin jihar Kaduna, a karkashin shirin samar da ayyukan noma na karkara (RAAMP).

Babban sakataren ya ci gaba da cewa, a kwanakin baya ma’aikatar ta gudanar da ziyarar gani da ido, a kashi na biyu na wasu al’ummomin da suka ci gajiyar ayyukan hanyoyin.

Sakataren ya bukaci ‘yan kwangila, da su kammala ayyukan cikin gaggawa tare da kiyaye ka’idoji.

Hakazalika, Ko’odinetan ayyukan, Malam Zubairu Abubakar, ya zayyana wasu daga cikin ayyukan hanyoyin da ake gudanarwa a matakai daban-daban.

Ya ce sun hada da tituna Sama da kilomita 50 na Fala zuwa Sayasaya, Masama Gadas zuwa Anchau Road a karamar hukumar Ikara.

Sauran in ji shi, sun hada da titin Gora zuwa Kwoi, mai tsawon kilomita 3.5 a karamar hukumar Jaba, sannan titin Aduwan Gida zuwa Fadan Kaje mai nisan kilomita 5.6 a Zonkwa.

Akwai kuma na karamar hukumar Zangon Kataf da titin Illa zuwa Kofato, mai kilomita 13.4 a karamar hukumar Igabi da titin Sabon Tasha zuwa Juji zuwa Unguwar Barde da sauransu.

A cewar mai gudanar da aikin, duk ayyukan hanyoyin shiga karkara karkashin RAAMP, za a kammala sune a karshen shekarar 2025.

Don haka, ya yi kira ga mazauna yankin da masu amfani da hanyoyin, da su ci gaba da bada hadin kai ga ‘yan kwangilar, domin kammala da ayyukan cikin sauki da kuma dace. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AM/KLM

Fassarar Aisha Ahmed

 

Al’ummar Adamawa sun koka da barkewar bakuwar cuta

Daga Ibrahim Kado

Fufore (Adamawa), Satumba 5, 2025 (NAN) Mazauna garin Malabo a karamar hukumar Fufore ta jihar Adamawa, sun nuna damuwarsu kan barkewar wata bakuwar cuta da ke damun sassan jiki tare da haifar da radadi mai tsanani.

Wasu majinyata da suka zanta da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Malabo a ranar Juma’a, sun ce cutar kan fara ne kamar borin jiki, daga baya kuma sai ta watsu, kuma a hankali tana cin naman jiki tare da lalata kasusuwa.

Misis Phibi Sabo, ta ce ta shafe makonni tana fama da cutar.

“Abun ya fara kamar borin jiki mai zafi, daga baya ya kumbura ya fashe, sa’an nan ya fara cinye naman da ke kafada, yana lalata kasusuwa kuma ya jawo mun ciwo mai tsanani.

“Hakan ya sa ni rauni a fili, ba zan iya bayyana abin da ke faruwa da ni ba, duk da cewa na ziyarci asibiti kuma na sami magunguna,” in ji Sabo.

Ta yi kira ga gwamnati da tallafa, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin majinyata ba za su iya yin ayyukansu na yau da kullum ko kuma tallafa wa iyalansu ba.

“Don Allah, muna son taimakon gwamnati kafin al’ummarmu ta salwanta,” Sabo ya yi kuka.

Ta kuma jaddada bukatar gwamnati ta binciki musabbabin cutar, tare da samar da kayan agaji ga gidajen da lamarin ya shafa.

Wani da abin ya shafa, Malam Junaidu Adamu, shi ma ya ce ya shafe sama da watanni biyu yana fama da irin wannan ciwon, ya bayyana irin wadannan alamomin.

“Kimanin watanni biyu da suka wuce bayan na dawo daga gona, sai na ji zafi a kafata, sai ta fara kamar borin jiki, sai ta fashe ta bazu har namana ya fara rubewa.

“Ina kashe kimanin Naira 25,000 a mako-mako wajen sayen magunguna, amma idan na sha, sai ya kara tsananta yanayin.

“Yanzu matata tana gida don ta kula da ni da yaran, wanda hakan ya shafi rayuwarmu,” in ji shi.

Adamu, ya kuma roki gwamnati da ta gaggauta kawo dauki kafin cutar ta yadu zuwa ga sauran al’umma.

Da yake tabbatar da lamarin, Hakimin Malabo, Alhaji Aliyu Hammawa, ya ce akalla mutane 30 ne abin ya shafa.

Ya ce a halin yanzu mutane takwas daga ciki suna karbar magani a asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama (MAUTH) a Yola, yayin da wasu kuma ke samun kulawa a cibiyar kula da lafiyar al’umma.

Ya kuma yabawa gwamnatin jihar, bisa gaggauta daukar matakin da yi, tare da yin kira da a gaggauta gudanar da bincike don gano musabbabin cutar.

Shima da yake tabbatar da bullar cutar, Shugaban Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Adamawa, Dakta Suleiman Bashir, ya ce hukumar tare da hadin gwiwar karamar hukuma, ta dauki nauyin mutane 28 da suka kamu da cutar.

Ya tabbatar da cewa mutane takwas ne kawai suka karbi magani.

Dakta ya kara da cewa, gwamnatin jihar ta riga ta biya kudin jinyar wasu a MAUTH, yayin da aka dauki samfuri domin yin gwaji.

“Ana sa ran sakamako a cikin kwanaki 10 masu zuwa. Muna kira ga wadanda abin ya shafa, da su karbi magani maimakon dogaro da magungunan gargajiya,” in ji shi.

Bashir ya bukaci mazauna yankin, da su gaggauta kai rahoton yanayin duk wani rashin lafiya da ba a saba gani ba, zuwa ga cibiyoyin kiwon lafiya don tantancewa da kyau (NAN) IMK/TIM/YMU

Edited by Yakubu Uba

 

Fassarar Aisha Ahmed

‘Yan sanda na bincike kan harin da aka Kaiwa tawagar Malami a Kebbi

Daga Ibrahim Bello

Birnin Kebbi, Satumba 2, 2025 (NAN) Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta fara gudanar da bincike kan harin da aka kaiwa ayarin motocin tsohon ministan shari’a kuma babban lauya Abubakar Malami (SAN), a Birnin Kebbi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa an kaiwa ayarin motocin Malami hari ne a ranar Litinin, a lokacin da suke dawowa daga ziyarar jaje a babban birnin jihar.

Malami ya fice daga jam’iyyar APC ne a ranar 2 ga watan Yuli, sannan ya koma jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Bayan wani taron gaggawa da jami’an tsaro suka yi da jami’an tsaro, kwamishinan ‘yan sanda, Mista Bello Sani, ya tabbatar da cewa ba a kama kowa ba.

“Mun fara bincike kan harin, kuma ba a kama wani mutum ba tukuna, ya kara da cewa Gwamnan Kebbi, ya kira wannan taro ne domin duba abubuwan da suka shafi tsaro,” in ji Sani.

Sani ya kara da cewa, al’amarin ya faru a kewayen yankin GRA da suka shafi ‘yan jam’iyyun siyasa, wadanda ke da alaka da saba ka’idojin yakin neman zabe na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Kwamishinan ya bayyana cewa, za a gayyaci shugabannin jam’iyyun siyasa tare da gargadinsu akan sabawa ya ka’idojin zabe.

Ya jaddada cewa za a dauki matakai,  da nufin hana afkuwar tashin hankali yayin da zaben da ke kara kusantowa.

Kwamishinan ya kuma bukaci shugabannin siyasa a Kebbi, da su kwantar da hankalinsu da kuma tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar. (NAN) (www.nannews.ng)

IBI/KTO

======

Fassarar Aisha Ahmed

Kungiyar IPMAN za ta dabbaka ingancin man fetur a fanfunan gidajen mai 

IPMAN

Daga Stanley Nwanosike

Enugu, 25 ga Agusta, 2025 (NAN) Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya (IPMAN), ta ce tana shirin dabbaka ingancin famfun mai a gidajen mai, ta hanyar magance magudi da kuma munanan ayyuka.

Shugaban kungiyar IPMAN reshen Jihar Enugu, Cif Chinedu Anyaso, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi a Enugu, jim kadan bayan kammala babban taron kungiyar(AGM), na shekarar 2025.

Sashen Enugu na IPMAN, ya kunshi masu sayar da man fetur masu zaman kansu a jihohin Enugu, Anambra da Ebonyi, da kuma wasu sassan jihohin Abia, Imo, Kogi da Cross River.

Anyaso, ya ce mambobin kungiyar, sun amince gaba daya a taron AGM, kan a tabbatar da ingancin famfunan mai, domin tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun ci moriyar kudadensu.

Ya jaddada cewa, IPMAN ta himmatu wajen daukaka martabarta wajen hidima da ingancin kayayyaki, inda ya kara da cewa: “IPMAN ta kuduri aniyar kafa wata rundunar da za ta tabbatar da bin dukkanin mambobinta.

“Wannan ya zama dole ne domin ingantaccen aikin samar da wutar lantarki.”

A cewarsa, za a kaddamar da kwamitin ne a watan Satumba mai zuwa, kuma za a gudanar da ayyukan ne ta hanyar kwazo a kowace jiha dake karkashin wannan runduna.

“Domin a tsaftace tsarin da kuma tabbatar da cewa an kiyaye martabar kungiyar IPMAN da gidajen man ‘ya’yanmu, mambobin kungiyar a lokacin taron kungiyar, sun amince da cewa dole ne a dakatar da magudi da kuma munanan ayyuka.

“IPMAN za ta kafa wani kwamiti na aiki na yau da kullun nan ba da jimawa ba, yayin da mambobin kungiyar baki daya suka amince da a ci tarar kudi mai yawa, tare da sanya takunkumi ga duk wani gidan mai da ya gaza mallakar kowane memba,” inji shi.

Ya kuma bayyana cewa, kungiyar ta kuduri aniyar yin tsayin daka wajen tunkarar matsalar, ta hanyar ladabtarwar cikin gida; kamar yadda kungiyar ta kawar da gurbataccen man fetur.

Shugaban kungiyar, ya bayyana cewa, kungiyar IPMAN Enugu, ta kuma yaba da irin nasarorin da gwamnoni da gwamnatocin jihohi daban-daban suke yi kan ayyukan raya kasa musamman hanyoyin mota da na tsaro a jihohin yankin.

“Mun samu kwarin guiwa da jajircewar gwamnonin, wajen ci gaba da samar da ingantaccen yanayin kasuwanci da kuma samar da titina na kayayyakin man fetur, don isa ga kowane lungu da sako na sashin,” in ji shi.

Anyaso, ya tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun amince baki daya cewa za su sake rubutawa Gwamna Chukwuma Soludo na Anambra takarda, kan batun IGR na gidajen mai a Anambra.

“Mun yaba masa kan tattaunawar da aka yi zuwa yanzu; duk da haka, muna kira ga duk masu ruwa da tsaki, da su zo kan teburin tattaunawa, don warware sabanin da ke tsakaninsu, su yi sulhu cikin lumana domin amfanar kowa da kowa,” in ji shi.

Shugaban ya ce, mambobin kungiyar sun kuma yanke shawarar sake rubutawa Gwamna Soludo takarda kan bashin sama da Naira miliyan 900 da ake bin mambobin kungiyar IPMAN da suka samar da dizal don gudanar da fitilun tituna a jihar.

“Gwamnatin Jihar Anambra ta ci basuka tun shekara daya da ta wuce, duk da wasiku da kiraye-kirayen kai-tsaye har sau uku ga Gwamna da Jami’an Jihar da abin ya shafa, har ya zuwa yanzu ba a yi komai ba.

“Muna bin hanyar diflomasiyya tunda ba ma son mu umurci mambobinmu da su shiga yajin aiki ko kuma su daina sayar da albarkatun man fetur, domin hakan zai kara sanya talakawa a wahala da kuncin rayuwa.

“Idan ‘yan kungiyar IPMAN suka tafi yajin aiki, a bayyane yake cewa litar man fetur na iya haura kusan N2,000 zuwa N3,000 a jihar, baya ga sauran illolin da wannan yunkuri zai haifar.

“Duk da haka, muna son gwamnatin jihar ta saurari kokenmu da kuma halin da ‘yan kungiyarta IPMAN ke ciki, wadanda suka samar da kayayyaki kuma a halin yanzu suna bin cibiyoyin kudi.”

Anyaso ya jaddada cewa, a cikin ‘yan watanni ‘yan kungiyar IPMAN din guda takwas a Anambra, wadanda suke bin gwamnatin jihar bashi sun mutu sakamakon damuwa da kaduwa, domin matsin lamba da hukumomin kudi ke yi, na neman a biya su lamuni mai tsanani.

“Wasu daga cikin cibiyoyin hada-hadar kudi sun karbe tashoshinsu, wasu kuma tuni aka rufe wasu da dama kuma sun kori ma’aikatansu saboda gazawar kudi,” inji shi.

Shugaban ya kara da cewa, mambobin sun kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi walwala, ingantattun hanyoyin da za a bi wajen daga man fetur da yadda za a yi shirin sayar da kayayyaki.

Kamar yadda ya fada, yace za a fito da shiri don isar da kayayyakin Dangote kai tsaye da kuma shirin samar da man fetur da iskar Gas na JEZCO don taimakawa mambobin.

A taron, an gabatar da jawabai daga hukumar harajin cikin gida ta tarayya, kan shigar da harajin lantarki, da kuma ta TradeGrid Limited kan yadda za a saukaka ayyukan sanya wutar lantarki mai amfani da hasken rana a gidajen mai, da dai sauran batutuwa. (NAN) ( www.nannews.ng )

 

KSN/KO

Fassarar Aisha Ahmed

‘Yan majalisa sun koka kan rashin tsaro a Nasarawa

Tsaro

By Awayi Kuje

Lafia, Aug. 22, 2025 (NAN) Majalisar Dokokin jihar Nasarawa, ta ja hankulan jama’a game da karuwar matsalar rashin tsaro a jihar, musamman masu garkuwa da mutane.

Dokta Danladi Jatau, kakakin majalisar ne ya bayyana hakan a bayan da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Lafia ta tsakiya, Mista Solomon Akwashiki, ya tabo batun.

Akwashiki, ya tabo batun da ya shafi bukatun jama’a a domin jaddada zaman majalisar a Lafiya.

Shugaban majalisar ya yi kira ga hukumomin tsaro a jihar, da su yi amfani da dokar yaki da garkuwa da mutane da majalisar ta kafa domin dakile satar mutane a jihar.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda ake hada baki da masu satar mutane a yi garkuwa da mutane, yana mai nuna damuwa cewa jihar na zama cibiyar garkuwa da mutane.

“Kudirinmu na haka ne, muna kira ga gwamnan jihar, da ya umarci jami’an tsaro su kara karfafa tsaro a fadin jihar.

“Na biyu, muna umurtar jami’an tsaro da su yi amfani da dokar da wannan majalisa ta kafa, wajen dakile garkuwa da mutane.

“Na uku, muna kira ga mazauna yankin da su kai rahoton duk wani motsi da ayyukan daidaikun mutane ga jami’an tsaro, don daukar mataki,” in ji kakakin.

Tun da farko, Mista Akwashiki, mamba mai wakiltar mazabar Lafia ta tsakiya, ya nuna damuwa akan cewa Lafia, babban birnin jihar Nasarawa ba shi da mafaka, sakamakon ci gaba da yin garkuwa da mutane.

“Mai girma shugaban majalisar, idan Lafia ba ta da lafiya ina kuma za a samu lafiya?

“Wadannan masu garkuwa da mutane suna ta kai hare-hare, suna barna ba tare da wata tangarda ba, dole ne mu tashi kafin lokaci ya kure,” in ji Akwashiki.

Shima da yake bayar da gudunmawarsa, Daniel Ogazi (APC-Kokona Gabas) ya tunatar da majalisar cewa majalisar dokokin jihar ta zartar da dokar yaki da garkuwa da mutane.

“Dokar da wannan majalisa ta kafa ta tanadi cewa idan aka kama mai garkuwa da mutane, a kawar da shi ko ita, wannan yana aiki, amma ba mu san abin da ya faru daga baya ba,” in ji Ogazi.

Da suke bayar da gudunmawa, shugaban masu rinjaye na majalisar, Mista Suleiman Azara, Mista Esson Mairiga (PDP-Lafia North) da kuma Mista Mohammed Omadefu (APC-Keana), sun bukaci hukumomin tsaro da su canza salon dakile satar mutane. (NAN) (www.nannews.ng)

 

AKW/BEKl/COF

Fassarar Aisha Ahmed

Kwamitin majalisar wakilai ya yaba da sake fasalin kiwon lafiya a jihar Jigawa

Kwamitin majalisar wakilai ya yaba da sake fasalin kiwon lafiya a Jigawa

Lafiya

Daga Aisha Ahmed 

Dutse, Aug. 22, 2025 (NAN) Kwamitin majalisar wakilai mai kula da harkokin kiwon lafiya, ya yabawa gwamnatin jihar Jigawa bisa bullo da sabbin tsare-tsare masu inganci a fannin kiwon lafiya. 

Shugaban kwamitin, Mista Amos Gwamna-Magaji, ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi,;a Dutse.

Ya yaba da irin nasarorin da aka samu a shirin kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, musamman kashi 15 na kasafin kudin da aka ware wa fannin.

“Muna alfahari da farin cikin jin cewa sama da kashi 15 cikin 100 na kasafin kudi na shekara bana, don kiwon lafiya ne, wanda abin mamaki ne kuma ya yi tasiri.

“Duk da haka, mun kuma ga cewa sama da kashi 15 cikin 100 na kasafin, ba a takarda kawai yake ba, kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin na yawo tare da sauya yanayin kiwon lafiya yadda ya kamata a jihar Jigawa,” inji shi.

Gwamna-Magaji ya taya gwamnan murnar samun kyautar kudi sama da dala 500,000 na PSC Leadership Challenge Award da jihar ta samu.

Yana mai bayyana hakan a matsayin hujjar daukakar kimarsa a garambawul na kiwon lafiya. 

“Wannan ya nuna jajircewar ku da kuma matsayin da kuka kai, da kuma abin da kuka yi a fannin lafiya,” in ji shi.

Shugaban ya kuma yabawa gwamnatin jihar, kan yadda aka daidaita albashin ma’aikatan lafiya da ma’auni na tarayya.

Ya kara da cewa, wannan wani gagarumin mataki ne na magance dakilewar kwakwalwar kwararrun likitoci.

Da yake mayar da martani, Namadi ya sake jaddada kudurin sauya fannin kiwon lafiya zuwa ga cimma nasarar da ake samu na kula da lafiya ta duniya (UHC) a jihar.

 A cewar Namadi, kiwon lafiya shine tushen ci gaban zamantakewa da bunkasar tattalin arziki da ci gaban al’umma. 

“Mun yi imanin cewa al’umma mai koshin lafiya al’umma ce mai ci gaba, tare da lafiya ne kawai za ku nemi ilimi, kuma ku bunkasa harkokin tattalin arziki don inganta tattalin arziki,” in ji shi.

Ya ce gwamnatinsa ta gudanar da bincike na kwakwaf, don jagorantar tsare-tsare da ba da fifiko a dukkan bangarori, tare da kula da lafiya a matsayin fifiko.

Namadi ya ce jihar ta mayar da hankali ne wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko, da ke zama ginshikin samar da ingantaccen sabis. 

“Dole ne a karfafa kiwon lafiya na farko don samar da lafiya ga mutane. Mun tabbatar akwai bukatar samar da cibiyoyin kiwon daga tushe, inda ma’aikata da ‘yan ƙasa za su yi farin ciki,” in ji shi. 

Gwamnan ya bada tabbacin aniyar gwamnatin sa na zurfafa sauye-sauyen harkokin kiwon lafiya domin cimma nasarar UHC. (NAN) (www.nannews.ng)

 

 AAA// RSA 

Fassarar Aisha Ahmed

Hukumar Kwastam ta kama miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai N690m a Katsina

 

Magunguna

Daga Abbas Bamalli

Katsina, Aug. 19, 2025 (NAN) Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta ce hukumar kwastam ta Najeriya ta kama miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai kimanin Naira miliyan 690.

Rundunar ta ce sun tare wasu motoci guda biyu da ke dauke da kayayyakin.

Shugaban hukumar NCS a jihar, Mista Idriss Abba-Aji, ne ya bayyana hakan a Katsina ranar Talata, yayin da yake zantawa da manema labarai kan kama magungunan.

A cewarsa, jami’an ‘yan sanda sun kama katan 14 na Tramadol da kudinsu ya kai Naira miliyan 650 da kuma kafsul din Fragbaline na Naira miliyan 28, wadanda aka boye a cikin motoci daban-daban guda biyu.

Ya bayyana cewa an kama su ne a cikin makonni biyu, ya kara da cewa jami’an sun kwace tabar wiwi na kimanin naira miliyan 15.

“A ‘yan kwanakin nan, mun lura cewa ana amfani da iyakokinmu wajen safarar miyagun kwayoyi, ana amfani da motoci da wayo don rikitar da jami’an tsaro da ke cin karo da su.

“Kuna iya lura irin wadannan motoci na jigilar manyan mutane ne, jama’a su fahimci cewa a yayin gudanar da ayyukanmu, muna dakatar da duk wata mota don tabbatar da an duba lamarin.

“Mutane na korafin yadda kwastam ke damun masu ababen hawa, masu safarar muggan kwayoyi ba za su taba amfani da manyan motoci ko bude motoci ba.

“Suna boye muggan kwayoyi a cikin motocin da aka kera,” in ji Kwanturolan.

Ya jaddada cewa jami’an ba za su iya gano irin wannan boye-boye ba tare da tsayawa da bincike ba. A cewar sa, sun yi sa’ar kwace motoci biyu a lokuta daban-daban.

Abba-Aji ya lura cewa kowace mota na dauke da muggan kwayoyi masu yawa, wadanda ake zargin ana raba su a cikin Katsina da jihohin da ke makwabtaka da su idan ba a kama su ba.

“Kwanan nan, a daya daga cikin iyakokinmu, mun kama miyagun kwayoyi, musamman Tramadol, a cikin kwali 14 da kudinsu ya kai kimanin Naira miliyan 650.

“Wannan ne laifi mafi girma irinsa ga wannan rundunar,” in ji Abba-Aji.

 Ya ci gaba da cewa shaye-shayen miyagun kwayoyi na rura wutar rikicin ‘yan fashi a yankin.

Don taimakawa wajen dakile wannan barazana, rundunar ta kara kaimi wajen aiwatar da ayyukan ta.

A cewarsa, an kama mutum daya da ake zargi tare da daya daga cikin motocin, amma daga baya aka sake shi akan beli. (NAN) (www.nannews.ng)

AABS/KTO

 

Fassarar Aisha Ahmed

An gudanar da zaben cike gurbi cikin lumana a jihar Jigawa

Zabe

Daga Muhammad Nasir Bashir

Babura (Jigawa), Aug. 16, 2025 (NAN) An gudanar da zabe cikin lumana a zaben cike gurbi na mazabar Babura-Garki a Jigawa a ranar Asabar.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa tun da karfe 8:00 na safe, masu kada kuri’a suka yi dafifi zuwa rumfunan zabe, a daidai lokacin da jami’an tsaro ke da isasshen tsaro a fadin yankin.

Jami’an ‘yan sandan Najeriya (NPF), jami’an tsaro ta Civil Defence (NSCDC), Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS) da sauran su, sun tabbatar da kiyaye doka da oda a rumfunan zabe da sauran muhimman wurare a Babura da Garki.

A rumfar zabe ta Garki Kofar Fada (003) da firamaren Yamma (005) a garin Garki, an ga jami’an zabe suna shirya kayan zaben tun kafin a fara da karfe 8:30 na safe.

Mista Ibrahim Shehu, jami’in zabe na 1 a rumfar zabe, ya ce sun yi isassun shirye-shirye domin saukaka gudanar da aikin.

Wani sashe na masu kada kuri’a sun yaba da yadda zaben ya gudana cikin kwanciyar hankali, inda suka jin dadi ga yadda jami’an tsaro suka gudanar da aikinsu.

Zaben ya samu fitowar jama’a da dama da suka hada da ministan tsaro, Badaru Abubakar, da karamar Ministan Ilimi Hajiya Suwaiba Ahmad.

An kuma ga wasu mazauna yankin suna gudanar da harkokinsu na yau da kullum, yayin kada kuri’a cikin lumana a mafi yawan wuraren da aka ziyarta. (NAN) (www.nannews.ng)

 

MNB/ISHO/ RSA

Fassara Aisha Ahmed

Zaben cike gurbi: An kama mutane 100 bisa zargin bangar siyasa a Kano

Banga

Daga Aminu Garko

Bagwai (Kano) Aug.16, 2025 (NAN) Hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano, ta tabbatar da cewa an kama sama da mutane 100 da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne a karamar hukumar Bagwai yayin zaben cike gurbi da ake gudanarwa a jihar.

Kwamishinan zabe na jihar Kano, Mista Abdu Zango, ya tabbatar da faruwar lamarin, yayin da yake zantawa da manema labarai, bayan ya duba zaben da aka gudanar a garin Bagwai a ranar Asabar.

Ya ce an samu wadanda ake zargin dauke da makamai daban-daban, kuma Zango ya nuna jin dadinsa da yadda zaben ya gudana.

A cewarsa, an samar wa jami’an zabe kayayyakin da suka dace a duk wuraren da aka kebe.

Sai dai ya tabbatar da cewa an samu wasu tsaikon a harkar saboda al’amuran da suka shafi dabarun samun ingantaccen tsaro.

Ya ce akwai jami’an tsaro a dukkan wuraren zabe domin tabbatar da doka da oda tare da gudanar da zabe cikin lumana. (NAN) (www.nannews.ng)

AAG/ISHsa Ishola/Sam Oditah ne ya gya

 

Aisha Ahmed ta fassara

Mamakon ruwan sama yana yi mana barazana – manoman shinkafa a Abakaliki

 Douglas Okoro

Abakaliki, 6 ga Agusta, 2025 (NAN) Manoman shinkafa a Abakaliki, sun koka kan yadda ake samun mamakon ruwan sama, wanda a cewarsu yana barazana ga noman shinkafa a shekarar 2025.

Manoman, sun bayyana damuwar tasu ne a wata tattaunawa da suka yi da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) a ranar Laraba a garin Abakaliki.

An dai samu mamakon ruwan sama a bana wanda ya yi sanadin ambaliya da asarar amfanin gona a manyan yankunan da ake noman shinkafa a jihar.

Mista Emmanuel Nwali, wani fitaccen manomin shinkafa a karamar hukumar Izzi, ya ce kusan rabin gonar shinkafarsa ta nutse sakamakon ruwan sama mai yawa.

“Ambaliya ta lalata yawancin gonakinmu, abin da ya rage tuni ya koma tawaya.

“Kusan kullum ana ruwan sama tun tsakiyar watan Yuli. Wataƙila ba za mu yi tsammanin samun girbi mai yawa a wannan kakar ba,” in ji Nwali.

Wani manomi, Mista Chinedu Okenwa, ya ce ya yi asarar gidajen yara na reno sakamakon ambaliyar ruwa, wanda ya yi sanadin asarar manyan albarkatu.

“Ban san yadda zan gyara asarar da aka yi ba, domin a halin yanzu, ba zan iya dasa komai ba don ya lalace.

“Muna fuskantar karancin amfanin gona a wannan kakar, kuma hakan na iya haifar da hauhawar farashin shinkafar gida a shekara mai zuwa,” in ji shi.

Hakazalika, Mista Aloysius Njoku, wani Mai nomana kasuwanci, ya ce ya yi asarar wani kaso mai yawa na gonar shinkafa sakamakon ambaliya, kuma yana fargabar ci gaban zai yi illa ga girbi.

“Damina da ambaliyar ruwa sun yi mummunar barna, idan ba a yi wani abu ba, shinkafa za ta yi karanci da tsada, kuma kowa zai ji ajikinsa,” in ji Njoku.

Misis Sylvia Elom, wata ma’aikaciyar gwamnati kuma mai noman shinkafa, ta bayyana ddamuwarta inda tace barnar da ruwan sama ya yi a gonaki ta yi kamari kuma abun zai shafi mutane da dama da suka dogara da noman shinkafa domin tafiyar da rayuwarsu.

“Shinkafa ita ce babbar hanyar samun kudin shiga ga yawancin mutanenmu wadanda galibi manoma ne, idan ambaliyar ruwa ta lalata mana gonakinmu, ba a bar mu da komai ba kenan,” in ji ta.

A halin da ake ciki, Dr Paul Onwe, wani kwararren manoma mai zaman kansa, ya bayyana cewa akwai gagarumar matsala a noman shinkafa idan damuna ta tsawaita aka samu ambaliya.

Ya kara da cewa ruwan sama kamar da bakin kwarya, yana haifar da babbar barazana ga gonakin shinkafa, musamman wadanda ke cikin fadamu.

Ya shawarci manoma da su mai da hankali sosai kan hasashen yanayi kafin su fara noman shinkafa, yana mai cewa gwamnatin tarayya na bayar da gargadin a farkon kowace kakar noma.

“Filayen da ke cikin ƙasa suna fama da takurewar girma, ƙarancin abinci mai gina jiki, da cututtukan fungal,” Onwe yayi gargaɗi.

Wata majiya daga ma’aikatar noma ta jihar Ebonyi da ta nemi a sakaya sunanta, ta tabbatar da cewa gwamnatin jihar na bin diddigin illolin da ambaliyar ruwa ta haifar a gonaki a halin yanzu.

Ya kara da cewa gwamnati na kuma tattara rahotanni daga yankunan da abin ya shafa domin daukar matakan da suka dace.

NAN ta ruwaito cewa hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet), a hasashenta na yanayi, ta bayyana jihar Ebonyi a matsayin daya daga cikin jihohin da ake sa ran za su fuskanci ambaliyar ruwa a lokacin damuna ta 2025.

Jihar Ebonyi dai na daya daga cikin jihohin da ake noman shinkafa a Najeriya, kuma ‘yan kasuwar shinkafa a manyan kasuwannin Abakaliki, sun bayyana fargabar cewa farashin shinkafar na iya tashi sakamakon rashin girbi da ake sa ran za a samu. (NAN) (www.nannews.ng)

 

Edited by Aisha Ahmed